< Matthew 27 >

1 When the morning was come, all the chiefe Priests, and the elders of the people tooke counsell against Iesus, to put him to death,
Da gari ya waye, duk manyan firistoci da dattawan jama'a suka shirya yadda zasu kulla makirci domin su kashe shi.
2 And led him away bounde, and deliuered him vnto Pontius Pilate the gouernour.
Suka daure shi, suka mika shi ga gwamna Bilatus.
3 Then when Iudas which betraied him, sawe that hee was condemned, hee repented himselfe, and brought againe the thirtie pieces of siluer to the chiefe Priestes, and Elders,
Sa'adda Yahuza, wanda ya bashe shi, ya ga an zartarwa Yesu hukuncin kisa, ya nemi tuba ya kuma mayar da azurfar talatin ga manyan firistocin da dattawan,
4 Saying, I haue sinned, betraying the innocent bloud. But they sayde, What is that to vs? see thou to it.
yace, “Na yi zunubi ta wurin cin amanar mara laifi.” Amma sukace, “Ina ruwan mu? Ka ji da shi da kanka?”
5 And when hee had cast downe the siluer pieces in the Temple, hee departed, and went, and hanged himselfe.
Sai ya jefar da kwandalolin azurfar a kasa cikin haikalin ya kuma bar su, ya tafi ya rataye kansa.
6 And the chiefe Priestes tooke the siluer pieces, and sayde, It is not lawfull for vs to put them into the treasure, because it is the price of bloud.
Sai babban firist ya dauki kwandalolin azurfar ya ce, “Ba daidai bane bisa ga shari'a musa wannan cikin ma'aji, saboda kudin jini ne.”
7 And they tooke counsell, and bought with them a potters fielde, for the buriall of strangers.
Sai suka tattauna al'amarin a tsakanin su, kudin kuma suka sayi filin maginin tukwane domin makabatar baki.
8 Wherefore that field is called, The field of bloud, vntill this day.
Dalilin wannan ne ake kiran wurin, “Filin jini” har yau.
9 (Then was fulfilled that which was spoken by Ieremias the Prophet, saying, And they tooke thirtie siluer pieces, ye price of him that was valued, whom they of ye children of Israel valued.
Sai abin da aka fada ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa, “Suka dauki tsabar azurfa talatin na farashin da mutanen Isra'ila suka sa a kansa,
10 And they gaue them for the potters fielde, as the Lord appointed me.)
suka bayar domin sayen filin mai tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
11 And Iesus stood before ye gouernour, and the gouernour asked him, saying, Art thou that King of the Iewes? Iesus said vnto him, Thou sayest it.
Sai Yesu ya tsaya a gaban gwamna, gwamna ya kuma tambaye shi, “Kai sarkin Yahudawa ne?” Yesu ya amsa, “Haka ka fada.”
12 And when he was accused of the chiefe Priestes, and Elders, he answered nothing.
Amma da manyan firistocin da dattawan suka zarge shi, bai ce komai ba.
13 Then saide Pilate vnto him, Hearest thou not howe many things they lay against thee?
Sai Bilatus yace masa, “Baka ji dukan zarge-zargen da ake yi maka ba?”
14 But he answered him not to one worde, in so much that the gouernour marueiled greatly.
Amma bai ce masa ko kalma guda ba, sai gwamna yayi matukar mamaki.
15 Nowe at the feast, the gouernour was wont to deliuer vnto the people a prisoner whom they would.
To lokacin bikin idi, al'adar gwamna ne ya saki mutum guda wanda jama'a suka zaba.
16 And they had then a notable prisoner, called Barabbas.
A wannan lokacin suna da wani sanannen dan kurkuku mai suna Barabbas.
17 When they were then gathered together, Pilate said vnto the, Whether will ye that I let loose vnto you Barabbas, or Iesus which is called Christ?
To da suka tattaru, sai Bilatus yace masu, “Wa kuke so a sakar maku? Barabbas, ko Yesu wanda ake kira Almasihu?”
