< 1 Peter 1 >

1 PETER, an apostle of Jesus Christ, to the sojourners, dispersed through Pontus, Galatia, Cappadocia, Asia, and Bithynia,
Bitrus, manzon Yesu Almasihu, zuwa ga zababbu wadanda suke baki, a warwatse cikin Buntus, Galatiya, kappadokiya, Asiya, da Bitiniya.
2 elect according to the foreknowledge of God the Father, by sanctification of the Spirit, that they might be brought to the obedience, and sprinkled with the blood of Jesus Christ: grace unto you and peace be multiplied.
Bisa ga rigasanin Allah Uba, Ta wurin tsarkakewar Ruhu, zuwa biyayya da yayyafar jinin Yesu Almasihu. Alheri da salama su yawaita a gareku.
3 Blessed be the God and Father of our Lord Jesus Christ, who according to his abundant mercy hath begotten us again unto an animating hope through the resurrection of Jesus Christ from the dead,
Albarka ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Ta wurin jinkansa mai girma, ya maya haihuwarmu zuwa bege mai rai ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu.
4 for an inheritance incorruptible, and undefiled, and unfading, reserved in the heavens for you,
Zuwa gado marar lalacewa, marar baci, ba kuma zai kode ba. Wanda aka kebe a sama dominku.
5 who are guarded by the omnipotence of God, through faith to obtain the salvation which is ready to appear at the last time.
Ku da ikon Allah ya kiyaye ta wurin bangaskiya domin ceto wanda za'a bayyana a karshen zamanai.
6 Wherein ye exult, though yet for a little space, (if it must be so, ) ye are in sorrow through various trials:
Cikin wannan kuna murna da yawa, duk da ya ke ya zama wajibi gare ku yanzu ku yi bakin ciki, a cikin jarabobi iri iri.
7 that the test of your faith (much more precious than that of gold, which is of a perishing nature, though proved by fire) may be found unto praise and honour and glory at the revelation of Jesus Christ:
Wannan kuwa da nufin a iske aunawar bangaskiyarku ne, bangaskiyar da tafi zinariya daraja, wadda takan lalace ko da an gwada ta da wuta. Wannan ya faru domin bangaskiyan nan taku ta jawo maku yabo da girma da daukaka a bayyanuwar Yesu Almasihu.
8 whom though ye have not seen, ye love; on whom, though ye have not as yet gazed, yet believing, ye exult with joy unutterable and glorious:
Wanda kuke kauna, ko da yake baku ganshi ba. Ko da yake baku ganinsa yanzu, duk da haka kun bada gaskiya gare shi murnar da ku ke yi kwarai da farin ciki wanda tafi gaban a fadi cike da daukaka.
9 receiving the end of your faith, the salvation of your souls.
Kuna karbar sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku.
10 Concerning which salvation the prophets eagerly sought and diligently inquired, who prophesied of the grace which is come to you:
Annabawan da su ka yi annabcin ceton da ya zama naku su ka yi bidassa suka bincike kuma da himma.
11 investigating to what time and to what conjuncture the Spirit of Christ in them pointed, when predicting the sufferings coming upon Christ, and the glories subsequent thereto.
Sun nemi su san ko wanene da kuma kowanne lokaci ne Ruhun Almasihu da ke cikinsu yake bayyana ma su. Wannan ya faru ne sa'adda yake gaya ma su tun da wuri game da shan wahalar Almasihu da kuma daukakar da zata biyo baya.
12 To whom it was revealed, that not for themselves, but for us were their ministrations employed in the things which are now declared unto you by those who have preached the gospel unto you by the Holy Ghost sent down from heaven; on which things the angels bending forwards eagerly desire to gaze.
An kuwa bayyana wa annabawan cewa ba kansu suke hidimtawa ba, amma ku suke yi wa hidima. Wannan shine abin da suke yi game da abin da aka rigaya aka gaya maku, ta wurin wadanda da Ruhu mai Tsarki ya bishe su. Wanda aka aiko daga sama. Wadannan sune abubuwan da mala'iku ma suka yi marmarin a bayyana masu.
13 Wherefore girding up the loins of your mind, vigilant, wait with assured hope for the grace, which shall be brought unto you at the revelation of Jesus Christ;
Domin wannan fa ku natsu. Ku yi dammara a hankalinku. Ku kafa begenku sarai akan alherin da za'a kawo maku a lokacin bayyanuwar Yesu Almasihu.
14 as obedient children, not conformed to the former passions of the days of your ignorance:
Kamar 'ya'ya masu biyyaya, kada ku biyewa sha'awoyinku na da a zamanin jahilcinku.
15 but as he who hath called you is holy, be ye holy also in all your conduct:
Amma yadda shi wanda ya kira ku mai tsarki ne, kuma ku zama da tsarki cikin dukkan al'amuranku.
16 because it is written, “Be ye holy; for I am holy.”
Domin a rubuce yake, “Ku zama da tsarki, gama ni mai tsarki ne.”
17 And if ye invoke him as Father, who without respect of persons judgeth according to every man’s work, conduct yourselves during the time of your sojourning with jealous fear:
Idan ku na kira bisa gare shi “Uba” shi wanda yake hukuntawa ba da tara ba, amma gwar-gwadon aikin kowane mutum, sai kuyi zaman bakuncinku da tsoro da bangirma.
18 knowing that ye have not been redeemed out of your vain manner of life, derived traditionally from your fathers, by the corruptible things, silver and gold,
Kun san cewa ba da azurfa ko zinariya mai lalacewa aka fanshe ku ba, daga halinn wauta da kuka gada daga wurin iyayenku.
19 but by the precious blood of Christ, as the unblemished and spotless lamb:
Maimakon haka an fanshe ku da jinin Almasihu mai daraja, marar aibu kamar na dan rago.
20 who was indeed predestined before the foundation of the world, but manifested in these last times for us,
An zabi Almasihu tun kafin kafawar duniya, amma a karshen zamanu ya bayyanu a gare ku.
21 who by him believe in God, that raised him from the dead, and gave him glory; that your faith and hope might be in God.
Ku da kuka bada gaskiya ga Allah ta wurinsa, wanda ya tashe shi daga matattu ya kuma bashi daukaka domin bangaskiyarku da begenku su kasance cikin Allah.
22 Having purified your souls by obedience to the truth through the Spirit unto fraternal affection undissembled, love each other intensely out of a pure heart:
Da shike kun tsarkake rayukanku cikin biyayyar ku ga gaskiya zuwa ga sahihiyar kauna ta 'yan'uwa, sai ku kaunaci junanku da zuciya mai gaskiya.
23 born again, not of corruptible seed, but of incorruptible, by the quickening word of God, and which abideth for ever. (aiōn g165)
da shike an sake hai'huwarku ba daga iri mai lalacewa ba amma daga iri marar rubewa, ta wurin maganar Allah wadda take rayuwa ta kuma dawwama. (aiōn g165)
24 “For all flesh is as grass, and all the glory of man, as the flower of grass. The grass withereth, and the flower of it falleth off:”
Gama “dukkan jiki kamar ciyawa yake, dukkan darajarsa kuwa kamar furen ciyawa take. Ciyawa takan yi yaushi, furenta ya kan yankwane ya fadi,
25 but the word of the Lord abideth for ever. And this is the word which by the gospel is preached unto you. (aiōn g165)
amma maganar Ubangiji tabbatacciya ce har abada. “Wannan ita ce maganar bishara wadda akayi maku wa'azinta.” (aiōn g165)

< 1 Peter 1 >