< Matthew 27 >
1 When the morning was come, all the chiefe Priests, and the elders of the people tooke counsell against Iesus, to put him to death,
Da wayewar gari, sai dukan manyan firistoci da dattawan mutane suka yanke shawara su kashe Yesu.
2 And led him away bounde, and deliuered him vnto Pontius Pilate the gouernour.
Suka daure shi, suka tafi da shi, suka ba da shi ga gwamna Bilatus.
3 Then when Iudas which betraied him, sawe that hee was condemned, hee repented himselfe, and brought againe the thirtie pieces of siluer to the chiefe Priestes, and Elders,
Sa’ad da Yahuda, wanda ya bashe Yesu, ya ga an yanke wa Yesu hukuncin kisa, sai ya yi “da na sani.” Ya je mayar wa manyan firistoci da dattawan kuɗin azurfa talatin ɗin.
4 Saying, I haue sinned, betraying the innocent bloud. But they sayde, What is that to vs? see thou to it.
Ya ce, “Na yi zunubi da na ci amanar marar laifi.” Suka ce masa, “Ina ruwanmu da wannan? Wannan dai ruwanka ne.”
5 And when hee had cast downe the siluer pieces in the Temple, hee departed, and went, and hanged himselfe.
Sai Yahuda ya zubar da kuɗin a cikin haikalin ya tafi. Sa’an nan ya je ya rataye kansa.
6 And the chiefe Priestes tooke the siluer pieces, and sayde, It is not lawfull for vs to put them into the treasure, because it is the price of bloud.
Manyan firistoci suka ɗauki kuɗin, suka ce, “Doka ta hana a sa kuɗin a cikin ma’aji, da yake kuɗin jini ne.”
7 And they tooke counsell, and bought with them a potters fielde, for the buriall of strangers.
Saboda haka, sai suka yanke shawara su yi amfani da kuɗin suka sayi filin mai yin tukwane, saboda binne baƙi.
8 Wherefore that field is called, The field of bloud, vntill this day.
Shi ya sa ake kiran filin, Filin Jini har yă zuwa yau.
9 (Then was fulfilled that which was spoken by Ieremias the Prophet, saying, And they tooke thirtie siluer pieces, ye price of him that was valued, whom they of ye children of Israel valued.
Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika cewa, “Suka ɗauki azurfa talatin, kuɗin da mutanen Isra’ila suka sa a kansa,
10 And they gaue them for the potters fielde, as the Lord appointed me.)
suka kuma yi amfani da su, suka sayi filin mai yin tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
11 And Iesus stood before ye gouernour, and the gouernour asked him, saying, Art thou that King of the Iewes? Iesus said vnto him, Thou sayest it.
Ana cikin haka, Yesu kuwa yana tsaye a gaban gwamna, sai gwamnan ya tambaye shi, “Kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya ce, “I, haka ne, kamar yadda ka faɗa.”
12 And when he was accused of the chiefe Priestes, and Elders, he answered nothing.
Da manyan firistoci da dattawa suka zarge shi, bai ba da amsa ba.
13 Then saide Pilate vnto him, Hearest thou not howe many things they lay against thee?
Sai Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Ba ka jin shaidar da suke kawowa a kanka?”
14 But he answered him not to one worde, in so much that the gouernour marueiled greatly.
Amma Yesu bai ce uffam game da ko ɗaya daga cikin zargin da suka yi masa ba. Har gwamna ya yi mamaki ƙwarai.
15 Nowe at the feast, the gouernour was wont to deliuer vnto the people a prisoner whom they would.
A wannan irin Biki, gwamna yana da wata al’ada, ta sakin ɗan kurkuku guda wanda taron suka zaɓa.
16 And they had then a notable prisoner, called Barabbas.
To, a wannan lokaci kuwa suna da wani shahararren ɗan kurkuku da ake kira Barabbas.
17 When they were then gathered together, Pilate said vnto the, Whether will ye that I let loose vnto you Barabbas, or Iesus which is called Christ?
