< Numbers 23 >

1 And Balaam sayd vnto Balak, Builde me here seuen altars, and prepare me here seuen bullockes, and seuen rammes.
Bala’am ya ce, “Ka gina mini bagadai bakwai a nan, ka shirya mini bijimai bakwai da raguna bakwai.”
2 And Balak did as Balaam sayd, and Balak and Balaam offred on euery altar a bullocke and a ramme.
Balak ya yi yadda Bala’am ya faɗa, sai su biyu suka miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.
3 Then Balaam sayde vnto Balak, Stande by the burnt offring, and I will goe, if so be that the Lord will come and meete me: and whatsoeuer he sheweth me, I will tell thee: so he went forth alone.
Sa’an nan Bala’am ya ce wa Balak, “Tsaya nan kusa da hadayarka, ni kuwa in koma wani wurin da yake a kaɗaice. Wataƙila Ubangiji zai sadu da ni. Duk abin da ya bayyana mini, zan faɗa maka.” Sai ya haura kan wani wurin da yake a kaɗaice a tudun.
4 And God met Balaam, and Balaam sayd vnto him, I haue prepared seuen altars, and haue offred vpon euery altar a bullocke and a ramme.
Allah kuwa ya sadu da Bala’am. Bala’am ya ce, “Na shirya bagadai bakwai, na kuma miƙa bijimi guda da rago guda, a kan kowane bagade.”
5 And the Lord put an answere in Balaams mouth, and sayde, Go againe to Balak, and say on this wise.
Ubangiji ya ba wa Bala’am saƙo ya ce, “Ka koma wurin Balak, ka faɗa masa wannan saƙo.”
6 So when he returned vnto him, loe, hee stoode by his burnt offering, he, and all the princes of Moab.
Saboda haka, sai Bala’am ya koma wurin Balak ya same shi tsaye a kusa da hadayarsa, tare da dukan dattawan Mowab.
7 Then he vttered his parable, and sayde, Balak the king of Moab hath brought mee from Aram out of the mountaines of the East, saying, Come, curse Iaakob for my sake: come, and detest Israel.
Sai Bala’am ya furta abin da Allah ya faɗa masa ya ce, “Balak ya kawo ni daga Aram, sarkin Mowab ya kawo ni daga gabashin duwatsu. Ya ce, ‘Zo, ka la’anta mini Yaƙub; zo, ka tsine Isra’ila.’
8 How shall I curse, where God hath not cursed? or howe shall I detest, where the Lord hath not detested?
Yaya zan iya la’anta waɗanda Allah bai la’anta ba? Yaya zan tsine waɗanda Ubangiji bai tsine ba?
9 For from the top of the rocks I did see him, and from the hils I did beholde him: lo, the people shall dwell by themselues, and shall not be reckened among the nations.
Daga kan duwatsu na gan su, daga bisa kan tuddai na hange su. Na ga mutane da suke zaune su kaɗai ba sa ɗauki kansu ɗaya da al’ummai ba.
10 Who can tell the dust of Iaakob, and the nomber of the fourth part of Israel? Let me die the death of the righteous, and let my last ende be like his.
Wa zai iya ƙidaya ƙurar Yaƙub ko yă ƙidaya kashi ɗaya bisa huɗu na Isra’ila? Bari in mutu, mutuwar adali ƙarshena kuma yă zama kamar nasu!”
11 Then Balak saide vnto Balaam, What hast thou done vnto mee? I tooke thee to curse mine enemies, and beholde, thou hast blessed them altogether.
Balak ya ce wa Bala’am, “Me ke nan ka yi mini? Na kawo ka, ka la’anta abokan gābana, sai ga shi albarka kake sa musu!”
12 And he answered, and said, Must I not take heede to speake that, which the Lord hath put in my mouth?
Bala’am ya ce, “Ba dole in faɗa abin da Ubangiji ya sa a bakina ba?”
13 And Balak sayde vnto him, Come, I pray thee, with mee vnto another place, whence thou mayest see them, and thou shalt see but the vtmost part of them, and shalt not see them all: therefore curse them out of that place for my sake.
Sa’an nan Balak ya ce masa, “Zo, mu tafi wani wuri inda za ka gan su; a nan kana ganin sashe ne kawai, ba dukansu ba. Daga can kuwa, ka la’anta mini su.”
14 And he brought him into Sede-sophim to the top of Pisgah, and built seuen altars, and offred a bullocke, and a ramme on euery altar.
Saboda haka ya ɗauke shi zuwa filin Zofim a ƙwanƙolin Fisga, a can ya gina bagadai bakwai, ya kuma miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.
