< John 6 >
1 After these things Jesus went beyond the Sea of Galilee, of Tiberias.
Ɗan lokaci bayan wannan, sai Yesu ya ƙetare zuwa gaɓar mai nesa na Tekun Galili (wato, Tekun Tibariya),
2 And a great multitude followed Him, because they saw the miracles He was doing in behalf of the sick.
sai taro mai yawa na mutane suka bi shi domin sun ga abubuwan banmamakin da ya yi ga marasa lafiya.
3 And Jesus came into the mountain; and was sitting there with His disciples.
Sa’an nan Yesu ya hau gefen dutse ya zauna tare da almajiransa.
4 And the passover, the feast of the Jews, was nigh.
Bikin Ƙetarewan Yahudawa ya yi kusa.
5 Therefore Jesus lifting up His eyes, and seeing that a great multitude is coming to Him, He says to Philip, Whence can we purchase bread, that these may eat?
Sa’ad da Yesu ya ɗaga kai ya ga taro mai yawa suna zuwa wajensa, sai ya ce wa Filibus, “Ina za mu sayi burodi saboda mutanen nan su ci?”
6 He spoke this testing him; for He knew what He was about to do.
Ya yi wannan tambayar don yă gwada shi ne kawai, gama ya riga ya san abin da zai yi.
7 Philip responded to Him, The loaves of two hundred denaria are not sufficient for these, that each one may receive a little.
Sai Filibus ya amsa ya ce, “Kai, ko albashin wata takwas ba zai iya sayan isashen burodin da kowa zai ɗan samu kaɗan ba!”
8 And one of His disciples, Andrew, the brother of Peter, says to Him,
Sai wani daga cikin almajiransa Andarawus, ɗan’uwan Bitrus, ya yi magana,
9 There is a lad here who has five barley loaves and two fishes: but what are these among so many?
“Ga wani yaro da ƙananan burodin sha’ir guda biyar da ƙananan kifi biyu, amma me wannan zai yi wa yawan mutanen nan.”
10 And Jesus said, Make the people sit down. And there was much grass in the place. However the men sat down in number about five thousand.
Yesu ya ce, “Ku sa mutanen su zauna.” Wurin kuwa akwai ciyawa da sosai, sai maza suka zazzauna, sun kai wajen dubu biyar.
11 And Jesus took the bread; and gave thanks, and gave it to the disciples, and the disciples to the people sitting down; and likewise also of the fishes so much as they wished.
Sa’an nan Yesu ya ɗauki burodin, ya yi godiya, ya kuma rarraba wa waɗanda suke zaune gwargwadon abin da ya ishe su. Haka kuma ya yi da kifin.
12 And when they were filled, He says to His disciples, Gather up the remaining fragments, that nothing may be lost.
Sa’ad da duk suka ci suka ƙoshi, sai ya ce wa almajiransa, “Ku tattara gutsattsarin da suka rage. Kada kome yă lalace.”
13 Then they gathered them up, and filled twelve baskets from the live barley loaves, which remained to those having eaten.
Saboda haka suka tattara su suka kuma cika kwanduna goma sha biyu na gutsattsarin burodin sha’ir biyar nan da suka ragu bayan kowa ya ci.
14 Then the people, seeing the miracle which Jesus did, were saying, that, This is truly the prophet who is coming into the world.
Bayan mutanen suka ga abin banmamakin da Yesu ya yi, sai suka fara cewa, “Lalle, wannan shi ne Annabin nan mai zuwa duniya.”
15 And Jesus knowing that they are about to come and take Him, that they may make Him king, departs again into the mountain Himself alone.
Da Yesu ya gane suna shirin su ɗauke shi ƙarfi da yaji su naɗa shi sarki, sai ya sāke komawa kan dutsen shi kaɗai.
16 And when it was evening, His disciples went down to the sea;
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara zuwa tafki,
17 and embarking in the ship, they were going to the other side of the sea into Capernaum. And it was already dark, and Jesus had not come to them;
inda suka shiga jirgin ruwa suka tasar wa haye tafkin zuwa Kafarnahum. A lokacin kuwa duhu ya yi, Yesu kuma bai riga ya zo wurinsu ba tukuna.
