< Psalms 109 >

1 To him that excelleth. A Psalme of David. Holde not thy tongue, O God of my praise.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
2 For the mouth of the wicked, and the mouth full of deceite are opened vpon me: they haue spoken to me with a lying tongue.
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
3 They compassed me about also with words of hatred, and fought against me without a cause.
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
4 For my friendship they were mine aduersaries, but I gaue my selfe to praier.
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
5 And they haue rewarded me euil for good, and hatred for my friendship.
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
6 Set thou the wicked ouer him, and let the aduersarie stand at his right hand.
Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
7 Whe he shalbe iudged, let him be condemned, and let his praier be turned into sinne.
Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
8 Let his daies be fewe, and let another take his charge.
Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
9 Let his children be fatherlesse, and his wife a widowe.
Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
10 Let his children be vagabonds and beg and seeke bread, comming out of their places destroyed.
Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
11 Let the extortioner catch al that he hath, and let the strangers spoile his labour.
Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
12 Let there be none to extend mercie vnto him: neither let there be any to shewe mercie vpon his fatherlesse children.
Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
13 Let his posteritie be destroied, and in the generation following let their name be put out.
Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
14 Let the iniquitie of his fathers bee had in remembrance with the Lord: and let not the sinne of his mother be done away.
Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
15 But let them alway be before the Lord, that he may cut off their memorial from ye earth.
Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
16 Because he remembred not to shew mercie, but persecuted the afflicted and poore man, and the sorowfull hearted to slay him.
Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
17 As he loued cursing, so shall it come vnto him, and as he loued not blessing, so shall it be farre from him.
Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
18 As he clothed himselfe with cursing like a rayment, so shall it come into his bowels like water, and like oyle into his bones.
Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
19 Let it be vnto him as a garment to couer him, and for a girdle, wherewith he shalbe alway girded.
Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
20 Let this be the rewarde of mine aduersarie from the Lord, and of them, that speake euill against my soule.
Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
21 But thou, O Lord my God, deale with me according vnto thy Name: deliuer me, (for thy mercie is good)
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
22 Because I am poore and needie, and mine heart is wounded within me.
Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
23 I depart like the shadowe that declineth, and am shaken off as the grashopper.
Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
24 My knees are weake through fasting, and my flesh hath lost all fatnes.
Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
25 I became also a rebuke vnto them: they that looked vpon me, shaked their heads.
Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
26 Helpe me, O Lord my God: saue me according to thy mercie.
Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
27 And they shall know, that this is thine hand, and that thou, Lord, hast done it.
Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
28 Though they curse, yet thou wilt blesse: they shall arise and be confounded, but thy seruant shall reioyce.
Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
29 Let mine aduersaries be clothed with shame, and let them couer themselues with their confusion, as with a cloke.
Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
30 I will giue thankes vnto the Lord greatly with my mouth and praise him among ye multitude.
Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
31 For he will stand at the right hand of the poore, to saue him from them that woulde condemne his soule.
Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.

< Psalms 109 >