< Mark 14 >
1 And two daies after followed the feast of the Passeouer, and of vnleauened bread: and the hie Priests, and Scribes sought how they might take him by craft, and put him to death.
To, saura kwana biyu ne kaɗai a yi Bikin Ƙetarewa da Bikin Burodi Marar Yisti, sai manyan firistoci da malaman dokoki, suka nemi wani dalili su kama Yesu a ɓoye, su kashe.
2 But they sayde, Not in the feast day, least there be any tumult among the people.
Suka ce, “Ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su yi tawaye.”
3 And when hee was in Bethania in the house of Simon the leper, as he sate at table, there came a woman hauing a boxe of oyntment of spikenarde, very costly, and shee brake the boxe, and powred it on his head.
Yayinda yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu, yana cin abinci, sai wata mace ta zo da wani ɗan tulu na turaren alabasta da aka yi da nardi zalla, mai tsadan gaske. Ta fasa tulun, ta kuma zuba turaren a kansa.
4 Therefore some disdained among themselues, and sayde, To what ende is this waste of oyntment?
Waɗansu daga cikin waɗanda suke wurin, suka ji haushi, suka ce wa juna, “Me ya sa za a ɓata turaren nan haka?
5 For it might haue bene sold for more then three hundreth pence, and bene giuen vnto the poore, and they murmured against her.
Da an sayar da shi, ai, da an sami kuɗi fiye da albashi ma’aikaci na shekara guda, a ba wa matalauta. Sai suka tsawata mata da zafi.”
6 But Iesus saide, Let her alone: why trouble yee her? shee hath wrought a good worke on me.
Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta mana. Don me kuke damunta? Ta yi abu mai kyau a gare ni.
7 For yee haue the poore with you alwaies, and when yee will yee may doe them good, but me yee shall not haue alwaies.
Matalauta dai suna tare da ku kullum, za ku kuma iya taimakonsu a duk lokacin da kuke so. Amma ni ba zan kasance da ku kullum ba.
8 She hath done that she coulde: she came afore hand to anoynt my body to the burying.
Ta yi abin da ta iya yi. Ta zuba turare a jikina kafin lokaci, don shirin jana’izata.
9 Verely I say vnto you, wheresoeuer this Gospel shall be preached throughout the whole world, this also that she hath done, shalbe spoken of in remembrance of her.
Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bishara ko’ina a duniya, za a faɗi abin da ta yi, domin tunawa da ita.”
10 Then Iudas Iscariot, one of the twelue, went away vnto the hie Priestes, to betray him vnto them.
Sai Yahuda Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, ya je wajen manyan firistoci don yă bashe Yesu a gare su.
11 And when they heard it, they were glad, and promised that they woulde giue him monie: therefore he sought howe he might conueniently betraie him.
Suka yi murna da jin haka, suka yi alkawari za su ba shi kuɗi. Don haka, ya fara neman zarafi yă ba da shi.
12 Nowe the first day of vnleauened bread, when they sacrificed the Passeouer, his disciples sayde vnto him, Where wilt thou that we goe and prepare, that thou mayest eate the Passeouer?
A rana ta fari ta Bikin Burodi Marar Yisti, lokacin da akan yanka ɗan ragon hadayar kafara, bisa ga al’ada ta tunawa da Bikin Ƙetarewa, sai almajiran Yesu suka tambaye shi, suka ce, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin da za ka ci Bikin Ƙetarewa?”
13 Then hee sent foorth two of his disciples, and sayde vnto them, Goe yee into the citie, and there shall a man meete you bearing a pitcher of water: follow him.
Sai ya aiki biyu daga cikin almajiransa ya ce, “Ku shiga cikin birni, za ku sadu da wani ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi.
14 And whithersoeuer he goeth in, say yee to the good man of the house, The Master sayeth, Where is the lodging where I shall eate the Passeouer with my disciples?
Gidan da ya shiga, ku gaya wa maigidan cewa, ‘Malam yana tambaya, ina ɗakin baƙina, inda zan ci Bikin Ƙetarewa tare da almajiraina?’
15 And he wil shewe you an vpper chamber which is large, trimmed and prepared: there make it readie for vs.
Zai nuna muku wani babban ɗakin sama da aka shirya domin baƙi. Ku yi mana shirin a can.”
16 So his disciples went foorth, and came to the citie, and found as he had said vnto them, and made readie the Passeouer.
Almajiran suka tafi, suka shiga cikin birnin, suka kuwa tarar da kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
17 And at euen he came with the twelue.
Da yamma ta yi, sai Yesu ya zo tare da Sha Biyun.
