< Nehemiah 4 >

1 But when Sanballat heard that we builded the wall, then was he wroth and sore grieued, and mocked the Iewes,
Da Sanballat ya ji cewa muna sāke ginin katangar, sai ya husata, ya haukace ƙwarai. Ya yi wa Yahudawa dariya,
2 And sayde before his brethren and the armie of Samaria, thus he sayde, What doe these weake Iewes? wil they fortifie them selues? wil they sacrifice? will they finish it in a day? will they make the stones whole againe out of the heapes of dust, seeing they are burnt?
a gaban abokansa da kuma sojojin Samariya ya ce, “Me waɗancan Yahudawan nan marasa ƙarfi suke yi? Za su maido da katangarsu ne? Za su miƙa hadayu ne? Za su gama a rana ɗaya? Za su iya samun duwatsun gini daga tsibin matattun duwatsu?”
3 And Tobiah the Ammonite was beside him, and said, Although they buylde, yet if a foxe goe vp, he shall euen breake downe their stonie wall.
Tobiya wakilin mutanen Ammon wanda yake a gefensa ya ce, “Abin nan da suke gini, ko dila ma ya hau, zai rushe shi!”
4 Heare, O our God (for we are despised) and turne their shame vpon their owne head, and giue them vnto a pray in the lande of their captiuitie,
Ka ji mu, ya Allahnmu, gama an rena mu. Bari zagin da suke yi mana yă koma kansu. Ka sa a kwashe su a kai su bauta a wata ƙasa.
5 And couer not their iniquitie, neither let their sinne be put out in thy presence: for they haue prouoked vs before the builders.
Kada ka rufe laifinsu, kada kuwa ka gafarta musu, gama sun ci mutuncinmu, mu da muke gini.
6 So we built the wall, and all the wall was ioyned vnto the halfe thereof, and the heart of the people was to worke.
Sai muka sāke ginin katangar sai da duka ta kai rabin tsayinta, gama mutane sun yi aiki da dukan ƙarfinsu.
7 But when Sanballat, and Tobiah, and the Arabians, and the Ammonites, and the Ashdodims heard that the walles of Ierusalem were repayred, (for the breaches began to be stopped) then they were very wroth,
Amma da Sanballat, da Tobiya, da Larabawa, da Ammonawa, da kuma mutanen Ashdod suka ji cewa gyare-gyaren katangar Urushalima yana cin gaba, ana kuma tattoshe wuraren da suka tsattsaga, sai suka husata ƙwarai.
8 And conspired all together to come and to fight against Ierusalem, and to hinder them.
Dukansu suka ƙulla su zo, su yi yaƙi da Urushalima, su tā da hankali a cikinta.
9 The we prayed vnto our God, and set watchmen by them, day and night, because of them.
Amma muka yi addu’a ga Allahnmu muka kuma sa masu tsaro da rana da kuma dare don mu magance wannan barazana.
10 And Iudah said, The strength of the bearers is weakened, and there is much earth, so that we are not able to build the wall.
Ana cikin haka, mutane a Yahuda suka ce, “Ƙarfin ma’aikata yana kāsawa, akwai kuma sauran tarkace da yawa da ba za mu iya sāke gina katangar ba.”
11 Also our aduersaries had sayde, They shall not knowe, neither see, till we come into the middes of them and slay them, and cause the worke to cease.
Abokan gābanmu sun ce, “Ba za su sani ba, ba kuwa za su gan mu ba, sai dai kawai su gan mu a cikinsu, za mu karkashe su, mu tsai da aikin.”
12 But when the Iewes (which dwelt beside them) came, they told vs ten times, From all places whence ye shall returne, they wil be vpon vs.
Sau da yawa Yahudawan da suke da zama kusa da abokan gābanmu sun yi ta zuwa suna yin mana magana, suna cewa “Ko’ina muka juya, za su fāɗa mana.”
13 Therefore set I in the lower places behind the wall vpon the toppes of the stones, and placed the people by their families, with their swordes, their speares and their bowes.
Saboda haka na sa jama’a su ja ɗamara bisa ga iyalinsu a bayan katanga, a wuraren da ba a gina ba. Suna riƙe da takuba, da māsu, da bakkuna.
14 Then I behelde, and rose vp, and said vnto the Princes, and to the rulers, and to the rest of the people, Be not afrayde of them: remember the great Lord, and fearefull, and fight for your brethren, your sonnes, and your daughters, your wiues, and your houses.
Bayan na dudduba abubuwa, sai na miƙe tsaye na ce wa manyan gari da shugabanni da kuma sauran jama’a, “Kada ku ji tsoronsu. Ku tuna da Ubangiji, wanda yake mai girma da banrazana, ku yi yaƙi don’yan’uwanku, da’ya’yanku maza da mata, da matanku da kuma gidajenku.”
15 And when our enemies heard that it was knowen vnto vs, then God brought their counsell to nought, and we turned all againe to the wall, euery one vnto his worke.
Da abokan gābanmu suka ji muna sane da shirinsu, Allah kuma ya wargaje shirin nan, sai duk muka dawo ga katangar, kowa ya kama aikinsa.
16 And from that day, halfe of the yong men did the labour, and the other halfe part of them helde the speares, and shieldes, and bowes, and habergins: and the rulers stoode behinde all the house of Iudah.
Daga wannan rana zuwa gaba, rabin mutane suka yi aiki, yayinda sauran rabin suka kintsa da māsu, da garkuwa, da bakkuna da makamai. Shugabanni suka goyi bayan dukan mutanen Yahuda
17 They that buylded on the wall, and they that bare burdens, and they that laded, did the worke with one hand, and with the other helde the sworde.
waɗanda suke ginin katanga. Waɗanda suke ɗaukan kaya suka yi aikinsu da hannu ɗaya, suna kuma riƙe da makami a ɗaya hannun,
18 For euery one of the buylders had his sworde girded on his loynes, and so buylded: and he that blewe the trumpet, was beside me.
kuma kowane mai gini ya ɗaura takobinsa a gefe yayinda yake aiki. Amma mutum mai busa ƙaho ya kasance tare da ni.
19 Then saide I vnto the Princes, and to the rulers, and to the rest of the people, The worke is great and large, and we are separated vpon the wall, one farre from another.
Sai na ce wa manyan gari, da shugabanni, da sauran jama’a, “Aikin nan babba ne kuma mai yawa, ga shi muna a rarrabe nesa da juna a katangar.
20 In what place therefore ye heare the sound of the trumpet, resort ye thither vnto vs: our God shall fight for vs.
Duk inda kuka ji an busa ƙaho, sai ku taru a wurin. Allahnmu zai yi yaƙi dominmu!”
21 So we laboured in the worke, and halfe of them helde the speares, from the appearing of the morning, till the starres came foorth.
Saboda haka muka ci gaba da aiki, rabin mutane suna riƙe da māsu, daga wayewar gari har zuwa fitowar taurari.
22 And at the same time said I vnto the people, Let euery one with his seruant lodge within Ierusalem, that they may be a watch for vs in the night, and labour in the day.
A wannan lokaci na kuma ce wa mutane, “A sa kowane mutum da mataimakinsa su zauna a Urushalima da dare, domin a yi tsaro da dare, da safe kuma a kama aiki.”
23 So neither I, nor my brethren, nor my seruants, nor the men of the warde, (which followed me) none of vs did put off our clothes, saue euery one put them off for washing.
Saboda haka ni, da’yan’uwana, da bayina, da matsaran da suke tare da ni, ba wanda ya tuɓe tufafinsa; kowa ya rataye makaminsa, ko ya je shan ruwa ma.

< Nehemiah 4 >