Saboda haka da taron suka taru, sai Bilatus ya tambaye su ya ce, “Wane ne a cikinsu kuke so in sakar muku. Barabbas ko Yesu wanda ake kira Kiristi?”
18 (For he knewe well, that for enuie they had deliuered him.
Don ya san saboda sonkai ne suka ba da Yesu a gare shi.
19 Also when he was set downe vpon the iudgement seate, his wife sent to him, saying, Haue thou nothing to do with that iust man: for I haue suffered many things this day in a dreame by reason of him.)
Yayinda Bilatus yake zaune a kan kujerar shari’a, sai matarsa ta aika masa da wannan saƙo cewa, “Kada ka sa hannunka a kan marar laifin nan, domin na sha wahala ƙwarai, a cikin mafarki yau game da shi.”
20 But the chiefe Priestes and the Elders had persuaded the people that they shoulde aske Barabbas, and should destroy Iesus.
Amma manyan firistoci da dattawa suka shawo kan taron, su ce, a ba su Barabbas, amma a kashe Yesu.
21 Then the gouernour answered, and said vnto them, Whether of the twaine will ye that I let loose vnto you? And they said, Barabbas.
Gwamna ya yi tambaya ya ce, “Wane ne cikin biyun nan, kuke so in sakar muku?” Suka ce, “Barabbas.”
22 Pilate said vnto them, What shall I do then with Iesus, which is called Christ? They all said to him, Let him be crucified.
Bilatus ya yi tambaya, “To, me zan yi da Yesu wanda ake kira Kiristi?” Duka suka ce, “A gicciye shi!”
23 Then saide the gouernour, But what euill hath he done? Then they cryed the more, saying, Let him be crucified.
Bilatus ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?” Amma suka ƙara tā da ihu, suna cewa, “A gicciye shi!”
24 When Pilate saw that he auailed nothing, but that more tumult was made, he tooke water and washed his hands before the multitude, saying, I am innocent of the blood of this iust man: looke you to it.
Da Bilatus ya ga cewa ba ya kaiwa ko’ina, sai ma hargitsi ne yake so yă tashi, sai ya ɗibi ruwa, ya wanke hannuwansa a gaban taron ya ce, “Ni kam, ba ruwana da alhakin jinin mutumin nan. Wannan ruwanku ne!”
25 Then answered all the people, and saide, His bloud be on vs, and on our children.
Sai dukan mutane suka amsa, suka ce, “Bari alhakin jininsa yă zauna a kanmu da’ya’yanmu!”
26 Thus let he Barabbas loose vnto them, and scourged Iesus, and deliuered him to be crucified.
Sai ya sakar musu Barabbas. Amma ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.
27 Then the souldiers of the gouernour tooke Iesus into the common hall, and gathered about him the whole band,
Sai sojojin gwamna suka ɗauki Yesu suka kai shi Fadar mai mulki, sa’an nan suka tara dukan kamfanin sojoji kewaye da shi.
28 And they stripped him, and put about him a skarlet robe,
Suka tuɓe shi, suka yafa masa wata jar riga.
29 And platted a crowne of thornes, and put it vpon his head, and a reede in his right hand, and bowed their knees before him, and mocked him, saying, God saue thee King of the Iewes,
Suka kuma tuƙa wani rawanin ƙaya, suka sa masa a kā. Suka sa sanda a hannun damansa. Suka durƙusa a gabansa, suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
30 And spitted vpon him, and tooke a reede, and smote him on the head.
Suka tattofa masa miyau, suka karɓe sandan, suka yi ta ƙwala masa shi a kai.
31 Thus when they had mocked him, they tooke the robe from him, and put his owne rayment on him, and led him away to crucifie him.
Bayan sun yi masa ba’a, sai suka tuɓe masa rigar, suka sa masa nasa tufafin. Sai suka tafi da shi, domin su gicciye shi.
32 And as they came out, they found a man of Cyrene, named Simon: him they compelled to beare his crosse.
Suna fitowa ke nan, sai suka sadu da wani mutumin Sairin, mai suna Siman. Sai suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen.
33 And when they came vnto the place called Golgotha, (that is to say, the place of dead mens skulles)
Sai suka iso wani wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai).
