< Mark 6 >

1 And he departed thence, and came into his owne countrey, and his disciples followed him.
Ya bar su ya zo garinsu, almajiransa su ka biyo shi.
2 And when the Sabbath was come, he began to teach in the Synagogue, and many that heard him, were astonied, and sayd, From whence hath this man these things? and what wisdome is this that is giuen vnto him, that euen such great workes are done by his hands?
Sa'adda ranar Asabar tazo ya shiga cikin masujada ya yi koyarwa. Mutane da yawa da su ka ji koyarwarsa su ka yi mamaki, suka ce daga ina ya sami irin wannan koyarwar? Wacce irin hikima ce Allah ya ba shi haka? Wadanne irin ayyukan al'ajibi ya ke yi da hannuwansa?
3 Is not this that carpenter Maries sonne, the brother of Iames and Ioses, and of Iuda and Simon? and are not his sisters here with vs? And they were offended in him.
Wannan ba kafintan nan ba ne dan Maryamu, dan'uwan Yakubu da Yosi da Yahuza da Saminu? Ba ga 'yan'uwan sa 'yan mata mu na tare da su ba? Ba su ji dadi ba a ransu saboda Yesu.
4 Then Iesus sayd vnto them, A Prophet is not without honour, but in his owne countrey, and among his owne kindred, and in his own house.
Yesu ya ce, “Annabi ba ya rasa daraja sai a gidansa da garinsa da cikin danginsa.”
5 And he could there doe no great workes, saue that hee layd his hands vpon a fewe sicke folke, and healed them,
Bai iya yin wani aikin al'ajibi a wurin ba sai dai mutane kadan marasa lafiya ya dorawa hannu ya warkar da su.
6 And he marueiled at their vnbeliefe, and went about by ye townes on euery side, teaching.
Rashin bangaskiyarsu ya ba shi mamaki. Sai ya tafi cikin kauyuka na kewaye da su ya yi ta koyarwa.
7 And he called vnto him the twelue, and began to send them forth two and two, and gaue them power ouer vncleane spirits,
Ya kira almajiransa su goma sha biyu, ya aike su biyu-biyu, ya ba su iko a kan aljanu,
8 And commanded them that they should take nothing for their iourney, saue a staffe onely: neither scrip, neither bread, neither money in their girdles:
ya dokace su kada su dauki komai tare da su domin wannan tafiya, sai dai sanda kadai. Kada su dauki abinci ko jaka ko kudi a cikin aljihunsu,
9 But that they should be shod with sandals, and that they should not put on two coates.
sai dai su sa takalmi kadai, kada su sa taguwa biyu a jikinsu.
10 And he sayd vnto them, Wheresoeuer ye shall enter into an house, there abide till ye depart thence.
Ya ce da su, idan ku ka shiga wani gida sai ku zauna a gidan har lokacin da za ku tashi.
11 And whosoeuer shall not receiue you, nor heare you, when ye depart thence, shake off the dust that is vnder your feete, for a witnes vnto them. Verely I say vnto you, It shalbe easier for Sodom, or Gomorrha at the day of iudgement, then for that citie.
Idan ku ka je wani gari aka ki karbar ku, ku karkabe kurar da ke kafufunku ta zama shaida kan mutanen garin.
12 And they went out, and preached, that men should amend their liues.
Sai suka tafi suka yi ta shela ga mutane cewa su tuba daga zunubansu.
13 And they cast out many deuils: and they anointed many that were sicke, with oyle, and healed them.
Sun fitar da aljanu da yawa, suka shafawa mutane da yawa mai suka warkar da su.
14 Then King Herod heard of him (for his name was made manifest) and sayd, Iohn Baptist is risen againe from the dead, and therefore great workes are wrought by him.
Sarki Hirudus ya ji wannan, gama sunan Yesu ya zama sananne a wurin kowa da kowa. Wadansu suna cewa Yahaya mai yin baftisma ne ya tashi daga matattu shi ya sa ake yin wadannan ayyukan al'ajibi ta wurinsa.
15 Other sayd, It is Elias, and some sayd, It is a Prophet, or as one of those Prophets.
Wadansu kuma suna cewa, “Iliya,” Har yanzu wadansu suna cewa daya “daga cikin annabawa ne na da can.”
16 So when Herod heard it, he said, It is Iohn whom I beheaded: he is risen from the dead.
Sa'adda Hirudus ya ji wannan sai ya ce, “Yahaya wanda na fillewa kai shine ya tashi.”
17 For Herod him selfe had sent forth, and had taken Iohn, and bound him in prison for Herodias sake, which was his brother Philippes wife, because he had maried her.
Saboda Hirudus ne ya sa aka kama Yahaya aka kulle shi a kurkuku saboda Hirodiya( matar Filibus dan'uwansa), domin ya aure ta.
18 For Iohn sayd vnto Herod, It is not lawfull for thee to haue thy brothers wife.
Saboda Yahaya ya gaya wa Hirudus cewa bai halarta ya auri matar dan'uwansa ba.