18 (For he knewe well, that for enuie they had deliuered him.
Saboda ya san sun kawo shi ne domin kishi.
19 Also when he was set downe vpon the iudgement seate, his wife sent to him, saying, Haue thou nothing to do with that iust man: for I haue suffered many things this day in a dreame by reason of him.)
Da yake zaune a kujerar shari'a, matarsa ta aika masa cewa, “Ka fita sha'anin mutumin nan marar laifi. Saboda na sha wahala sosai a yau cikin mafarki saboda shi.”
20 But the chiefe Priestes and the Elders had persuaded the people that they shoulde aske Barabbas, and should destroy Iesus.
A lokacin nan manyan firistoci da dattawa suka rinjayi ra'ayin jama'a suce a sakar masu da Barabbas, a kashe Yesu.
21 Then the gouernour answered, and said vnto them, Whether of the twaine will ye that I let loose vnto you? And they said, Barabbas.
Sai gwamna ya tambayesu, “Wa kuke so a sakar maku?” Sukace, “Barabbas.”
22 Pilate said vnto them, What shall I do then with Iesus, which is called Christ? They all said to him, Let him be crucified.
Bilatus yace masu, “Me zan yi da Yesu wanda ake kira Almasihu?” Sai duka suka amsa, “A gicciye shi.”
23 Then saide the gouernour, But what euill hath he done? Then they cryed the more, saying, Let him be crucified.
Sai yace, “Don me, wane laifi ya aikata?” Amma suka amsa da babbar murya, “A gicciye shi”
24 When Pilate saw that he auailed nothing, but that more tumult was made, he tooke water and washed his hands before the multitude, saying, I am innocent of the blood of this iust man: looke you to it.
Amma da Bilatus ya ga ba zai iya komai ba don hargitsi zai iya barkewa, ya dauki ruwa ya wanke hannuwansa a gaban jama'a, yace, “Ba ni da laifi ga jinin mutumin nan marar laifi. Ku yi abin da kuka ga dama.”
25 Then answered all the people, and saide, His bloud be on vs, and on our children.
Duka mutanen sukace, “Bari jininsa ya kasance a kan mu da 'ya'yan mu.”
26 Thus let he Barabbas loose vnto them, and scourged Iesus, and deliuered him to be crucified.
Sai ya sakar masu da Barabbas amma yayi wa Yesu bulala ya mika shi garesu domin su gicciye shi.
27 Then the souldiers of the gouernour tooke Iesus into the common hall, and gathered about him the whole band,
Sai sojojin gwamna suka dauki Yesu zuwa farfajiya suka kuma tara dukan rundunar sojoji.
28 And they stripped him, and put about him a skarlet robe,
Suka yi masa tumbur sa'annan suka sa masa jar alkyabba.
29 And platted a crowne of thornes, and put it vpon his head, and a reede in his right hand, and bowed their knees before him, and mocked him, saying, God saue thee King of the Iewes,
Sai suka yi masa rawanin kaya suka sa a kansa, suka kuma bashi sanda a hannunsa na dama. Suka rusuna a gabansa suna masa ba'a, suna cewa, “Ranka ya dade, Sarkin Yahudawa!”
30 And spitted vpon him, and tooke a reede, and smote him on the head.
Suka kuma tofa masa yawu, suka kwace sandar suka buga masa a ka.
31 Thus when they had mocked him, they tooke the robe from him, and put his owne rayment on him, and led him away to crucifie him.
Bayan sun gama masa ba'a, suka cire masa alkyabbar suka sa masa kayansa, suka jagorance shi zuwa wurin da za a gicciye shi.
32 And as they came out, they found a man of Cyrene, named Simon: him they compelled to beare his crosse.
Da suka fito waje, sai suka iske wani Bakurame mai suna Saminu, wanda suka tilasta ya tafi tare dasu domin ya dauki gicciyen.
