< Mark 14 >

1 And two daies after followed the feast of the Passeouer, and of vnleauened bread: and the hie Priests, and Scribes sought how they might take him by craft, and put him to death.
Idin Ketarewa da bukin gurasa mara yisti sauran kwana biyu kenan, sai shugabanin firistoci da malaman attaura suka nemi yadda zasu kama Yesu a asirce domin su kashe shi.
2 But they sayde, Not in the feast day, least there be any tumult among the people.
Suna cewa amma “Ba a lokacin idin ba, domin kada su haddasa hargitsi a tsakanin mutane”.
3 And when hee was in Bethania in the house of Simon the leper, as he sate at table, there came a woman hauing a boxe of oyntment of spikenarde, very costly, and shee brake the boxe, and powred it on his head.
Yesu yana Betanya a gidan Saminu kuturu, yana shirin liyafa kenan sai ga wata mace dauke da kwalbar turare mai tamanin kwarai, ta shafa masa a kansa.
4 Therefore some disdained among themselues, and sayde, To what ende is this waste of oyntment?
wasu dake tare da Yesu suka husata, suna kwalbarta da cewa
5 For it might haue bene sold for more then three hundreth pence, and bene giuen vnto the poore, and they murmured against her.
“Ai wannan turare ne mai tsada, ina laifin a sayar a raba wa talakawa kudin? ina dalilin wannan almubazaranci?
6 But Iesus saide, Let her alone: why trouble yee her? shee hath wrought a good worke on me.
Sai Yesu yace masu “Ku kyaleta, don me kuke tsauta mata,
7 For yee haue the poore with you alwaies, and when yee will yee may doe them good, but me yee shall not haue alwaies.
ai Idan kuna da niyyar taimakon talakawa ko matalauta, suna nan tare da ku ko a yaushe amma ni bazan kasance da ku kullum ba.
8 She hath done that she coulde: she came afore hand to anoynt my body to the burying.
Macen nan tayi aiki nagari domin shirya jikina ga jana'iza.
9 Verely I say vnto you, wheresoeuer this Gospel shall be preached throughout the whole world, this also that she hath done, shalbe spoken of in remembrance of her.
hakika, Ina gaya maku, duk inda za'a yi bishara a duniya baza a mance da matan nan da hidimar da ta tayi mini ba.”
10 Then Iudas Iscariot, one of the twelue, went away vnto the hie Priestes, to betray him vnto them.
Da jin haka sai Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin manzannin ya ruga zuwa wurin baban firist domin ya bashe shi a garesu,
11 And when they heard it, they were glad, and promised that they woulde giue him monie: therefore he sought howe he might conueniently betraie him.
Da mayan firistoci suka ji haka suka yi murna matuka tare da alkawarin kudi ga Yahuza, shi kuwa sai ya fara neman zarafin da zai mika Yesu a gare su.
12 Nowe the first day of vnleauened bread, when they sacrificed the Passeouer, his disciples sayde vnto him, Where wilt thou that we goe and prepare, that thou mayest eate the Passeouer?
A ranar farko ta bukin gurasa marar yisti da kuma hadayar ragon Idin ketarewa, almajiransa suka ce masa “Ina zamu shirya liyafar domin idin ketarewa?
13 Then hee sent foorth two of his disciples, and sayde vnto them, Goe yee into the citie, and there shall a man meete you bearing a pitcher of water: follow him.
Ya aiki biyu daga cikin almajiransa da cewa “Ku shiga cikin birnin, zaku tarar da wani mutum dauke da tullun ruwa.
14 And whithersoeuer he goeth in, say yee to the good man of the house, The Master sayeth, Where is the lodging where I shall eate the Passeouer with my disciples?
Duk gidan da ya shiga ku bishi, sai ku cewa mai gidan, malam yace “ina bukatar masauki domin hidimar idin ketarewa tare da almajiraina?”'
15 And he wil shewe you an vpper chamber which is large, trimmed and prepared: there make it readie for vs.
Zai kuwa nuna maku babban bene gyararre. Sai ku yi mana shiri a can.”
16 So his disciples went foorth, and came to the citie, and found as he had said vnto them, and made readie the Passeouer.
Da shigar almajiran cikin birnin, sai kome ya kasance yadda ya fada, su kuwa suka yi shirye shiryen idin ketarewar.
17 And at euen he came with the twelue.
Da maraice ta yi, sai ya tare da sha biyun.
18 And as they sate at table and did eate, Iesus said, Verely I say vnto you, that one of you shall betray me, which eateth with me.
