< Psalms 7 >

1 Shigaion of Dauid, which he sang unto the Lord, concerning the wordes of Chush the sonne of Iemini. O Lord my God, in thee I put my trust: saue me from all that persecute me, and deliuer me,
Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
2 Least he deuoure my soule like a lion, and teare it in pieces, while there is none to helpe.
in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
3 O Lord my God, if I haue done this thing, if there be any wickednes in mine handes,
Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
4 If I haue rewarded euill vnto him that had peace with mee, (yea I haue deliuered him that vexed me without cause)
in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
5 Then let the enemie persecute my soule and take it: yea, let him treade my life downe vpon the earth, and lay mine honour in the dust. (Selah)
to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
6 Arise, O Lord, in thy wrath, and lift vp thy selfe against the rage of mine enemies, and awake for mee according to the iudgement that thou hast appointed.
Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
7 So shall the Congregation of the people compasse thee about: for their sakes therefore returne on hie.
Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
8 The Lord shall iudge the people: Iudge thou me, O Lord, according to my righteousnesse, and according to mine innocencie, that is in mee.
bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
9 Oh let the malice of the wicked come to an ende: but guide thou the iust: for the righteous God trieth the hearts and reines.
Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
10 My defence is in God, who preserueth the vpright in heart.
Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
11 God iudgeth the righteous, and him that contemneth God euery day.
Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
12 Except he turne, he hath whet his sword: he hath bent his bowe and made it readie.
In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
13 Hee hath also prepared him deadly weapons: hee will ordeine his arrowes for them that persecute me.
Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
14 Beholde, hee shall trauaile with wickednes: for he hath conceiued mischiefe, but he shall bring foorth a lye.
Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
15 Hee hath made a pitte and digged it, and is fallen into the pit that he made.
Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
16 His mischiefe shall returne vpon his owne head, and his crueltie shall fall vpon his owne pate.
Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
17 I wil praise the Lord according to his righteousnes, and will sing praise to the Name of the Lord most high.
Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.

< Psalms 7 >