18 and the sea wrought, a great wind blowing.
Iska mai ƙarfi kuwa tana bugowa, ruwaye kuma suka fara hauka.
19 Then having gone about twenty-five or thirty furlongs, they see Jesus walking on the sea, and being near the ship; and were terrified.
Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko uku da rabi, sai suka ga Yesu ya kusato jirgin ruwan, yana takawa a kan ruwan; sai suka tsorata.
20 And He says to them, I am here; fear not.
Amma ya ce musu, “Ni ne; kada ku ji tsoro.”
21 Then they wished to receive Him into the ship, and immediately the ship was at the land to which they were going.
Sa’an nan suka yarda suka karɓe shi a cikin jirgin ruwan, nan da nan kuwa jirgin ya kai gaɓar da za su.
22 On the following day the multitude standing beyond the sea saw that there was no other ship there, except one, and that Jesus did not go along with His disciples into the ship, but His disciples went away alone
Kashegari taron da suka tsaya a wancan ƙetaren tafkin suka lura cewa jirgin ruwa ɗaya ne yake a can dā ma, kuma sun lura cewa Yesu bai shiga ciki tare da almajiransa ba, gama sun tashi su kaɗai.
23 (other ships came from Tiberias near the place where they ate the bread, the Lord having given thanks).
Sai ga waɗansu jiragen ruwa daga Tibariya suka iso kusa da wurin da mutanen suka ci burodi bayan Ubangiji ya yi godiya.
24 And when the multitude saw that Jesus was not there, nor His disciples, they went into ships, and came into Capernaum, seeking Jesus.
Da taron suka lura cewa Yesu da almajiransa ba sa can, sai suka shiga jiragen ruwa suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
25 And having found Him beyond the sea, they said to Him, Master, when did you come hither?
Da suka same shi a wancan ƙetaren tafkin, sai suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, yaushe ka kai nan?”
26 Jesus responded to them and said, Truly, truly, I say unto you, You seek me not because you saw the miracles, but because you ate of the loaves, and were filled.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, kuna nemana ne ba don kun ga abubuwan banmamaki ba, sai dai domin kun ci burodi kun ƙoshi.
27 Labor not for the food that perishes, but the food that abideth unto eternal life, which the Son of man gives to you: for this God the Father hath sealed. (aiōnios )
Kada ku yi aiki saboda abincin da yake lalacewa, sai dai saboda abinci mai dawwama har yă zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. A kansa ne Allah Uba ya sa hatimin amincewarsa.” (aiōnios )
28 Then they said to Him, What must we do, that we may work the works of God?
Sai suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi don mu aikata ayyukan da Allah yake so?”
29 Jesus responded and said to them, This is the work of God, that you may believe on Him whom He hath sent.
Yesu ya amsa, “Aikin Allah shi ne, a gaskata da wanda ya aiko.”
30 Then they said to Him, Then what miracle do you perform, that we may see, and believe you, what you may do?
Sai suka tambaye shi, “Wace abin banmamaki ce za ka yi don mu gani mu kuwa gaskata ka? Me za ka yi?
31 Our fathers ate manna in the wilderness; as has been written, He gave them bread from heaven to eat.
Kakannin-kakanninmu sun ci Manna a hamada; kamar yadda yake a rubuce, ‘Ya ba su burodi daga sama su ci.’”
32 Then Jesus said to them, Truly, truly, I say unto you, Moses did not give you the bread from heaven; but my Father gives you the true bread from heaven.
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba Musa ne ya ba ku burodi daga sama ba, sai dai Ubana ne yake ba ku burodi na gaskiya daga sama.
33 For the bread of God is the One coming down from heaven, and giving life to the world.
Gama burodin Allah shi ne wanda yake saukowa daga sama, yana kuma ba wa duniya rai.”
34 Then they said to Him, Lord, evermore give to us this bread.
Sai suka ce, “Ranka yă daɗe, daga yanzu ka dinga ba mu wannan burodi.”
