< Psalms 114 >
1 When Israel went out of Egypt, and the house of Iaakob from the barbarous people,
Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
2 Iudah was his sanctification, and Israel his dominion.
Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
3 The Sea sawe it and fled: Iorden was turned backe.
Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
4 The mountaines leaped like rams, and the hils as lambes.
duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
5 What ailed thee, O Sea, that thou fleddest? O Iorden, why wast thou turned backe?
Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
6 Ye mountaines, why leaped ye like rams, and ye hils as lambes?
ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
7 The earth trembled at the presence of the Lord, at the presence of the God of Iaakob,
Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
8 Which turneth the rocke into waterpooles, and the flint into a fountaine of water.
wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.