< Numbers 15 >

1 And the Lord spake vnto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Speake vnto the children of Israel, and say vnto them, Whe ye be come into the land of your habitations, which I giue vnto you,
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Bayan kun shiga ƙasar da nake ba ku a matsayin gida,
3 And will make an offring by fire vnto the Lord, a burnt offring or a sacrifice to fulfil a vowe, or a free offring, or in your feastes, to make a sweete sauour vnto the Lord of the hearde, or of the flocke.
kuka yi hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji, daga cikin shanu, ko tumaki, abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa, ko hadayu don alkawura na musamman, ko hadayar yardar rai, ko kuma hadaya ta biki,
4 Then let him that offreth his offring vnto the Lord, bring a meate offring of a tenth deale of fine flowre, mingled with the fourth part of an Hin of oyle.
sai shi wanda ya kawo hadayar yă miƙa wa Ubangiji hadaya ta gari mai laushi mai kyau, kashi ɗaya bisa goma na efa wanda aka kwaɓa da kwalaba ɗaya na mai.
5 Also thou shalt prepare ye fourth part of an Hin of wine to be powred on a lambe, appointed for the burnt offring or any offring.
Da kowane ɗan rago don hadaya ta ƙonawa, a shirya kwalaba ɗaya na ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha.
6 And for a ram, thou shalt for a meat offring, prepare two tenth deales of fine floure, mingled with the third part of an Hin of oyle.
“‘In da rago ne za a miƙa, to, sai a shirya hadaya ta gari mai laushi, garin yă zama kashi biyu bisa goma na efa. A kwaɓa shi da kashi ɗaya bisa uku na garwan mai,
7 And for a drinke-offering, thou shalt offer the third part of an Hin of wine, for a sweete sauour vnto the Lord.
da kashi ɗaya bisa uku na garwan ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha. A miƙa ta abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
8 And when thou preparest a bullocke for a burnt offring, or for a sacrifice to fulfill a vowe or a peace offring to the Lord,
“‘Sa’ad da kuka shirya rago don hadaya ta ƙonawa saboda alkawari na musamman, ko hadaya ta salama ga Ubangiji,
9 Then let him offer with ye bullocke a meate offring of three tenth deales of fine floure, mingled with halfe an Hin of oyle.
sai ku kawo hadaya ta gari tare da bijimi, kashi ɗaya bisa uku na gari mai laushi kwaɓaɓɓe da rabin garwan mai.
10 And thou shalt bring for a drinke offring halfe an Hin of wine, for an offring made by fire of a sweete sauour vnto the Lord.
A kuma kawo rabin garwan ruwan inabi na hadaya ta sha. Za tă zama hadayar da aka yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
11 Thus shall it be done for a bullocke, or for a ram, or for a lambe, or for a kid.
Haka za a yi da kowane bijimi, ko rago, ko ɗan rago, ko bunsuru.
12 According to the nomber that yee prepare to offer, so shall yee doe to euery one according to their nomber.
Haka za a yi da kowannensu bisa ga abin da aka shirya.
13 All that are borne of the countrey, shall do these things thus, to offer an offring made by fire of sweete sauour vnto the Lord.
“‘Duk wanda yake ɗan ƙasa, ta haka ne dole zai aikata waɗannan abubuwa sa’ad da ya kawo hadaya da akan yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
14 And if a stranger soiourne with you, or whosoeuer bee among you in your generations, and will make an offring by fire of a sweete sauour vnto the Lord, as ye do, so hee shall doe.
Idan baƙon da yake baƙunci a cikinku, ko kowane ne da yake tare da ku a dukan zamananku, yana so yă ba da hadayar da akan yi da wuta don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, dole yă yi kamar yadda kuke yi.
15 One ordinance shalbe both for you of the Congregation, and also for the stranger that dwelleth with you, euen an ordinance for euer in your generations: as you are, so shall the stranger bee before the Lord.
Ƙa’ida ɗaya ce ga jama’a da kuma baƙin da suke zama a cikinku, wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a dukan tsararraki masu zuwa. Da ku, da baƙi, za ku zama ɗaya a gaban Ubangiji.
16 One Lawe and one maner shall serue both for you and for the stranger that soiourneth with you.
Doka ɗaya da ƙa’ida ɗaya za a yi aiki da ita a kan ku da kuma baƙin da suke zama a cikinku.’”
17 And the Lord spake vnto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
18 Speake vnto the children of Israel, and say vnto them, When ye be come into the lande, to the which I bring you,
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da ina kai ku,
19 And when ye shall eate of the bread of the land, ye shall offer an heaue offring vnto ye Lord.
kuka ci abincin ƙasar, ku miƙa wani sashe na amfanin ƙasar a matsayin hadaya ga Ubangiji.
20 Ye shall offer vp a cake of the first of your dowe for an heaue offring: as the heaue offring of the barne, so ye shall lift it vp.
Ku kawo waina daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku, ku kuma miƙa shi a matsayin hadaya daga masussuka.
21 Of the first of your dowe ye shall giue vnto the Lord an heaue offring in your generations.
A duk tsararraki masu zuwa, za ku miƙa wannan hadaya daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku ga Ubangiji.