19 Therefore Herodias layd waite against him, and would haue killed him, but she could not:
Sai ita Hirodiya ta yi kudurin ta kashe Yahaya amma bai yiwu ba.
20 For Herod feared Iohn, knowing that hee was a iust man, and an holy, and reuerenced him, and when he heard him, he did many things, and heard him gladly.
Domin Hirudus yana jin tsoron Yahaya, domin ya sani shi mai adalci ce, mai tsarki kuma. Domin haka Hirudus bai so wani abu ya faru da Yahaya ba, amma ya kan fusata idan ya ji wa'azin yahaya. Duk da haka da fari ciki yakan saurare shi.
21 But the time being conuenient, when Herod on his birth day made a banket to his princes and captaines, and chiefe estates of Galile:
Amma sai dama ta samu inda Hirodiya za ta iya yin abin da ta ke so ta yi. A lokacin kewayowar ranar haihuwar sa, sai Hirudus ya shirya liyafa domin manyan da ke aiki tare da shi a cikin gwamnatin sa, da shugabannin da ke cikin Galili.
22 And the daughter of the same Herodias came in, and daunced, and pleased Herod, and them that sate at table together, the King sayd vnto the mayde, Aske of me what thou wilt, and I will giue it thee.
Diyar Hirodiya ta zo ta yi masu rawa, rawarta kuwa tagamshi Hirudus da bakinsa. Sarki ya ce da yarinyar, “ki tambayi duk abin da ki ke so ni kuwa zan ba ki shi”.
23 And he sware vnto her, Whatsoeuer thou shalt aske of me, I will giue it thee, euen vnto the halfe of my kingdome.
Ya rantse mata da cewa”Ko menene ki ka ce ki na so, ko da rabin mulkina ne”
24 So she went forth, and said to her mother, What shall I aske? And she said, Iohn Baptists head.
Sai ta fita ta je ta tambayi mamarta, “me zan ce ya bani?” Sai ta ce kan Yahaya Mai Yin Baftisma.
25 Then she came in straightway with haste vnto the King, and asked, saying, I would that thou shouldest giue me euen now in a charger the head of Iohn Baptist.
Sai ta dawo da sauri cikin dakin taro wurin sarki ta ce da shi, “Ina so ka ba ni kan Yahaya Mai Yin Baftisma a cikin tire.”
26 Then the King was very sory: yet for his othes sake, and for their sakes which sate at table with him, he would not refuse her.
Sarki ya damu kwarai, amma saboda ya yi alkawari ga kuma ofisoshinsa, ba dama ya ce a'a.
27 And immediatly the King sent the hangman, and gaue charge that his head shoulde be brought in. So he went and beheaded him in the prison,
Sai sarki ya aiki wani soja ya ba shi ummurni ya je ya kawo kan Yahaya. Sojan ya je ya fillo kan sa daga cikin kurkuku.
28 And brought his head in a charger, and gaue it to the maide, and the maide gaue it to her mother.
Ya kawo kan a cikin tire ya ba yarinyar, yarinyar kuma ta kai wa mamarta.
29 And when his disciples heard it, they came and tooke vp his body, and put it in a tombe.
Da almajiran su ka ji labari, suka zo suka dauki gawarsa suka rufe a cikin kabari.
30 And the Apostles gathered themselues together to Iesus, and tolde him all things, both what they had done, and what they had taught.
Almajiran suka zo wurin Yesu, suka fada masa dukkan abin da suka yi da abin da suka koyar.
31 And he sayd vnto them, Come ye apart into the wildernes, and rest a while: for there were many commers and goers, that they had not leasure to eate.
Sai ya ce da su “ku je cikin kebabben wuri domin ku huta kadan,” domin mutane suna ta kaiwa da komowa, ba su sami damar hutawa ba balle su ci abinci
32 So they went by ship out of the way into a desart place.
Sai suka tafi kebabben wuri a cikin jirgin ruwa su kadai.
33 But the people sawe them when they departed, and many knewe him, and ran a foote thither out of all cities, and came thither before them, and assembled vnto him.
Amma mutane da yawa sun gansu suna tafiya sun kuma gane su, sai suka fito daga cikin dukan garuruwa da gudu har su ka kai wurin kafin su zo.
34 Then Iesus went out, and sawe a great multitude, and had compassion on them, because they were like sheepe which had no shepheard: and he began to teach them many things.
Sa'adda suka zo bakin gaba Yesu ya ga taron mutane da yawa sai ya ji tausayinsu domin sun yi kamar tumakin da ba da mai kiwo. Sai ya cigaba da koya masu abubuwa da yawa.
35 And when the day was nowe farre spent, his disciples came vnto him, saying, This is a desart place, and nowe the day is farre passed.
Sa'adda yamma ta yi, almajiran sa suka zo suka ce da shi, “wurinnan kebabben wuri ne kuma ga lokaci ya tafi.
36 Let them depart, that they may goe into the countrey and townes about, and buy them bread: for they haue nothing to eate.