Yayin da suke zazzaune a teburin suna cin abincin, sai Yesu ya ce “Hakika ina gaya maku wani da ke ci tare da ni a nan zai bashe ni”.
19 Then they began to be sorowful and to say to him one by one, Is it I? And another, Is it I?
Sai suka damu suka tambaye shi daya bayan daya suna cewa “Hakika bani bane ko?”
20 And he answered and sayde vnto them, It is one of the twelue that dippeth with mee in the platter.
Yesu ya amsa masu da cewa “Daya daga cikin sha biyu ne, wanda ke sa hannu tare da ni yanzu cikin tasar”.
21 Truely the Sonne of man goeth his way, as it is written of him: but woe bee to that man, by whome the Sonne of man is betrayed: it had beene good for that man, if hee had neuer beene borne.
Dan Mutum zai tafi ne yadda nassi ya umarta game da shi amma kaiton wanda zai bashe shi! “zai, fiye masa, dama ba a haife shi ba”.
22 And as they did eate, Iesus tooke the bread, and when hee had giuen thankes, he brake it and gaue it to them, and sayde, Take, eate, this is my bodie.
Lokacin da suke cin abincin, Yesu ya dauki gurasa ya sa albarka, ya gutsuttsura ta, sai ya basu yana cewa “Wannan jikinana ne”.
23 Also he tooke the cuppe, and when he had giuen thankes, gaue it to them: and they all dranke of it.
Ya kuma dauki koko, yayi godiya, ya basu, su kuwa suka sha daga kokon.
24 And he saide vnto them, This is my blood of that newe Testament, which is shed for many.
Ya ce “Wannan jinina ne na alkawari da an zubar ga yawancin mutane”.
25 Verely I say vnto you, I wil drinke no more of the fruit of ye vine vntill that day, that I drinke it newe in the kingdome of God.
Hakika, bazan kara sha daga wannan ruwan inabi ba sai a ranar da zan sha sabo cikin mulkin Allah.”
26 And when they had sung a Psalme, they went out to the mount of Oliues.
Bayan sun raira wakar yabo ga Allah, sai suka tafi wurin dutsen zaitun.
27 Then Iesus said vnto them, Al ye shall be offended by mee this night: for it is written, I will smite the shepheard, and the sheepe shall be scattered.
Yesu ya ce masu dukkan ku zaku yi tuntube harma ku fadi saboda ni gama rubuce take cewa “Zan buge makiyayin, tumakin kuwa za su watse;
28 But after that I am risen, I will goe into Galile before you.
Amma bayan tashina, zai yi gaba in riga ku zuwa Galili.
29 And Peter saide vnto him, Although all men should be offended at thee, yet would not I.
Bitrus ya ce masa “ko dukkansu sun fadi, faufau banda ni”.
30 Then Iesus saide vnto him, Verely I say vnto thee, this day, euen in this night, before the cocke crowe twise, thou shalt denie me thrise.
Yesu yace masa “Hakika ina gaya maka, cikin wannan dare kafin carar zakara ta biyu zaka yi musun sani na sau uku”.
31 But he saide more earnestly. If I shoulde die with thee, I will not denie thee: likewise also saide they all.
Amma Bitrus ya sake cewa “Koda za'a kasheni tare da kai ba zan yi musun sanin ka ba”. Dukkan su kuwa suka yi wannan Alkawari.
32 After, they came into a place named Gethsemane: then hee saide to his disciples, Sit yee here, till I haue praied.
Suka isa wani wuri da ake kira Getsamani, sai Yesu ya ce wa almajiransa “Ku dakata anan domin zan je inyi addu'a”.
33 And hee tooke with him Peter, and Iames, and Iohn, and hee began to be troubled, and in great heauinesse,
Sai ya dauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya. Ya fara jin wahala mutuka tare da damuwa kwarai.
34 And saide vnto them, My soule is very heauie, euen vnto the death: tarie here, and watch.
Sai ya ce masu “Raina na shan wahala harma kamar in mutu. Ku dakata a nan, ku zauna a fadake”.
35 So he went forward a litle, and fell downe on the ground, and praied, that if it were possible, that houre might passe from him.
Da Yesu yayi gaba kadan, sai ya fadi kasa yayi addu'a yana cewa idan mai yiwuwa ne “A dauke masa wannan sa'a daga gare shi.
36 And he saide, Abba, Father, all things are possible vnto thee: take away this cup from me: neuertheles not that I will, but that thou wilt, be done.
