< Matthew 2 >

1 When Jesus then was borne at Bethleem in Iudea, in the dayes of Herod the King, beholde, there came Wisemen from the East to Hierusalem,
Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana, daga gabas suka zo Urushalima
2 Saying, Where is that King of the Iewes that is borne? for wee haue seene his starre in the East, and are come to worship him.
suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”
3 When King Herod heard this, he was troubled, and all Hierusalem with him.
Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima.
4 And gathering together all the chiefe Priestes and Scribes of the people, hee asked of them, where Christ should be borne.
Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi.
5 And they saide vnto him, At Beth-leem in Iudea: for so it is written by the Prophet,
Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.
6 And thou Beth-leem in the lande of Iuda, art not the least among the Princes of Iuda: For out of thee shall come the gouernour that shall feede that my people Israel.
“‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda, ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba, gama daga cikinki mai mulki zai zo, wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’”
7 Then Herod priuily called the Wisemen, and diligently inquired of them the time of the starre that appeared,
Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana.
8 And sent them to Beth-leem, saying, Goe, and searche diligently for the babe: and when ye haue founde him, bring mee worde againe, that I may come also, and worship him.
Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”
9 So when they had heard the King, they departed: and loe, the starre which they had seene in the East, went before them, till it came and stoode ouer the place where the babe was.
Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake.
10 And when they sawe the starre, they reioyced with an exceeding great ioy,
Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai.
11 And went into the house, and founde the babe with Mary his mother, and fell downe, and worshipped him, and opened their treasures, and presented vnto him giftes, euen golde, and frankincense, and myrrhe.
Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur.
12 And after they were warned of God in a dreame, that they should not go againe to Herod, they returned into their countrey another way.
Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.
13 After their departure, behold, the Angel of the Lord appeareth to Ioseph in a dreame, saying, Arise, and take the babe and his mother, and flee into Egypt, and be there til I bring thee word: for Herod will seeke the babe, to destroy him.
Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”
14 So he arose and tooke the babe and his mother by night, and departed into Egypt,
Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar,
15 And was there vnto the death of Herod, that that might be fulfilled, which is spoken of the Lord by the Prophet, saying, Out of Egypt haue I called my sonne.
inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”
16 Then Herod, seeing that he was mocked of the Wisemen, was exceeding wroth, and sent foorth, and slew all the male children that were in Beth-leem, and in all the coasts thereof, from two yeere old and vnder, according to the time which he had diligently searched out of the Wisemen.
Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan.
17 Then was that fulfilled which is spoken by the Prophet Ieremias, saying,
Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,
18 In Rhama was a voyce heard, mourning, and weeping, and great howling: Rachel weeping for her children, and would not be comforted, because they were not.
“An ji murya a Rama, tana kuka da makoki mai tsanani, Rahila ce take kuka domin’ya’yanta, an kāsa ta’azantar da ita, don ba su.”
19 And whe Herod was dead, behold, an Angel of the Lord appeareth in a dreame to Ioseph in Egypt,
Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar,
20 Saying, Arise, and take the babe and his mother, and goe into the land of Israel: for they are dead which sought the babes life.
ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”
21 Then he arose vp and tooke the babe and his mother, and came into the land of Israel.
Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila.
22 But whe he heard that Archelaus did reigne in Iudea in stead of his father Herod, he was afraide to go thither: yet after he was warned of God in a dreame, he turned aside into the parts of Galile,
Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili,
23 And went and dwelt in a citie called Nazareth, that it might be fulfilled which was spoken by the Prophets, which was, That hee should be called a Nazarite.
ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”

< Matthew 2 >