22 And if ye haue erred, and not obserued all these commandements, which the Lord hath spoken vnto Moses,
“‘To, in ku a matsayin jama’a, da gangan kuka ƙi kiyaye waɗannan ƙa’idodi da Ubangiji ya ba wa Musa ba,
23 Euen all that the Lord hath commanded you by the hand of Moses, from the first day that the Lord commanded Moses, and hence forward among your generations:
ko wani daga cikin umarnan da Ubangiji ya ba ku ta wurinsa, daga ranar da Ubangiji ya ba da su, har zuwa tsararraki masu zuwa,
24 And if so be that ought be committed ignorantly of the Congregation, then all ye Congregatio shall giue a bullocke for a burnt offring, for a sweete sauour vnto the Lord, with the meat offring and drinke offring thereto, according to the maner, and an hee goate for a sinne offring.
in kuwa aka yi haka ba da gangan ba, kuma da rashin sani, sai duk jama’a su miƙa ɗan bijimi don hadaya ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji, tare da ƙayyadadden hadaya ta gari, da hadaya ta sha, da kuma bunsuru na hadaya don zunubi.
25 And the Priest shall make an atonement for al the Congregation of the children of Israel, and it shalbe forgiuen them: for it is ignorance: and they shall bring their offring for an offring made by fire vnto the Lord, and their sinne offering before the Lord for their ignorance.
Firist kuwa zai yi kafara domin dukan jama’ar Isra’ilawa, za a kuma gafarta musu, gama ba da gangan ba ne suka aikata, kuma sun kawo wa Ubangiji hadayar da akan yi da wuta da kuma hadaya don zunubi saboda laifinsu.
26 Then it shalbe forgiuen all the Congregation of the children of Israel, and the stranger that dwelleth among them: for all the people were in ignorance.
Za a gafarta wa dukan jama’ar Isra’ilawa, da baƙin da suke zama a cikinsu, gama duk laifin da aka yi da rashin sani, yakan shafi dukan mutane.
27 But if any one person sinne through ignorance, then he shall bring a shee goate of a yeere olde for a sinne offring.
“‘Amma in mutum ɗaya ne kaɗai ya yi laifi ba da gangan ba, dole yă kawo akuya domin hadaya don zunubi.
28 And the Priest shall make an atonement for the ignorant person, when hee sinneth by ignorance before the Lord, to make reconciliation for him: and it shalbe forgiuen him.
Firist zai yi kafara a gaban Ubangiji saboda mutumin nan da ya aikata laifi ba da gangan ba, in kuwa an yi kafara saboda shi, za a gafarta masa.
29 He that is borne among the children of Israel, and the stranger that dwelleth among them, shall haue both one lawe, who so doth sinne by ignorance.
Ƙa’ida dai za tă zama ɗaya ga duk wanda ya yi laifi ba da gangan ba, ko shi ɗan ƙasa ne, ko kuma baƙon da yake zama a cikinku.
30 But the person that doeth ought presumptuously, whether he be borne in the land, or a stranger, the same blasphemeth the Lord: therefore that person shalbe cut off from among his people,
“‘Amma duk wanda ya yi zunubi da gangan, ko shi ɗan ƙasa ne, ko baƙo, ya saɓi Ubangiji, dole a ware wannan mutum daga mutanensa,
31 Because he hath despised the worde of the Lord, and hath broken his commandement: that person shalbe vtterly cut off: his iniquitie shalbe vpon him.
gama ya rena maganar Ubangiji, ya kuma karya umarninsa. Tabbatacce za a kashe wannan mutum, alhakinsa laifinsa kuwa yana wuyansa.’”
32 And while the children of Israel were in the wildernesse, they found a man that gathered stickes vpon the Sabbath day.
Yayinda Isra’ilawa suke ciki hamada, sai aka sami wani mutum yana tattara itace a ranar Asabbaci.
33 And they that found him gathering sticks, brought him vnto Moses and to Aaron, and vnto all the Congregation,
Waɗanda suka gan shi, suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukan taro,
34 And they put him warde: for it was not declared what should be done vnto him.
sai suka sa shi a gidan waƙafi don ba su riga sun san abin da za a yi da shi ba tukuna.
35 Then the Lord said vnto Moses, This man shall dye the death: and let al the multitude stone him with stones without the hoste.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Dole mutumin yă mutu. Dole dukan taron su jajjefe shi a bayan sansani.”
36 And all the Congregation brought him without the hoste, and stoned him with stones, and he died, as the Lord had commanded Moses.
Saboda haka taron suka ɗauke shi zuwa bayan sansani, suka kuma jajjefe shi har ya mutu, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
37 And the Lord spake vnto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
38 Speake vnto the children of Israel, and bid them that they make them fringes vpon the borders of their garments throughout their generations, and put vpon the fringes of the borders a ryband of blewe silke.
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘A dukan tsararraki masu zuwa, za ku sa tuntaye a gefen rigunarku, su sa zare mai ruwan shuɗi a bisan kowane tuntu.
39 And ye shall haue the fringes, that when ye looke vpon them, ye may remember all the commandemets of the Lord, and do them: and that ye seeke not after your own heart, nor after your owne eyes, after the which ye go a whoring;
Tuntayen za su zama muku abin dubawa don ku riƙa tunawa da dukan umarnan Ubangiji, don kada ku bi son zuciyarku, da sha’awar idanunku yadda kuka taɓa yi.
40 That yee may remember and doe all my commandements, and bee holy vnto your God.
Sa’an nan za ku riƙa tuna, ku kuma aikata dukan umarnaina ku zama tsarkaka ga Allahnku.
41 I am the Lord your God, which brought you out of the lande of Egypt, to bee your God: I am the Lord your God.
Ni ne Ubangiji Allahnku, da ya fitar da ku daga Masar, don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”

< Numbers 15 >