Ka sallami mutanen nan domin su shiga cikin garuruwa da kauyuka da ke kusa domin su sayi abin da zasu ci.
37 But he answered, and said vnto them, Giue yee them to eate. And they said vnto him, Shall we goe, and buy two hundreth peny worth of bread, and giue them to eate?
Amma sai ya ba su amsa ya ce,”Ku ku basu abinci su ci mana”. Sai suka ce da shi, “ma iya zuwa mu sawo gurasa ta sule dari biyu mu basu su ci?”
38 Then he sayde vnto them, Howe many loaues haue ye? goe and looke. And when they knewe it, they sayd, Fiue, and two fishes.
Sai ya ce dasu, “Dunkulen gurasa guda nawa kuke dasu? Kuje ku gani.” Dasuka gano sai suka ce da shi, dunkule biyar ne da kifi guda biyu.”
39 So he commanded them to make them all sit downe by companies vpon the greene grasse.
Sai ya ba da umarni mutanen su dukka su zauna a kan danyar ciyawa.
40 Then they sate downe by rowes, by hundreds, and by fifties.
Suka zauna kungiya kungiya wadansu su dari wadansu hamsin.
41 And he tooke the fiue loaues, and the two fishes, and looked vp to heauen, and gaue thanks, and brake the loaues, and gaue them to his disciples to set before them, and the two fishes he deuided among them all.
Sai ya dauki dunkulen gurasa guda biyar da kifi guda biyu, ya ta da kansa sama, yasa albarka, ya kakkarya dunkulen gurasan, ya ba almajiran domin su rabawa taron jama'a duka.
42 So they did all eate, and were satisfied.
Dukansu suka ci suka koshi.
43 And they tooke vp twelue baskets full of the fragments, and of the fishes.
Suka tattara gutsattsarin gurasar suka cika kwanduna guda goma sha biyu da gutsattsarin da kuma gutsattsarin kifin.
44 And they that had eaten, were about fiue thousand men.
Mutanen da suka ci gurasar sun kai mutum dubu biyar.
45 And straightway he caused his disciples to goe into the ship, and to goe before vnto the other side vnto Bethsaida, while he sent away the people.
Nan da nan ya ce almajiran sa su hau jirgin ruwa su yi gaba kafin ya zo, su je Baitsaida. Shi kuma ya tsaya domin ya sallami taron mutanen.
46 Then assoone as he had sent them away, he departed into a mountaine to pray.
Bayan da suka tafi shi kuma ya hau kan dutse domin ya yi addu'a.
47 And when euen was come, the ship was in the mids of the sea, and he alone on the land.
Har yamma ta yi jirgin ruwan ya na tsakiyar rafi shi kuma yana kan tudu shi kadai.
48 And he saw them troubled in rowing, (for the winde was contrary vnto them) and about the fourth watch of the night, hee came vnto them, walking vpon the sea, and would haue passed by them.
Ya gansu suna wahala gama iska ta hana su tafiya. Wajan karfe hudu na asuba sai ya tawo wurin su yana tafiya a kan ruwa, yana so ya wuce gaban su.
49 And when they saw him walking vpon the sea, they supposed it had bene a spirit, and cried out.
Sa'adda suka gan shi ya na tafiya a kan ruwa suka yi tsammani fatalwa ce, suka yi ihu,
50 For they all saw him, and were sore afrayd: but anon he talked with them, and said vnto them, Be ye of good comfort: it is I, be not afrayd.
gama su duka sun gan shi, tsoro ya kama su. Sai nan da nan ya yi magana dasu ya ce, “Ku karfafa ni ne! kada ku ji tsoro!''
51 Then he went vp vnto them into the ship, and the winde ceased, and they were much more amased in them selues, and marueiled.
Ya shiga cikin jirgin ruwan tare dasu, sai iska ta dena bugawa. Sai suka yi mamaki kwarai.
52 For they had not considered the matter of the loaues, because their hearts were hardened.
Gama basu gane batun dunkulen ba. Maimakon haka, sai zukatansu suka taurare.
53 And they came ouer, and went into the land of Gennesaret, and arriued.
Sa'adda suka haye su zo kasar Janisarita suka sa wa jirgin sarka.
54 So when they were come out of the ship, straightway they knewe him,
Su na fitowa daga cikin jirgin kenan, mutane suka gane cewa Yesu ne.
55 And ran about throughout all that region round about, and began to cary hither and thither in couches all that were sicke, where they heard that he was.
Mutane suka ruga cikin yankin su, suka kawo marasa lafiya a bisa shinfidun su zuwa wurinsa, dukan inda suka ji yana zuwa.
56 And whithersoeuer he entred into townes, or cities, or villages, they laide their sicke in the streetes, and prayed him that they might touch at the least the edge of his garment. And as many as touched him, were made whole.
Ko ina ya shiga birni da kauye, ko a cikin kasar sukan kawo marasa lafiya a kasuwanni suna rokonsa su taba ko da habar rigarsa, dukan wadanda suka taba kuwa suka warke.

< Mark 6 >