< Psalms 103 >
1 A Psalme of David. My soule, prayse thou the Lord, and all that is within me, prayse his holy Name.
Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
2 My soule, prayse thou the Lord, and forget not all his benefites.
Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
3 Which forgiueth all thine iniquitie, and healeth all thine infirmities.
wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
4 Which redeemeth thy life from the graue, and crowneth thee with mercy and compassions.
wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
5 Which satisfieth thy mouth with good things: and thy youth is renued like the eagles.
Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
6 The Lord executeth righteousnes and iudgement to all that are oppressed.
Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
7 He made his wayes knowen vnto Moses, and his workes vnto the children of Israel.
Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
8 The Lord is full of compassion and mercie, slowe to anger and of great kindnesse.
Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
9 He will not alway chide, neither keepe his anger for euer.
Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
10 He hath not dealt with vs after our sinnes, nor rewarded vs according to our iniquities.
ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
11 For as high as the heauen is aboue ye earth, so great is his mercie toward them that feare him.
Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
12 As farre as the East is from the West: so farre hath he remooued our sinnes from vs.
kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
13 As a father hath compassion on his children, so hath the Lord compassion on them that feare him.
Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
14 For he knoweth whereof we be made: he remembreth that we are but dust.
gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
15 The dayes of man are as grasse: as a flowre of the fielde, so florisheth he.
Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
16 For the winde goeth ouer it, and it is gone, and the place thereof shall knowe it no more.
iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
17 But the louing kindnesse of the Lord endureth for euer and euer vpon them that feare him, and his righteousnes vpon childrens children,
Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
18 Vnto them that keepe his couenant, and thinke vpon his commandements to doe them.
tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
19 The Lord hath prepared his throne in heauen, and his Kingdome ruleth ouer all.
Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
20 Prayse the Lord, ye his Angels, that excell in strength, that doe his commandement in obeying the voyce of his worde.
Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
21 Prayse the Lord, all ye his hostes, ye his seruants that doe his pleasure.
Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
22 Prayse the Lord, all ye his workes, in all places of his dominion: my soule, prayse thou the Lord.
Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.