Ya ce “Ya Abba Uba, kome mai yuwane gare ka, ka dauke mini kokon wahalan nan, duk da haka ba nufina ba sai dai naka”.
37 Then hee came, and founde them sleeping, and said to Peter, Simon, sleepest thou? couldest not thou watche one houre?
Da komowarsa ya same su suna barci, sai ya ce wa Bitrus, Siman barci kake? Ashe, ba za ka iya zama a fadake ko da sa'a daya ba?
38 Watch ye, and pray, that ye enter not into tentation: the spirite in deede is ready, but the flesh is weake.
Ku zauna a fadake, kuyi addu'a kada ku fada cikin jaraba. Lalle ruhu na da niyya amma jiki raunana ne.
39 And againe hee went away, and praied, and spake the same wordes.
Sai ya sake komawa, yayi addu'a, yana maimaita kalmominsa na farko.
40 And he returned, and founde them a sleepe againe: for their eyes were heauie: neither knewe they what they should answere him.
Har wa yau kuma ya sake dawowa, ya same su suna barci don barci ya cika masu idanu kwarai, sun kuwa kasa ce masa kome.
41 And he came the third time, and said vnto them, Sleepe henceforth, and take your rest: it is ynough: the houre is come: beholde, the Sonne of man is deliuered into the hands of sinners.
Ya sake komowa karo na uku yace masu “har yanzu barci kuke yi kuna hutawa? Ya isa haka! Lokaci yayi, an bada Dan Mutum ga masu zunubi”.
42 Rise vp: let vs go: loe, he that betraieth me, is at hand.
Ku tashi mutafi kun ga, ga mai bashe ni nan ya kusato.”
43 And immediatly while hee yet spake, came Iudas that was one of the twelue, and with him a great multitude with swordes and staues from the hie Priests, and Scribes, and Elders.
Nan da nan, kafin ya rufe baki sai ga Yahuza, daya daga cikin sha biyun da taron jama'a rike da takkuba da kulake. Manyan firistoci da malaman attaura da shugabanni suka turo su.
44 And he that betraied him, had giuen them a token, saying, Whomsoeuer I shall kisse, he it is: take him and leade him away safely.
Mai bashe shi din nan ya riga ya kulla da su cewa “Wanda zan yi wa sumba shine mutumin, ku kama shi ku tafi da shi a tsare.
45 And assoone as hee was come, hee went straightway to him, and saide, Haile Master, and kissed him.
Da isowarsa kuwa, sai ya zo wurin Yesu ya ce “Ya malam!”. Sai ya sumbace shi.
46 Then they laide their handes on him, and tooke him.
Su kuwa suka kama shi, suka tafi da shi.
47 And one of them that stoode by, drewe out a sword, and smote a seruant of the hie Priest, and cut off his eare.
Amma daya daga cikin na tsaye ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya yanke masa kunne.
48 And Iesus answered and saide to them, Ye be come out as against a thiefe with swordes, and with staues, to take me.
Sai Yesu ya ce “kun fito kamar masu kama yan fashi da takkuba da kulake, domin ku kama ni?
49 I was daily with you teaching in the Temple, and yee tooke me not: but this is done that the Scriptures should be fulfilled.
Lokacin da nake koyarwa a Haikali, kowace rana da ku, baku kama ni ba. Amma anyi haka ne domin a cika abinda Nassi ya fada.”
50 Then they all forsooke him, and fled.
Daga nan duk wadanda suke tare da Yesu suka yashe shi, suka tsere.
51 And there followed him a certaine yong man, clothed in linnen vpon his bare bodie, and the yong men caught him.
Wani saurayi, daga shi sai mayafi ya bi shi, suka kai masa cafka.
52 But he left his linnen cloth, and fled from them naked.
Shi kuwa ya bar masu mayafin ya gudu tsirara.
53 So they led Iesus away to the hie Priest, and to him came together all the hie Priestes, and the Elders, and the Scribes.
Daga nan suka tafi da Yesu wurin babban firist. a can suka tara dattawa duk da manyan firistoci da shugabanni da marubuta, suka taru a wurinsa.
54 And Peter folowed him afarre off, euen into the hall of the hie Priest, and sate with the seruants, and warmed himselfe at the fire.
Bitrus kuwa ya bi shi daga nesa har cikin gidan babban firist. Ya zauna tare da dogaran Haikalin, yana jin dumin wuta.