34 They gaue him vineger to drinke, mingled with gall: and when he had tasted thereof, he would not drinke.
A can, suka ba shi ruwan inabi gauraye da wani abu mai ɗaci yă sha. Amma da ya ɗanɗana, sai ya ƙi sha.
35 And when they had crucified him, they parted his garments, and did cast lottes, that it might be fulfilled, which was spoken by the Prophet, They deuided my garments among them, and vpon my vesture did cast lottes.
Bayan da suka gicciye shi, sai suka raba tufafinsa a tsakaninsu ta wurin jefa ƙuri’a.
36 And they sate, and watched him there.
Sa’an nan suka zauna suna tsaronsa.
37 They set vp also ouer his head his cause written, THIS IS IESVS THE KING OF THE IEVVES.
Bisa da kansa kuwa, an kafa rubutun zargin da aka yi masa, da ya ce, Wannan shi ne Yesu Sarkin Yahudawa.
38 And there were two theeues crucified with him, one on the right hand, and another on the left.
An gicciye’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗaya kuma a hagunsa.
39 And they that passed by, reuiled him, wagging their heades,
Masu wucewa, suka zazzage shi, suna kaɗa kai,
40 And saying, Thou that destroyest ye Temple, and buildest it in three dayes, saue thy selfe: if thou be ye Sonne of God, come downe from ye crosse.
suna cewa, “Kai da za ka rushe haikali, ka kuma gina shi cikin kwana uku, ceci kanka mana! In kai Ɗan Allah ne, ka sauka daga gicciyen!”
41 Likewise also the hie Priests mocking him, with the Scribes, and Elders, and Pharises, said,
Haka ma, manyan firistoci da malaman dokoki da kuma dattawa, suka yi ta yin masa ba’a, suna cewa,
42 He saued others, but he cannot saue him selfe: if he be ye King of Israel, let him now come downe from ye crosse, and we will beleeue in him.
“Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa! In shi ne Sarkin Isra’ila! To, yă sauko daga kan gicciyen nan, mu kuwa mu gaskata shi.
43 He trusted in God, let him deliuer him nowe, if he will haue him: for he saide, I am the Sonne of God.
Ya dogara ga Allah. Bari Allah yă cece shi yanzu, in yana sonsa, domin ya ce, ‘Ni Ɗan Allah ne.’”
44 The selfe same thing also ye theeues which were crucified with him, cast in his teeth.
Haka ma,’yan fashin da aka gicciye tare da shi, suka zazzage shi.
45 Now from ye sixt houre was there darkenesse ouer all the land, vnto the ninth houre.
Daga sa’a ta shida, har zuwa sa’a ta tara, duhu ya rufe ƙasa duka.
46 And about ye ninth houre Iesus cryed with a loud voyce, saying, Eli, Eli, lamasabachthani? that is, My God, my God, why hast thou forsaken me?
Wajen sa’a ta tara, Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).
47 And some of them that stoode there, when they heard it, said, This man calleth Elias.
Sa’ad da waɗanda suke tsattsaye a wurin suka ji haka, sai suka ce, “Yana kiran Iliya.”
48 And straightway one of them ran, and tooke a spondge, and filled it with vineger, and put it on a reede, and gaue him to drinke.
Nan da nan, ɗaya daga cikinsu ya ruga, ya sami soso, ya jiƙa shi da ruwan tsami, ya sa a sanda, ya miƙa wa Yesu, yă sha.
49 Other said, Let be: let vs see, if Elias wil come and saue him.
Sauran kuwa suka ce, “Ƙyale shi mu ga, ko Iliya zai zo yă cece shi.”
50 Then Iesus cryed againe with a loude voyce, and yeelded vp the ghost.
Da Yesu ya sāke ɗaga murya da ƙarfi, sai ya saki ruhunsa.
51 And behold, the vayle of the Temple was rent in twaine, from the top to the bottome, and the earth did quake, and the stones were cloue.
A daidai wannan lokaci, sai labulen haikali ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa. Ƙasa ta jijjiga, duwatsu kuma suka farfashe.
