< Psalms 91 >

1 Who so dwelleth in the secrete of the most High, shall abide in the shadowe of the Almightie.
Shi wanda yake zama a wurin Mafi Ɗaukaka zai huta a cikin inuwar Maɗaukaki.
2 I will say vnto the Lord, O mine hope, and my fortresse: he is my God, in him will I trust.
Zan ce game da Ubangiji, “Shi ne mafakata da kagarata, Allahna, wanda nake dogara.”
3 Surely he will deliuer thee from the snare of the hunter, and from the noysome pestilence.
Tabbatacce zai cece ka daga tarkon mai farauta da kuma daga cututtuka masu kisa.
4 Hee will couer thee vnder his winges, and thou shalt be sure vnder his feathers: his trueth shall be thy shielde and buckler.
Zai rufe ka da fikafikansa, a ƙarƙashin fikafikansa kuwa za ka sami mafaka; amincinsa zai zama maka garkuwa da katanga.
5 Thou shalt not be afraide of the feare of the night, nor of the arrowe that flyeth by day:
Ba za ka ji tsoron razanar dare, ko kibiyoyi da suke firiya da rana ba,
6 Nor of the pestilence that walketh in the darkenesse: nor of the plague that destroyeth at noone day.
ko bala’in da yake aukowa cikin duhu, ko annobar da take hallakarwa da tsakar rana.
7 A thousand shall fall at thy side, and tenne thousand at thy right hand, but it shall not come neere thee.
Dubu za su iya fāɗuwa a gefenka, dubu goma a hannun damanka, amma ba abin da zai zo kusa da kai.
8 Doubtlesse with thine eyes shalt thou beholde and see the reward of the wicked.
Za ka dai gan da idanunka yadda ake hukunta mugaye.
9 For thou hast said, The Lord is mine hope: thou hast set the most High for thy refuge.
In ka mai da Mafi Ɗaukaka wurin zamanka, har ma Ubangiji wanda yake mafakata,
10 There shall none euill come vnto thee, neither shall any plague come neere thy tabernacle.
to, babu wani mugun abin da zai same ka, ba masifar da za tă zo kusa da tentinka.
11 For hee shall giue his Angels charge ouer thee to keepe thee in all thy wayes.
Gama zai umarci mala’ikunsa game da kai don su tsare ka a dukan hanyoyinka;
12 They shall beare thee in their handes, that thou hurt not thy foote against a stone.
za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.
13 Thou shalt walke vpon the lyon and aspe: the yong lyon and the dragon shalt thou treade vnder feete.
Za ka taka zaki da gamsheƙa; za ka tattake babban zaki da maciji.
14 Because he hath loued me, therefore will I deliuer him: I will exalt him because hee hath knowen my Name.
Ubangiji ya ce, “Domin ya ƙaunace ni, zan kuɓutar da shi; zan kiyaye shi, gama ya yarda da sunana.
15 He shall call vpon me, and I wil heare him: I will be with him in trouble: I will deliuer him, and glorifie him.
Zai kira bisa sunana, zan kuma amsa masa; zan kasance tare da shi a lokacin wahala, zan kuɓutar da shi in kuma girmama shi.
16 With long life wil I satisfie him, and shew him my saluation.
Da tsawon rai zan ƙosar da shi in kuma nuna masa cetona.”

< Psalms 91 >