< Numbers 24 >

1 When Balaam saw that it pleased the Lord to blesse Israel, then he went not, as certaine times before, to set diuinations, but set his face toward the wildernesse.
To, da Bala’am ya ga cewa Ubangiji yana jin daɗin sa wa Isra’ila albarka, bai koma wajen sihiri kamar dā ba, amma ya juya fuskarsa wajen hamada.
2 And Balaam lift vp his eyes, and looked vpon Israel, which dwelt according to their tribes, and the Spirit of God came vpon him.
Da Bala’am ya duba sai ya ga Isra’ila sun yi sansani kabila, kabila, Ruhun Allah kuwa ya sauko masa,
3 And he vttered his parable, and sayd, Balaam the sonne of Beor hath sayde, and the man, whose eyes were shut vp, hath sayd,
sai ya yi annabcinsa ya ce, “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
4 He hath sayde, which heard the wordes of God, and sawe the vision of the Almightie, and falling in a traunce had his eyes opened:
maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, maganar wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, mutumin da ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
5 How goodly are thy tentes, O Iaakob, and thine habitations, O Israel!
“Ina misalin kyan tentunanka, ya Yaƙub, wuraren zamanka, ya Isra’ila!
6 As the valleis, are they stretched forth, as gardes by the riuers side, as the aloe trees, which the Lord hath planted, as the cedars beside the waters.
“Kamar kwaruruka suke a shimfiɗe, kamar lambu kusa da rafi, kamar itatuwan aloyes da Ubangiji ya dasa, kamar itatuwa al’ul kusa da ruwaye.
7 The water droppeth out of his bucket, and his seede shalbe in many waters, and his king shall be hier then Agag, and his kingdome shall bee exalted.
Ruwa zai kwararo daga bokitinsu; irinsu za su sami ruwa a yalwace. “Sarkinsu zai fi sarkin Agag; mulkinsu zai ɗaukaka.
8 God brought him out of Egypt: his strength shalbe as an vnicorne: he shall eate the nations his enemies, and bruise their bones, and shoote them through with his arrowes.
“Allah ya fitar da su daga Masar; suna da ƙarfin kutunkun ɓauna. Sun cinye abokan gāban, suka kakkarya ƙasusuwansu; da kibiyoyinsu suka sossoke su.
9 He coucheth and lieth downe as a yong lion, and as a lion: who shall stirre him vp? blessed is he that blesseth thee, and cursed is he that curseth thee.
Kamar zaki sun laɓe sun kwanta, kamar zakanya, wa zai yi ƙarfin hali yă tashe su? “Bari waɗanda suka albarkace ka, su sami albarka waɗanda kuma suka la’anta ka, su la’antu!”
10 Then Balak was very angry with Balaam, and smote his handes together: so Balak sayde vnto Balaam, I sent for thee to curse mine enemies, and beholde, thou hast blessed them nowe three times.
Fushin Balak ya ƙuna a kan Bala’am. Ya tafa hannunsa, ya ce masa, “Na kira ka don ka la’anta abokan gābana, amma sai ga shi ka sa musu albarka har sau uku.
11 Therefore nowe flee vnto thy place: I thought surely to promote thee vnto honour, but loe, the Lord hath kept thee backe from honour.
Yanzu ka bar nan ka tafi gida! Na ce zan sāka maka da lada mai kyau, amma Ubangiji ya hana ka samun ladan.”
12 Then Balaam answered Balak, Tolde I not also thy messengers, which thou sentest vnto me, saying,
Bala’am ya ce wa Balak, “Ban faɗa wa’yan aikan da ka aiko wurina ba cewa,
13 If Balak would giue me his house ful of siluer and gold, I can not passe the commandement of the Lord, to doe either good or bad of mine owne minde? what the Lord shall commaund, the same will I speake.
‘Ko da a ce Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Ubangiji Allahna ba, kuma dole in faɗa abin da Ubangiji ya ce ne kawai’?
14 And nowe behold, I goe vnto my people: come, I will aduertise thee what this people shall doe to thy folke in the later dayes.
Yanzu zan koma wajen mutanena, amma bari in gargaɗe ka game da abin da mutanen nan za su yi wa mutanenka cikin kwanaki masu zuwa.”
15 And he vttered his parable, and sayd, Balaam the sonne of Beor hath sayde, and the man whose eyes were shut vp, hath sayd,
Sa’an nan ya furta saƙonsa. “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
16 He hath said that heard the words of God, and hath the knowledge of the most High, and sawe the vision of the Almightie, and falling in a traunce had his eyes opened:
maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, wanda yake da sani daga Mafi Ɗaukaka, wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, wanda ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
17 I shall see him, but not nowe: I shall behold him, but not neere: there shall come a starre of Iaakob, and a scepter shall rise of Israel, and shall smite the coastes of Moab, and destroy all the sonnes of Sheth.
“Na gan shi, amma ba yanzu ba; na hange shi, amma ba kusa ba. Tauraro zai fito daga Yaƙub; sandan mulki zai fito daga Isra’ila. Zai ragargaje goshin Mowab, kawunan dukan’ya’yan Set.
18 And Edom shalbe possessed, and Seir shall be a possession to their enemies: but Israel shall do valiantly.
Za a ci Edom da yaƙi; za a ci Seyir, abokiyar gābanta, amma Isra’ila zai ƙara ƙarfi.
19 He also that shall haue dominion shall bee of Iaakob, and shall destroy the remnant of the citie.
Mai mulki zai fito daga Yaƙub yă hallaka waɗanda suka ragu a birnin.”
20 And when he looked on Amalek, he vttered his parable, and sayd, Amalek was the first of the nations: but his latter ende shall come to destruction.
Sai Bala’am ya ga Amalek, ya kuma furta maganarsa. “Amalek yana cikin al’ummai na fari, amma zai zama na ƙarshen da za a hallaka.”
21 And he looked on the Kenites, and vttered his parable, and sayde, Strong is thy dwelling place, and put thy nest in the rocke.
Sai ya ga Keniyawa, ya kuma furta maganarsa. “Wurin zamanku lafiya yake, an kuma sa sheƙarku a cikin duwatsu;
22 Neuerthelesse, the Kenite shalbe spoyled vntill Asshur cary thee away captiue.
duk da haka, za a hallaka ku Keniyawa sa’ad da Asshur ya kame ku.”
23 Againe he vttered his parable, and sayd, Alas, who shall liue when God doeth this?
Sai ya furta maganarsa ya ce, “Wayyo, wa zai rayu sa’ad da Allah ya yi haka?
24 The ships also shall come from the coastes of Chittim, and subdue Asshur, and shall subdue Eber, and he also shall come to destruction.
Jiragen ruwa za su zo daga Kittim; za su murƙushe Asshur da Eber, amma su ma za a hallaka su.”
25 Then Balaam rose vp, and went and returned to his place: and Balak also went his way.
Sa’an nan Bala’am ya tashi ya koma gidan, Balak kuma ya yi tafiyarsa.

< Numbers 24 >