52 And the graues did open themselues, and many bodies of the Saintes, which slept, arose,
Kaburbura suka bubbuɗe, jikunan tsarkaka da yawa kuwa cikin waɗanda da suka mutu, suka tashi.
53 And came out of the graues after his resurrection, and went into the holy citie, and appeared vnto many.
Suka firfito daga kaburbura, sa’an nan bayan tashin Yesu daga matattu, suka shiga birni mai tsarki, suka bayyana ga mutane da yawa.
54 When the Centurion, and they that were with him watching Iesus, saw the earthquake, and the thinges that were done, they feared greatly, saying, Truely this was the Sonne of God.
Da jarumin nan tare da waɗanda suke tsaron Yesu, suka ga girgizar ƙasa, da kuma abin da ya faru, sai tsoro ya kama su, suka kuma ce, “Gaskiya, wannan Ɗan Allah ne!”
55 And many women were there, beholding him a farre off, which had folowed Iesus from Galile, ministring vnto him.
Akwai mata da yawa a can, suna kallo daga nesa. Sun bi Yesu tun daga Galili, suna masa hidima.
56 Among whom was Marie Magdalene, and Marie the mother of Iames, and Ioses, and the mother of Zebedeus sonnes.
A cikinsu, akwai Maryamu Magdalin, da Maryamu uwar Yaƙub da Yoses, da kuma uwar’ya’yan Zebedi.
57 And when the euen was come, there came a riche man of Arimathea, named Ioseph, who had also himselfe bene Iesus disciple.
Da yamma ta yi, sai ga wani mutum mai arziki daga Arimateya, sunansa Yusuf, wanda shi da kansa almajirin Yesu ne.
58 He went to Pilate, and asked ye body of Iesus. Then Pilate commanded ye body to be deliuered.
Ya je wurin Bilatus, ya roƙe shi yă ba shi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a ba shi.
59 So Ioseph tooke the body, and wrapped it in a cleane linnen cloth,
Yusuf ya ɗauki jikin ya nannaɗe shi da zanen lilin mai tsabta.
60 And put it in his new tombe, which he had hewen out in a rocke, and rolled a great stone to the doore of the sepulchre, and departed.
Sa’an nan ya sa shi a sabon kabarinsa, wanda ya haƙa a dutse. Bayan ya gungura wani babban dutse ya rufe bakin kabarin, sai ya tafi abinsa.
61 And there was Marie Magdalene, and the other Marie sitting ouer against the sepulchre.
Maryamu Magdalin da ɗayan Maryamun, suna zaune a wurin, ɗaura da kabarin.
62 Nowe the next day that followed the Preparation of the Sabbath, the hie Priestes and Pharises assembled to Pilate,
Kashegari, wato, bayan Ranar Shirye-shirye, sai manyan firistoci da Farisiyawa, suka je wurin Bilatus.
63 And said, Syr, we remember that that deceiuer saide, while he was yet aliue, Within three dayes I will rise.
Suka ce, “Ranka yă daɗe, mun tuna, mai ruɗin nan tun yana da rai ya ce, ‘Bayan kwana uku, zan tashi daga matattu.’
64 Command therefore, that the sepulchre be made sure vntill the third day, lest his disciples come by night, and steale him away, and say vnto the people, He is risen from the dead: so shall the last errour be worse then the first.
Saboda haka, ka ba da umarni, a tsare kabarin sai rana ta uku ɗin. In ba haka ba, almajiransa za su iya zuwa su sace jikin, sa’an nan su faɗa wa mutane cewa, an tashe shi daga matattu. Ruɗin ƙarshen nan fa, sai yă fi na farkon muni.”
65 Then Pilate saide vnto them, Ye haue a watch: goe, and make it sure as ye knowe.
Sai Bilatus ya ce, “Shi ke nan, ku ɗebi soja, ku je ku tsare kabarin iya ƙoƙarinku.”
66 And they went, and made the sepulchre sure with the watch, and sealed the stone.
Sai suka je suka tsare kabarin ta wurin buga masa hatimi, suka kuma sa masu gadi.