< Psalms 51 >

1 To him that excelleth. A Psalme of David, when the Prophet Nathan came unto him, after he had gone in to Bath-sheba. Have mercie vpon me, O God, according to thy louing kindnes: according to the multitude of thy compassions put away mine iniquities.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
2 Wash me throughly from mine iniquitie, and clense me from my sinne.
Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
3 For I know mine iniquities, and my sinne is euer before me.
Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
4 Against thee, against thee onely haue I sinned, and done euill in thy sight, that thou mayest be iust when thou speakest, and pure when thou iudgest.
Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
5 Beholde, I was borne in iniquitie, and in sinne hath my mother conceiued me.
Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
6 Beholde, thou louest trueth in the inwarde affections: therefore hast thou taught mee wisedome in the secret of mine heart.
Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
7 Purge me with hyssope, and I shalbe cleane: wash me, and I shalbe whiter then snowe.
Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
8 Make me to heare ioye and gladnes, that the bones, which thou hast broken, may reioyce.
Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
9 Hide thy face from my sinnes, and put away all mine iniquities.
Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
10 Create in mee a cleane heart, O God, and renue a right spirit within me.
Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
11 Cast mee not away from thy presence, and take not thine holy Spirit from me.
Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
12 Restore to me the ioy of thy saluation, and stablish me with thy free Spirit.
Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
13 Then shall I teache thy wayes vnto the wicked, and sinners shalbe conuerted vnto thee.
Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
14 Deliuer me from blood, O God, which art the God of my saluation, and my tongue shall sing ioyfully of thy righteousnes.
Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
15 Open thou my lippes, O Lord, and my mouth shall shewe foorth thy praise.
Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
16 For thou desirest no sacrifice, though I would giue it: thou delitest not in burnt offering.
Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
17 The sacrifices of God are a contrite spirit: a contrite and a broken heart, O God, thou wilt not despise.
Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
18 Bee fauourable vnto Zion for thy good pleasure: builde the walles of Ierusalem.
Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
19 Then shalt thou accept ye sacrifices of righteousnes, euen the burnt offering and oblation: then shall they offer calues vpon thine altar.
Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.

< Psalms 51 >