15 After, he sayde vnto Balak, Stande here by thy burnt offring, and I wil meete the Lord yonder.
Bala’am ya ce wa Balak, “Tsaya nan kusa da hadayarka, ni kuwa in je in sadu da Ubangiji a can.”
16 And the Lord mette Balaam, and put an answere in his mouth, and sayd, Goe againe vnto Balak, and say thus.
Ubangiji ya sadu da Bala’am, ya kuma ba shi saƙo ya ce, “Koma wurin Balak ka ba shi wannan saƙo.”
17 And when he came to him, beholde, hee stoode by his burnt offering, and the princes of Moab with him: so Balak sayde vnto him, What hath the Lord sayd?
Saboda haka ya tafi ya same Balak tsaye a kusa da hadayarsa, tare da dattawan Mowab. Balak ya tambaye Bala’am ya ce, “Mene ne Ubangiji ya ce?”
18 And he vttered his parable, and sayde, Rise vp, Balak, and heare: hearken vnto me, thou sonne of Zippor.
Sai Bala’am ya furta saƙon da aka ba shi ya ce, “Tashi, Balak, ka saurara; ka kasa kunne gare ni, ɗan Ziffor.
19 God is not as man, that he should lie, neither as the sonne of man that he shoulde repent: hath he sayde and shall he not do it? and hath he spoken, and shall he not accomplish it?
Allah ba mutum ba ne, da zai yi ƙarya, shi ba ɗan mutum ba ne, da zai canja tunaninsa. Yana maganar abin da ba zai iya aikata ba ne? Yakan kuma yi alkawarin da ba zai iya cikawa ba?
20 Behold, I haue receiued commandement to blesse: for he hath blessed, and I cannot alter it.
Na karɓi umarni in sa albarka; na kuwa sa albarka, ba zan iya janye ta ba.
21 Hee seeth none iniquitie in Iaakob, nor seeth no transgression in Israel: the Lord his God is with him, and the ioyfull shoute of a king is among them.
“Bai ga mugunta a cikin Yaƙub ba, bai kuma ga wahala a Isra’ila ba. Ubangiji Allahnsu yana tare da su; sowar Sarki yana cikinsu.
22 God brought them out of Egypt: their strength is as an vnicorne.
Allah ya fitar da su daga Masar; suna da ƙarfi iri na kutunkun ɓauna.
23 For there is no sorcerie in Iaakob, nor soothsaying in Israel: according to this time it shalbe sayde of Iaakob and of Israel, What hath God wrought?
Ba wata maitar da za tă ci Yaƙub, ba sihiri da zai cuci Isra’ila. Yanzu za a ce game da Yaƙub da Isra’ila, ‘Duba abin da Allah ya yi!’
24 Behold, the people shall rise vp as a lyon, and lift vp himselfe as a yong lyon: hee shall not lye downe, till he eate of the pray, and till he drinke the blood of the slayne.
Mutane sun tashi kamar ƙaƙƙarfar zakanya; sun tā da kansu kamar zaki wanda ba ya hutawa sai ya cinye naman abin da ya kama ya kuma sha jinin abin da ya kama.”
25 Then Balak sayde vnto Balaam, Neither curse, nor blesse them at all.
Sai Balak ya ce wa Bala’am, “Kada ka la’anta su, kada kuma ka sa musu albarka!”
26 But Balaam answered, and saide vnto Balak, Tolde not I thee, saying, All that the Lord speaketh, that must I do?
Bala’am amsa ya ce, “Ban faɗa maka zan yi kaɗai abin da Ubangiji ya ce ba?”
27 Againe Balak sayd vnto Balaam, Come, I pray thee, I wil bring thee vnto another place, if so be it wil please God, that thou mayest thence curse them for my sake.
Sai Balak ya ce wa Bala’am, “Zo in kai ka wani wuri. Wataƙila zai gamshi Allah, yă bari ka la’anta mini su daga can.”
28 So Balak brought Balaam vnto the top of Peor, that looketh toward Ieshmon.
Balak kuwa ya ɗauki Bala’am zuwa ƙwanƙolin Feyor, wanda yake fuskantar hamada.
29 Then Balaam sayde vnto Balak, Make me here seuen altars, and prepare me here seuen bullocks, and seuen rammes.
Bala’am ya ce, “Ka gina mini bagadai bakwai a nan, ka kuma shirya mini bijimai bakwai da raguna bakwai.”
30 And Balak did as Balaam had sayd, and offred a bullocke and a ram on euery altar.
Balak ya yi yadda Bala’am ya ce, ya kuwa miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.

< Numbers 23 >