18 And as they sate at table and did eate, Iesus said, Verely I say vnto you, that one of you shall betray me, which eateth with me.
Yayinda suke cin abinci a tebur, sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, ɗaya daga cikinku zai bashe ni, wani wanda yake ci tare da ni.”
19 Then they began to be sorowful and to say to him one by one, Is it I? And another, Is it I?
Suka cika da baƙin ciki, da ɗaya-ɗaya suka ce masa, “Tabbatacce, ba ni ba ne, ko?”
20 And he answered and sayde vnto them, It is one of the twelue that dippeth with mee in the platter.
Ya ce, “Ɗaya daga cikin Sha Biyun ne, wanda yake ci tare da ni a kwano.
21 Truely the Sonne of man goeth his way, as it is written of him: but woe bee to that man, by whome the Sonne of man is betrayed: it had beene good for that man, if hee had neuer beene borne.
Ɗan Mutum zai tafi kamar yadda yake a rubuce game da shi, amma kaiton mutumin da ya bashe Ɗan Mutum! Zai fi masa, da ba a haife shi ba.”
22 And as they did eate, Iesus tooke the bread, and when hee had giuen thankes, he brake it and gaue it to them, and sayde, Take, eate, this is my bodie.
Yayinda suke cin abinci, sai Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya, ya ba wa almajiransa, yana cewa, “Ku karɓa, wannan jikina ne.”
23 Also he tooke the cuppe, and when he had giuen thankes, gaue it to them: and they all dranke of it.
Sai kuma ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, ya kuma miƙa musu, dukansu suka sha daga ciki.
24 And he saide vnto them, This is my blood of that newe Testament, which is shed for many.
Sai ya ce musu, “Wannan jinina ne na alkawari, wanda aka zubar da shi saboda mutane da yawa.
25 Verely I say vnto you, I wil drinke no more of the fruit of ye vine vntill that day, that I drinke it newe in the kingdome of God.
Gaskiya nake gaya muku, ‘Ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai ranan nan, da zan sha shi sabo a mulkin Allah.’”
26 And when they had sung a Psalme, they went out to the mount of Oliues.
Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
27 Then Iesus said vnto them, Al ye shall be offended by mee this night: for it is written, I will smite the shepheard, and the sheepe shall be scattered.
Yesu ya ce musu, “Dukanku za ku ja da baya ku bar ni, gama yana a rubuce cewa, “‘Zan bugi makiyayin tumaki, tumakin kuwa za su warwatse.’
28 But after that I am risen, I will goe into Galile before you.
Amma bayan na tashi, zan sha gabanku zuwa Galili.”
29 And Peter saide vnto him, Although all men should be offended at thee, yet would not I.
Bitrus ya ce, “Ko da duka sun ja da baya suka bar ka, ba zan bar ka ba.”
30 Then Iesus saide vnto him, Verely I say vnto thee, this day, euen in this night, before the cocke crowe twise, thou shalt denie me thrise.
Yesu ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, yau, tabbatacce, a daren nan, kafin zakara yă yi cara sau biyukai da kanka za ka yi mūsun sanina sau uku.”
31 But he saide more earnestly. If I shoulde die with thee, I will not denie thee: likewise also saide they all.
Amma Bitrus ya yi ta nanatawa da ƙarfi ya ce, “Ko da zan mutu tare da kai, ba zan taɓa yin mūsun saninka ba.” Duk sauran ma suka ce haka.
32 After, they came into a place named Gethsemane: then hee saide to his disciples, Sit yee here, till I haue praied.
Suka tafi wani wurin da ake kira Getsemane, Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Ku zauna a nan, yayinda ni kuwa in yi addu’a.”
33 And hee tooke with him Peter, and Iames, and Iohn, and hee began to be troubled, and in great heauinesse,
Ya tafi tare da Bitrus, Yaƙub da kuma Yohanna. Sai ya fara baƙin ciki da damuwa ƙwarai.
34 And saide vnto them, My soule is very heauie, euen vnto the death: tarie here, and watch.
Sai ya ce musu, “Raina yana cike da baƙin ciki har ma kamar zan mutu. Ku dakata a nan ku yi tsaro.”
35 So he went forward a litle, and fell downe on the ground, and praied, that if it were possible, that houre might passe from him.
Sai ya yi gaba kaɗan, ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a, ya ce in mai yiwuwa ne, a ɗauke masa wannan sa’a.
36 And he saide, Abba, Father, all things are possible vnto thee: take away this cup from me: neuertheles not that I will, but that thou wilt, be done.
