< Acts 15 >
1 AND certain persons coming down from Judea taught the brethren, That if ye are not circumcised according to the ordinances of Moses, ye cannot be saved.
Wadansu mutane suka zo daga Yahudiya suka koyar da 'yan'uwa, cewa, “Idan ba yi maku kaciya bisa ga al'addar Musa ba, ba za ku sami ceto ba.”
2 There being therefore no small contention and dispute maintained by Paul and Barnabas against them, they determined that Paul and Barnabas, and certain others of their body, should go up to the apostles and presbyters at Jerusalem, for the decision of this question.
Da Bulus da Barnaba suka tunkare su da mahawara, sai 'yan'uwa suka yanke shawara Bulus da Barnaba da wasu su je Urushalima wurin manzanni da dattawa a kan wannan magana.
3 They therefore being sent on their way by the church, passed through Phoenicia and Samaria, giving a particular narrative of the conversion of the Gentiles: and they gave great joy to all the brethren.
Da shike iklisiya ce ta aike su, sai suka bi ta Finikiya da ta Samariya suka sanar da tuban al'ummai. Ya kawo murna mai yawa a wurin 'yan'uwa.
4 Then when they arrived at Jerusalem, they were cordially received by the church, and the apostles and presbyters, and they related how great things God had done by them.
Bayan sun zo Urushalima, sai iklisiya da manzanni da dattawa, suka marabce su, sai suka fada masu abin da Allah ya yi ta wurinsu.
5 But up rose some of the pharisaical sect, who professed the faith, insisting, That it was necessary to circumcise them, and to enjoin them to observe the law of Moses.
Amma wadansu mutane wadanda suka ba da gaskiya daga cikin Farisawa, suka tashi suka ce, “Dole ne a yi masu kaciya a kuma umarce su su kiyaye dokar Musa.”
6 Then the apostles and presbyters were assembled to consider of this matter.
Sai manzanin da dattawan suka taru don su duba wannan lamari.
7 When after much dispute, Peter arose, and said unto them, Men and brethren, ye know that a considerable time ago God chose among us, by my mouth, that the Gentiles should hear the gospel-word, and believe.
Bayan mahawara mai tsanani, sai Bitrus ya tashi ya ce masu, “'Yan'uwa, kun san lokacin baya da ya wuce, Allah ya yi zabi a cikinku, cewa ta bakina ne al'ummai za su ji bishara, su kuma ba da gaskiya.
8 And God, who is the discerner of the heart, bore them witness, giving them the Holy Ghost, even as to us;
Allah, wanda ya san zuciya, ya yi masu shaida, ya kuma basu Ruhu Mai Tsarki kamar yadda ya yi mana;
9 and made no difference betwixt either us or them, purifying their hearts by faith.
kuma bai bambanta mu da su ba, ya tsabtace zuciyarsu ta wurin bangaskiya.
10 Why then now tempt ye God, by imposing a yoke on the neck of the disciples, which neither our fathers nor we were able to bear?
To, saboda haka don me kuke gwada Allah, kuna sa wa almajirai nauyi a wuya wanda ubanninmu duk da mu ba mu iya dauka ba?
11 But we believe that we shall be saved by the grace of the Lord Jesus Christ, in the same way as they.
Amma mun gaskanta za mu samu ceto ta wurin alherin Ubangiji Yesu, kamar yadda suke.”
12 Then the whole multitude kept silence, and listened to Barnabas and Paul, relating how great signs and miracles God had wrought among the Gentiles by them.
Dukan taron jama'ar suka yi shiru sa'adda suke sauraron sakon shaidar da mamakin abin da Allah ya yi ta wurin Bulus da Barnaba a cikin al'ummai.
13 Now when they ceased speaking, James replied, saying, Men and brethren, hear me:
Bayan sun gama magana, Yakubu ya amsa, ya ce, “'Yan'uwa, ku ji ni.
14 Simon hath fully related, how at first God graciously looked upon the Gentiles, to take from them a people for his name.
Saminu ya fada yadda Allah ya fara nuna jinkai ga al'ummai domin ya dauke jama'a daga cikinsu domin sunansa.
15 And in accord with this are the words of the prophets; as it is written,
Maganar annabawa ta yarda da wannan, kamar yadda yake a rubuce,
16 “After this will I return, and build again the tabernacle of David, that is fallen; and re-edify what hath been dug up from the foundation, and will set it upright again:
'Bayan wadannan abubuwa zan dawo, zan gina gidan Dauda wanda ya fadi kasa; in sake gina bangonsa, in tsayar da shi,
17 that the residue of men may diligently seek the Lord, and all the Gentiles, among whom my name is invoked, even among them, saith the Lord, who doth all these things.”
saboda sauran jama'a su nemi fuskar Ubangiji, har da al'ummai da ake kira da sunana.
18 Known unto God from the beginning are all his works. (aiōn )
Wannan shine abin da Ubangiji ya fadi, shi wanda ya yi wadannan abubuwa da aka sani tun zamanin da. (aiōn )
19 Therefore I am decided, that we give no unnecessary disquietude to those who from the heathen have turned to God:
Saboda haka, a gani na kada mu matsa wa al'umman da suka juyo gun Allah;
20 but that we write to them, that they abstain from pollutions of idol sacrifices, and from whoredom, and from what is strangled, and from blood.
amma zamu rubuta masu da cewa, su guje wa gumaka da zina da faskanci da maye da cin mushe.