33 And when they came vnto the place called Golgotha, (that is to say, the place of dead mens skulles)
Suka iso wani wuri da ake kira Golgotta, wanda ke nufin,”Wurin kwalluwa.”
34 They gaue him vineger to drinke, mingled with gall: and when he had tasted thereof, he would not drinke.
Suka bashi ruwan inabi da aka gauraya da wani abu mai daci. Amma da ya 'dan-'dana shi sai ya ki sha.
35 And when they had crucified him, they parted his garments, and did cast lottes, that it might be fulfilled, which was spoken by the Prophet, They deuided my garments among them, and vpon my vesture did cast lottes.
Bayan da suka gicciye shi, suka kada kuri'a a kan rigarsa.
36 And they sate, and watched him there.
Suka kuma zauna suna kallonsa.
37 They set vp also ouer his head his cause written, THIS IS IESVS THE KING OF THE IEVVES.
A sama da kansa suka sa abinda ake tuhumarsa da ita a rubuce, “Wannan shine sarkin Yahudawa.”
38 And there were two theeues crucified with him, one on the right hand, and another on the left.
An gicciye shi da 'yanfashi guda biyu, daya ta damansa dayan kuma ta hagunsa.
39 And they that passed by, reuiled him, wagging their heades,
Wadanda suke wucewa suna zaginsa, suna girgiza kai,
40 And saying, Thou that destroyest ye Temple, and buildest it in three dayes, saue thy selfe: if thou be ye Sonne of God, come downe from ye crosse.
suna kuma cewa, “Kai da kace zaka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku, ka ceci kanka mana! In dai kai Dan Allah ne, ka sauko daga gicciyen!”
41 Likewise also the hie Priests mocking him, with the Scribes, and Elders, and Pharises, said,
Ta haka ma manyan firistocin suka rika yi masa ba'a, tare da marubuta da shugabannin, suna cewa,
42 He saued others, but he cannot saue him selfe: if he be ye King of Israel, let him now come downe from ye crosse, and we will beleeue in him.
“Ya ceci wasu amma ya kasa ceton kansa. Shi ne sarkin Isra'ila. Ya sauko mana daga kan gicciyen, sai mu ba da gaskiya gareshi.
43 He trusted in God, let him deliuer him nowe, if he will haue him: for he saide, I am the Sonne of God.
Tun da ya yarda da Allah. Bari Allahn ya cece shi mana, saboda yace, “Ni dan Allah ne.”
44 The selfe same thing also ye theeues which were crucified with him, cast in his teeth.
Hakan nan ma 'yanfashin guda biyu da aka gicciye su tare suka zage shi.
45 Now from ye sixt houre was there darkenesse ouer all the land, vnto the ninth houre.
To tun da tsakar rana sai duhu ya rufe kasar gaba daya har karfe uku na yamma.
46 And about ye ninth houre Iesus cryed with a loud voyce, saying, Eli, Eli, lamasabachthani? that is, My God, my God, why hast thou forsaken me?
Wajen karfe uku, Yesu ya tada murya mai karfi yace, “Eli, Eli lama sabaktani?” wanda ke nufin, “Allahna, Allahna, don me ka yashe ni?”
47 And some of them that stoode there, when they heard it, said, This man calleth Elias.
Da wadanda suke tsaye kusa suka ji haka, sai sukace, “Yana kiran Iliya.”
48 And straightway one of them ran, and tooke a spondge, and filled it with vineger, and put it on a reede, and gaue him to drinke.
Nan take wani ya ruga da gudu ya dauki soso ya tsoma cikin ruwan inabi mai tsami ya soka kan sandar kara ya mika masa ya sha.
49 Other said, Let be: let vs see, if Elias wil come and saue him.
Sai sauran sukace, “Rabu da shi mu gani ko Iliya zai zo ya cece shi.”
50 Then Iesus cryed againe with a loude voyce, and yeelded vp the ghost.
Sai Yesu ya ta da murya mai karfi yayi kuka sai ya saki ruhunsa.