Ya ce, “Ya Abba, Uba, kome mai yiwuwa ne a gare ka. Ka ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba abin da nake so ba, sai dai abin da kake so.”
37 Then hee came, and founde them sleeping, and said to Peter, Simon, sleepest thou? couldest not thou watche one houre?
Sai ya koma wajen almajiransa, ya same su suna barci. Ya ce wa Bitrus, “Siman, kana barci ne? Ka kāsa yin tsaro na sa’a ɗaya?
38 Watch ye, and pray, that ye enter not into tentation: the spirite in deede is ready, but the flesh is weake.
Ku yi tsaro, ku kuma yi addu’a, domin kada ku fāɗi cikin jarraba. Ruhu yana so, sai dai jiki raunana ne.”
39 And againe hee went away, and praied, and spake the same wordes.
Ya sāke komawa, ya maimaita addu’ar da ya yi.
40 And he returned, and founde them a sleepe againe: for their eyes were heauie: neither knewe they what they should answere him.
Da ya dawo, ya sāke tarar da su suna barci, domin barci ya cika musu ido. Suka rasa abin da za su ce masa.
41 And he came the third time, and said vnto them, Sleepe henceforth, and take your rest: it is ynough: the houre is come: beholde, the Sonne of man is deliuered into the hands of sinners.
Da ya koma sau na uku, sai ya ce musu, “Har yanzu kuna barci, kuna hutawa ba? Ya isa! Lokaci ya yi. Duba an ba da Ɗan Mutum a hannun masu zunubi.
42 Rise vp: let vs go: loe, he that betraieth me, is at hand.
Ku tashi! Mu tafi! Ga mai bashe ni ɗin yana zuwa!”
43 And immediatly while hee yet spake, came Iudas that was one of the twelue, and with him a great multitude with swordes and staues from the hie Priests, and Scribes, and Elders.
Yana cikin magana ke nan, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun ya bayyana. Ya zo tare da taro da suke riƙe da takuba da sanduna. Manyan firistoci da malaman dokoki, da kuma dattawa ne suka turo taron.
44 And he that betraied him, had giuen them a token, saying, Whomsoeuer I shall kisse, he it is: take him and leade him away safely.
Mai bashe shi ɗin ya riga ya shirya alama da su cewa, “Wanda na yi wa sumba, shi ne mutumin, ku kama shi, ku riƙe sosai.”
45 And assoone as hee was come, hee went straightway to him, and saide, Haile Master, and kissed him.
Nan da nan Yahuda ya je wurin Yesu ya ce, “Rabbi!” Ya kuma yi masa sumba.
46 Then they laide their handes on him, and tooke him.
Mutanen kuwa suka kama Yesu, suka riƙe shi.
47 And one of them that stoode by, drewe out a sword, and smote a seruant of the hie Priest, and cut off his eare.
Sai wani cikin waɗanda suke tsattsaye kusa ya zāre takobinsa, ya sare kunnen bawan babban firist.
48 And Iesus answered and saide to them, Ye be come out as against a thiefe with swordes, and with staues, to take me.
Yesu ya ce, “Ina jagoran wani tawaye ne da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni?
49 I was daily with you teaching in the Temple, and yee tooke me not: but this is done that the Scriptures should be fulfilled.
Kowace rana ina tare da ku, ina koyarwa a filin haikali, ba ku kama ni ba. Amma dole a cika Nassi.”
50 Then they all forsooke him, and fled.
Sai kowa ya yashe shi ya gudu.
51 And there followed him a certaine yong man, clothed in linnen vpon his bare bodie, and the yong men caught him.
Wani saurayin da ba ya sanye da kome sai rigar lilin, yana bin Yesu. Da suka yi ƙoƙarin kama shi,
52 But he left his linnen cloth, and fled from them naked.
sai ya gudu ya bar rigarsa, ya gudu tsirara.
53 So they led Iesus away to the hie Priest, and to him came together all the hie Priestes, and the Elders, and the Scribes.
Suka kai Yesu wajen babban firist, sai dukan manyan firistoci, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru.
54 And Peter folowed him afarre off, euen into the hall of the hie Priest, and sate with the seruants, and warmed himselfe at the fire.
Bitrus ya bi shi daga nesa, har cikin filin gidan babban firist. A can, ya zauna tare da masu gadi, yana jin ɗumin wuta.
55 And the hie Priests, and all the Councill sought for witnesse against Iesus, to put him to death, but found none.
Manyan firistoci da dukan’yan Majalisa, suka shiga neman shaidar laifin da za a tabbatar a kan Yesu, domin su kashe shi. Amma ba su sami ko ɗaya ba.