35 Then Jesus said to them, I am the bread of life; the one coming unto me can never hunger, and the one believing on me shall never thirst.
Sa’an nan Yesu ya furta cewa, “Ni ne burodin rai. Wanda ya zo wurina ba zai taɓa jin yunwa ba, wanda kuma ya gaskata da ni ba zai taɓa jin ƙishirwa ba.
36 But I said unto you, That you have seen, and you do not believe.
Amma kamar yadda na faɗa muku, kun gan ni duk da haka ba ku gaskata ba.
37 Everything which the Father giveth unto me shall come to me; and him that cometh unto me I will in no wise cast out.
Duk waɗanda Uba ya ba ni za su zo wurina, kuma duk wanda ya zo wurina ba zan kore shi ba ko kaɗan.
38 Because I have come down from heaven, not that I may do my own will, but the will of Him that sent me.
Gama na sauko daga sama ba don in cika nufin kaina ba sai dai don in cika nufin shi wanda ya aiko ni.
39 And this is the will of the One having sent me, that everything that the Father has given unto me I shall lose nothing of it, but I shall raise it up in the last day.
Nufin wanda ya aiko ni kuwa shi ne, kada in yar da ko ɗaya daga cikin duk waɗanda ya ba ni, sai dai in tashe su a rana ta ƙarshe.
40 For this is the will of my Father, that every one seeing the Son, and believing on Him, may have eternal life; and I will raise him up in the last day. (aiōnios )
Gama nufin Ubana shi ne, duk wanda yake duban Ɗan, ya kuma gaskata shi zai sami rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.” (aiōnios )
41 Then the Jews were murmuring concerning Him, because He said, I am the bread having come down from heaven,
Da jin haka, Yahudawa suka fara gunaguni a kansa, domin ya ce, “Ni ne burodin da ya sauka daga sama.”
42 and they continued to say, Is this not Jesus, the son of Joseph, whose father and mother we know? how does He now say; I have come down from heaven?
Suka ce, “Kai, wannan ba Yesu ba ne, ɗan Yusuf, wanda mahaifinsa da mahaifiyarsa duk mun san su? Yaya yanzu zai ce, ‘Na sauko daga sama?’”
43 Jesus responded and said to them, Murmur not with one another.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ku daina gunaguni a junanku.
44 No one is able to come unto me, unless the Father who sent me may draw him: and I will raise him up in the last day.
Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uban da ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.
45 It is written in the prophets, They shall all be taught of God; every one hearing and learning from the Father, comes to me.
A rubuce yake a cikin Annabawa cewa, ‘Allah zai koyar da dukansu.’Duk wanda ya saurari Uba, ya kuma koyi daga wurinsa, zai zo wurina.
46 No one has seen the Father, except the One who is with God, He hath seen God.
Ba wanda ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda ya zo daga Allah; shi ne kaɗai ya taɓa ganin Uban.
47 Truly, truly, I say unto you, the one believing has eternal life. (aiōnios )
Gaskiya nake gaya muku, wanda ya gaskata yana da rai madawwami. (aiōnios )
48 I am the bread of life.
Ni ne burodin rai.
49 Your fathers ate the manna in the wilderness, and died;
Kakannin-kakanninku sun ci Manna a hamada, duk da haka suka mutu.
50 this is the bread coming down from heaven, that any one may eat of it, and not die.
Amma ga burodin da ya sauko daga sama, wanda mutum zai iya ci, ba zai kuma mutu ba.
51 I am the living bread, having come down from heaven; if any one may eat of me the bread, he will live forever: and the bread which I will give for the life of the world is my flesh. (aiōn )
Ni ne burodin rai mai saukowa daga sama. Duk wanda ya ci wannan burodi, zai rayu har abada. Wannan burodin shi ne jikina, da zan bayar don duniya ta sami rai.” (aiōn )
52 Then the Jews were contending with one another, saying, How is this One able to give unto us His flesh to eat?
Sai Yahudawa suka fara gardama mai tsanani a junansu suna cewa, “Yaya wannan mutum zai ba mu naman jikinsa mu ci?”