21 For Moses for ages past in every city hath those who preach him, being read in the synagogues every sabbath-day.
Tun zamanin da akwai mutane a kowanne birni wadanda suke wa'azi da karatun Musa a majami'u kowanne Asabaci.”
22 Then it was determined by the apostles and presbyters with the whole church, to send select men from themselves unto Antioch with Paul and Barnabas; Judas surnamed Barsabas, and Silas, leading men among the brethren;
Sai ya yi wa manzanin kyau su da dattawa da dukan iklisiyar su zabi Yahuza da Barnaba da Sila da dattawan iklisiya a tura su Antakiya tare da Bulus da Barnaba.
23 writing a letter by their hand, in these words: The apostles and presbyters and the brethren, to the brethren from among the Gentiles which are at Antioch, and in Syria, and Cilicia, greeting:
Sai suka rubuta wasika, “Manzani da dattawa da 'yan'uwa zuwa ga al'ummai 'yan'uwa a Antakiya da Suriya da Kilikiya, gaisuwa mai yawa.
24 Forasmuch as we have heard, that certain persons who went out from us have disturbed you with discourses, unsettling your minds, insisting, that you should be circumcised, and observe the law: to whom we gave no such charge:
Mun ji cewa wasu mutane daga cikinmu wadanda ba mu umarce su ba, sun fita daga cikinmu sun yi maku koyarwar da ta daga maku hankali.
25 it hath seemed fit to us, assembled unanimously, to send unto you select men with our beloved Barnabas and Paul,
Ya yi kyau da dukanmu, muka amince mu zabi wadansu mutane mu tura su wurinku tare da Bulus da Barnaba,
26 men who have hazarded their lives for the name of our Lord Jesus Christ.
mutane wadanda suka sadaukar da ransu domin sunan Ubangiji Yesu Almasihu.
27 We have sent therefore Judas and Silas, and they by word of mouth will tell you the same things.
Mun aika Yahuza da Sila su gaya maku wadannan abubuwa.
28 For it hath seemed good to the Holy Ghost and to us, to lay upon you no other burden except these things which are of absolute necessity;
Saboda haka ya yi kyau Ruhu Mai Tsarki da mu, kada mu sa maku nauyi fiye da wadannan abubuwan:
29 that ye abstain from eating whatever is sacrificed to idols, and from blood, and from what is strangled, and from whoredom: from which things carefully preserving yourselves, ye shall do well. Farewell.
ku bar yi wa gumaka hadaya, ku bar cin mushe da shan kayan maye da zina da faskanci, in kun kiyaye wadannan abubuwa za ku zauna lafiya. Ku huta lafiya.”
30 They then being thus dispatched, came to Antioch: and assembling the multitude, they delivered the letter:
Da aka sallame su, sai suka je Antakiya. Bayan sun tara jama'a sai suka ba su wasikar.
31 and when they had read it, they rejoiced in the consolation of it.
Bayan da suka karanta ta, sai suka yi murna sosai saboda karfafawa.
32 Then Judas and Silas, being also themselves prophets, exhorted the brethren, in many a discourse, and established them.
Yahuza da Sila, da shike su annabawa ne, suka karfafa 'yan'uwa da kalmomi masu yawa.
33 And having stayed their time, they were dismissed in peace from the brethren to the apostles.
Bayan sun yi kwananki a wurin, sai aka sallame su zuwa wurin 'yan'uwa wadanda suka aiko su.
34 However Silas thought proper to abide there.
Amma ya gamshe Sila ya zauna a wurin.
35 Paul also and Barnabas abode at Antioch, teaching and preaching, with many others also, the word of the Lord.
Amma Bulus da Barnaba suka tsaya a Antakiya da sauran 'yan'uwa, suna koyar da maganar Ubangiji.
36 Then after certain days said Paul to Barnabas, Let us now return and visit our brethren in every city among whom we have preached the word of the Lord, that we may see how they hold on.
Bayan kwanaki kadan Bulus ya ce ma Barnaba, “Mu koma yanzu mu ziyarci dukan 'yan'uwa da muka yi masu bisharar Ubangiji, mu ga yadda suke.
37 Now Barnabas had resolved to take with him John, whose surname is Mark.
Barnaba yana so su dauki Yahaya wanda kuma ake kira Markus.
38 But Paul did not think him a fit person to take with them, who had withdrawn from them from Pamphylia, and no longer went with them to the service.
Amma Bulus ya yi tunanin bai kamata a tafi da Markus ba, tun da ya bar su a Bamfiliya bai ci gaba da su ba.
39 So there grew up a sudden quarrel, insomuch that they separated from each other: and Barnabas, taking Mark with him, sailed away to Cyprus:
Nan jayayya ta tashi tsakaninsu, har suka rabu da juna sai Barnaba ya tafi tare da Markus suka ketare zuwa Kuburus.
40 but Paul selecting Silas, departed, being commended by the brethren to the favour of God.
Amma Bulus ya zabi Sila suka tafi, bayan 'yan'uwa sun yi masu addu'ar alherin Allah ya kiyaye su.
41 And he passed through Syria and Cilicia, confirming the churches.
Bulus ya tafi ya zazzaga Suriya da Kilikiya yana ta karfafa iklisiyoyin.