55 And the hie Priests, and all the Councill sought for witnesse against Iesus, to put him to death, but found none.
Sai, manyan firistoci da duk 'yan majalisa Yahudawa suka nemi shaidar da za a tabbatar a kan Yesu, don su samu su kashe shi. Amma basu samu ba.
56 For many bare false witnesse against him, but their witnesse agreed not together.
Da yawa kuma suka yi masa shaidar Zur (Karya), amma bakin su bai zama daya ba.
57 Then there arose certaine, and bare false witnesse against him, saying,
Sai wadansu kuma suka taso suka yi masa shaidar zur (karya) suka ce.
58 We hearde him say, I will destroy this Temple made with hands, and within three daies I will builde another, made without hands.
“Mun ji ya ce, wai zai rushe haikalin nan da mutane suka gina, ya sake gina wani cikin kwana uku, ba kuwa ginin mutum ba”.
59 But their witnesse yet agreed not together.
Duk da haka, sai shaidar tasu bata zo daya ba.
60 Then the hie Priest stoode vp amongst them, and asked Iesus, saying, Answerest thou nothing? what is the matter that these beare witnesse against thee?
Sai babban firist ya mike a tsakanin su, ya tambayi Yesu yace “Ba ka da wata amsa game da shaidar da mutanen nan suke yi a kanka?
61 But hee helde his peace, and answered nothing. Againe the hie Priest asked him, and sayde vnto him, Art thou that Christ the Sonne of the Blessed?
Amma yayi shiru abinsa, bai ce kome ba. Sai babban firist din ya sake tambayarsa “To, ashe kai ne Allmasihu Dan Madaukaki?
62 And Iesus said, I am he, and yee shall see the Sonne of man sitte at the right hande of the power of God, and come in the clouds of heauen.
Yesu ya ce “Nine. Za ku kuwa ga Dan Mutum zaune dama ga mai iko, yana kuma zuwa cikin gajimare”.
63 Then the hie Priest rent his clothes, and sayd, What haue we any more neede of witnesses?
Sai babban firist ya kyakketa tufafinsa yace “Wacce shaida kuma zamu nema?
64 Ye haue heard the blasphemie: what thinke yee? And they all condemned him to be worthie of death.
Kun dai ji sabon da yayi! Me kuka gani? Duk suka yanke masa hukunci akan ya cancanci kisa.
65 And some began to spit at him, and to couer his face, and to beate him with fists, and to say vnto him, Prophesie. And the sergeants smote him with their roddes.
Wadansu ma suka fara tottofa masa yau, suka daure masa idanu, suka bubbuge shi suna cewa “Yi annabci” Dogaran kuma suka yi ta marinsa.
66 And as Peter was beneath in the hal, there came one of the maides of the hie Priest.
Bitrus kuwa na kasa a filin gida, sai wata baranyar babban firist ta zo.
67 And when shee sawe Peter warming him selfe, shee looked on him, and sayde, Thou wast also with Iesus of Nazareth.
Da ta ga Bitrus na jin dumi, ta yi masa kallon gaske ta ce “Kaima ai tare kake da banazaren nan Yesu”.
68 But he denied it, saying, I knowe him not, neither wot I what thou saiest. Then he went out into the porche, and the cocke crewe.
Amma ya musa ya ce “Ni ban ma san abinda kike fada ba balle in fahimta”. Sai ya fito zaure. Sai zakara yayi cara.
69 Then a maid sawe him againe, and bega to say to them that stood by, This is one of them.
Sai baranyar ta ganshi, ta sake ce wa wadanda ke tsaitsaye a wurin, “Wannan ma daya daga cikinsu ne”.
70 But hee denied it againe: and anon after, they that stoode by, sayde againe to Peter, Surely thou art one of them: for thou art of Galile, and thy speach is like.
Amma ya sake musawa, jim kadan sai na tsaitsayen suka ce wa Bitrus “Lalle kai ma dayansu ne don ba Galile ne kai”.
71 And he began to curse, and sweare, saying, I knowe not this man of whom ye speake.
Sai ya fara la'anta kansa yana ta rantsuwa yana ce wa “Ban ma san mutumin nan da kuke fada ba”.
72 Then the seconde time the cocke crewe, and Peter remembred the woorde that Iesus had saide vnto him, Before the cocke crowe twise, thou shalt denie me thrise, and waying that with himselfe, he wept.
Nan da nan sai zakara ya yi cara ta biyu, Bitrus kuwa ya tuna da maganar Yesu a gare shi cewa “Kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi musun sani na sau uku”. Da ya tuno haka, sai ya fashe da kuka.

< Mark 14 >