53 Then Jesus said unto them, Truly, truly, I say unto you, Unless you may eat the flesh of the Son of man and drink His blood, you have no life in you.
Sai Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, sai kun ci naman jikin Ɗan Mutum kuka kuma sha jininsa, ba za ku kasance da rai a cikinku ba.
54 The one eating my flesh and drinking my blood has eternal life; and I will raise him up in the last day. (aiōnios )
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana da rai madawwami. Ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe. (aiōnios )
55 For my flesh is the true food, and my blood is the true drink.
Gama naman jikina abinci ne na gaskiya jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
56 The one eating my flesh and drinking my blood abides in me, and I in him.
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana cikina, ni kuma ina cikinsa.
57 As the living Father sent me, and I live through the Father; truly the one eating me, shall also live through me.
Kamar dai yadda Uba mai rai ya aiko ni, ina kuma rayuwa ta saboda shi, haka ma wanda yake ni ne abincinsa zai rayu saboda ni.
58 He is the bread having come down from heaven: not as the fathers ate, and died: the one eating this bread shall live forever. (aiōn )
Wannan shi ne burodin da ya sauko daga sama. Kakannin-kakanninku sun ci Manna suka kuma mutu, amma duk wanda yake cin wannan burodi zai rayu har abada.” (aiōn )
59 And He spoke these things in the synagogue, teaching in Capernaum.
Ya faɗi wannan ne lokacin da yake koyarwa a cikin majami’a a Kafarnahum.
60 Then many of His disciples, hearing, said, This is a hard sermon; who is able to hear it?
Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan koyarwa tana da wuya. Wa zai iya yarda da ita?”
61 And Jesus knowing in Himself that His disciples are murmuring concerning it, said to them, Does this offend you?
Da yake ya san almajiransa suna gunaguni game da wannan, sai Yesu ya ce musu, “Wannan ya ɓata muku rai ne?
62 If then you may see the Son of man ascending up, where He was formerly?
Me za ku ce ke nan, in kuka gan Ɗan Mutum yana hawa zuwa inda yake dā!
63 The Spirit is the One who creates life; the flesh profits nothing; the words which I have spoken unto you are spirit and life.
Ruhu ne yake ba da rai; jikin kam, ba ya amfana kome. Kalmomin da na faɗa muku, Ruhu ne, da kuma rai.
64 But there are certain ones of you who do not believe. For Jesus knew from the beginning that there are certain ones not believing, and there is one going to betray Him.
Duk da haka akwai waɗansunku da ba su gaskata ba.” Gama Yesu ya sani tun farko, waɗanda ba su gaskata ba, da kuma wanda zai bashe shi.
65 And He said, Therefore I have said unto you, that no one is able to come unto me, unless it may have been given unto him of the Father.
Ya ci gaba da cewa, “Shi ya sa na faɗa muku cewa ba mai iya zuwa wurina, sai dai Uba ya yardar masa.”
66 Moreover from this many of His disciples went back, and walked with Him no more.
Daga wannan lokaci da yawa daga cikin almajiransa suka ja da baya, suka daina bin sa.
67 Then Jesus said to the twelve, Do you also wish to go away?
Sai Yesu ya tambayi Sha Biyun, “Ku ma za ku tafi ne?”
68 Simon Peter responded to Him, Lord, to whom shall we go away? thou hast the words of eternal life; (aiōnios )
Sai Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji wajen wa za mu tafi? Kai ne da kalmomin rai madawwami. (aiōnios )
69 we have believed and we know that thou art the Holy One of God.
Mun gaskata mun kuma san cewa kai ne Mai Tsarkin nan na Allah.”
70 Jesus responded to them, Have I not chosen you twelve, and one of you is devilish?
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ba ni na zaɓe ku Sha Biyu ba? Amma ɗayanku Iblis ne!”
71 But He spoke of Judas Iscariot the son of Simon, for he was going to betray Him, being one of the twelve.
(Yana nufin Yahuda, ɗan Siman Iskariyot, wanda, ko da yake ɗaya ne cikin Sha Biyun, zai bashe shi daga baya.)