51 And behold, the vayle of the Temple was rent in twaine, from the top to the bottome, and the earth did quake, and the stones were cloue.
Sai labullen haikali ya yage gida biyu daga sama zuwa kasa. Kasa kuma ta girgiza, duwatsu suka farfashe.
52 And the graues did open themselues, and many bodies of the Saintes, which slept, arose,
Kaburbura suka bude, tsarkaka kuwa wadanda suke barci da yawa suka tashi.
53 And came out of the graues after his resurrection, and went into the holy citie, and appeared vnto many.
Suka fito daga kaburbura bayan tashinsa, suka shiga birni mai tsarki suka bayyana ga mutane da yawa.
54 When the Centurion, and they that were with him watching Iesus, saw the earthquake, and the thinges that were done, they feared greatly, saying, Truely this was the Sonne of God.
Da hafsan sojan da wadanda suke kallon Yesu suka ga girgizar kasar da abinda ya faru, suka ji tsoro kwarai sukace, “Hakika wannan Dan Allah ne”
55 And many women were there, beholding him a farre off, which had folowed Iesus from Galile, ministring vnto him.
Mata dayawa da suka bi Yesu daga Galili domin su lura da shi suka tsaya suna kallo daga nesa.
56 Among whom was Marie Magdalene, and Marie the mother of Iames, and Ioses, and the mother of Zebedeus sonnes.
A cikin su akwai Maryamu Magadaliya, Maryamu uwar Yesu da Yusufu, da uwar 'ya'yan Zabadi.
57 And when the euen was come, there came a riche man of Arimathea, named Ioseph, who had also himselfe bene Iesus disciple.
Da yamma sai wani attajiri mutumin Armatiya ya zo, mai suna Yusufu wanda shi ma almajirin Yesu ne.
58 He went to Pilate, and asked ye body of Iesus. Then Pilate commanded ye body to be deliuered.
Ya je wurin Bilatus ya roka a bashi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a bashi.
59 So Ioseph tooke the body, and wrapped it in a cleane linnen cloth,
Yusufu ya dauki jikin, ya rufe shi da likafani mai tsabta,
60 And put it in his new tombe, which he had hewen out in a rocke, and rolled a great stone to the doore of the sepulchre, and departed.
sai ya sa shi a cikin sabon kabarinsa da ya sassaka cikin dutse. Sai ya mirgina babban dutse a bakin kofar kabarin ya tafi.
61 And there was Marie Magdalene, and the other Marie sitting ouer against the sepulchre.
Maryamu Magadaliya da dayan Maryamun suna nan zaune akasin kabarin.
62 Nowe the next day that followed the Preparation of the Sabbath, the hie Priestes and Pharises assembled to Pilate,
Washegari, wato bayan ranar Shiri, Sai manyan firistoci da Farisawa suka taru tare da Bilatus.
63 And said, Syr, we remember that that deceiuer saide, while he was yet aliue, Within three dayes I will rise.
Sukace, “Mai gida, mun tuna lokacin da mayaudarin nan yake da rai, yace, “Bayan kwana uku zan tashi.”
64 Command therefore, that the sepulchre be made sure vntill the third day, lest his disciples come by night, and steale him away, and say vnto the people, He is risen from the dead: so shall the last errour be worse then the first.
Saboda haka, ka bada umarni a tsare kabarin na kwana uku. In ba haka ba almajiransa zasu zo su sace shi, kuma su ce wa mutane, “Ya tashi daga mattatu.” Kuma yaudarar karshe zata fi ta farko muni.”
65 Then Pilate saide vnto them, Ye haue a watch: goe, and make it sure as ye knowe.
Bilatus yace masu, “Ku dauki masu tsaro. Kuyi tsaro iyakar karfin ku.”
66 And they went, and made the sepulchre sure with the watch, and sealed the stone.
Sai suka tafi suka tsare kabarin, suka hatimce dutsen, suka sa masu tsaro.

< Matthew 27 >