56 For many bare false witnesse against him, but their witnesse agreed not together.
Da yawa suka ba da shaidar ƙarya a kansa, amma shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.
57 Then there arose certaine, and bare false witnesse against him, saying,
Sai waɗansu suka miƙe tsaye, suka ba da wannan shaida ƙarya a kansa, suka ce,
58 We hearde him say, I will destroy this Temple made with hands, and within three daies I will builde another, made without hands.
“Mun ji shi ya ce, ‘Zan rushe wannan haikali da mutum ya gina, cikin kwana uku, in sāke gina wani wanda ba ginin mutum ba.’”
59 But their witnesse yet agreed not together.
Duk da haka ma, shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.
60 Then the hie Priest stoode vp amongst them, and asked Iesus, saying, Answerest thou nothing? what is the matter that these beare witnesse against thee?
Sai babban firist ya tashi a gabansu, ya tambayi Yesu ya ce, “Ba za ka amsa ba? Wane shaida ke nan waɗannan mutane suke kawowa a kanka?”
61 But hee helde his peace, and answered nothing. Againe the hie Priest asked him, and sayde vnto him, Art thou that Christ the Sonne of the Blessed?
Amma Yesu ya yi shiru, bai kuwa amsa ba. Babban firist ya sāke tambayarsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Mai Albarka?”
62 And Iesus said, I am he, and yee shall see the Sonne of man sitte at the right hande of the power of God, and come in the clouds of heauen.
Yesu ya ce, “Ni ne. Za ku kuwa ga Ɗan Mutum yana zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a cikin gizagizan sama.”
63 Then the hie Priest rent his clothes, and sayd, What haue we any more neede of witnesses?
Babban firist ya yage tufafinsa, ya yi ce, “Ina dalilin neman waɗansu shaidu kuma?
64 Ye haue heard the blasphemie: what thinke yee? And they all condemned him to be worthie of death.
Kun dai ji saɓon. Me kuka gani?” Duka suka yanke masa hukuncin kisa.
65 And some began to spit at him, and to couer his face, and to beate him with fists, and to say vnto him, Prophesie. And the sergeants smote him with their roddes.
Sai waɗansu suka fara tattofa masa miyau, suka rufe masa idanu, suka bubbuge shi da hannuwansu, suka ce, “Yi annabci!” Masu gadin kuma suka ɗauke shi, suka yi masa duka.
66 And as Peter was beneath in the hal, there came one of the maides of the hie Priest.
Yayinda Bitrus yake ƙasa a filin gidan, sai wata yarinya, baiwa, ɗaya daga cikin ma’aikatan babban firist, ta zo can.
67 And when shee sawe Peter warming him selfe, shee looked on him, and sayde, Thou wast also with Iesus of Nazareth.
Da ta ga Bitrus yana jin ɗumi, sai ta dube shi da kyau. Ta ce, “Kai ma kana tare da Yesu, Banazare.”
68 But he denied it, saying, I knowe him not, neither wot I what thou saiest. Then he went out into the porche, and the cocke crewe.
Amma ya yi mūsu ya ce, “Ban san abin da kike magana ba, balle ma in fahimce ki.” Sai ya fita zuwa zaure.
69 Then a maid sawe him againe, and bega to say to them that stood by, This is one of them.
Da baiwar ta gan shi a can, sai ta sāke gaya wa waɗanda suke tsattsaye a wurin, ta ce, “Wannan mutum yana ɗaya daga cikinsu.”
70 But hee denied it againe: and anon after, they that stoode by, sayde againe to Peter, Surely thou art one of them: for thou art of Galile, and thy speach is like.
Sai ya sāke yin musu. Bayan ɗan lokaci kaɗan, sai waɗanda suke tsattsaye kusa suka ce wa Bitrus, “Lalle, kana ɗaya daga cikinsu, gama kai mutumin Galili ne.”
71 And he began to curse, and sweare, saying, I knowe not this man of whom ye speake.
Sai ya fara la’antar kansa, yana rantsuwa musu, yana cewa, “Ban san wannan mutumin da kuke magana a kai ba.”
72 Then the seconde time the cocke crewe, and Peter remembred the woorde that Iesus had saide vnto him, Before the cocke crowe twise, thou shalt denie me thrise, and waying that with himselfe, he wept.
Nan da nan zakara ya yi cara sau na biyu. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya yi masa cewa, “Kafin zakara yă yi cara sau biyu, za ka yi mūsun sanina sau uku.” Sai ya fashe da kuka.