< Mark 11 >

1 And when they came neere to Hierusalem, to Bethphage and Bethania vnto the mount of Oliues, he sent forth two of his disciples,
Da suka kusa Urushalima, kusa da Betafaji, da Betanya, wajen dutsen zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa biyu
2 And sayd vnto them, Goe your wayes into that towne that is ouer against you, and assoone as ye shall enter into it, ye shall finde a colte tied, whereon neuer man sate: loose him, and bring him.
ya ce masu, “ku shiga kauyen can kusa da mu. Da zarar kun shiga za ku ga aholaki a daure, wanda ba a taba hawa ba. Ku kwance shi, ku kawo mani.
3 And if any man say vnto you, Why doe ye this? Say that the Lord hath neede of him, and straightway he will send him hither.
In wani ya ce maku, “Don me kuke haka? ku ce, 'Ubangiji ne yake bukatarsa, zai kuma komo da shi nan da nan.”'
4 And they went their way, and found a colt tyed by the doore without, in a place where two wayes met, and they loosed him.
Sai suka tafi, suka tadda aholakin a daure a kofar gida a bakin hanya, suka kwance shi.
5 Then certaine of them, that stoode there, sayd vnto them, What doe ye loosing the colt?
sai wadanda suke tsaye a gun suka ce masu, “Don me kuke kwance aholakin nan?
6 And they sayde vnto them, as Iesus had commanded them: So they let them goe.
Suka fada masu abinda Yesu yace, sai suka kyale su suka tafi.
7 And they brought the colte to Iesus, and cast their garments on him, and he sate vpon him.
Almajiran nan biyu suka kawo wa Yesu aholakin, suka shimfida mayafansu a kai, sai ya hau.
8 And many spred their garments in the way: other cut downe branches off the trees, and strawed them in the way.
Sai mutane da yawa suka shimfida mayafansu a hanya, wadansu kuma suka baza ganyen da suka yanko daga filayen.
9 And they that went before, and they that folowed, cryed, saying, Hosanna: blessed be hee that commeth in the Name of the Lord.
Wadanda suke gaba da shi da wadanda ke bin bayansa suka yi sowa suna cewa, “Hosanna! Albarka ta tabbata ga mai zuwa cikin sunan Ubangiji.
10 Blessed be the kingdome that commeth in the Name of the Lord of our father Dauid: Hosanna, O thou which art in the highest heauens.
Albarka ta tabbata ga mulkin nan mai zuwa na Ubanmu Dawuda! Dukaka a cikin sama!”
11 So Iesus entred into Hierusalem, and into the Temple: and when he had looked about on all things, and now it was euening, he went forth vnto Bethania with the twelue.
San nan Yesu ya shiga Urushalima, ya shiga Haikalin. Sai ya dudduba komai, da magariba ta yi, ya fita ya tafi Betanya tare da goma sha biyu nan.
12 And on the morowe when they were come out from Bethania, he was hungry.
Kashe gari, suka tashi daga Betanya, sai ya ji yunwa.
13 And seeing a fig tree afarre off, that had leaues, he went to see if he might finde any thing thereon: but when he came vnto it, hee found nothing but leaues: for the time of figges was not yet.
Da ya hango itacen baure mai ganye daga nesa sai ya je ya ga ko za sami 'ya'ya. Da ya iso wurinsa bai ga komai ba sai ganye, don ba lokacin 'ya'yan baure ba ne.
14 Then Iesus answered, and sayd to it, Neuer man eate fruite of thee hereafter while the world standeth: and his disciples heard it. (aiōn g165)
Sai ya ce wa bauren, “Kada kowa ya kara cin ''ya'yanka har abada!” Almajiransa kuwa sun ji maganar. (aiōn g165)
15 And they came to Hierusalem, and Iesus went into the Temple, and began to cast out them that solde and bought in the Temple, and ouerthrewe the tables of the money changers, and the seates of them that solde doues.
Suka iso Urushalima, da shigar su, ya kori masu saye da sayarwa, ya watsar da taburan 'yan canjin kudi, da kujerun masu sayar da tantabaru.
16 Neither would hee suffer that any man should cary a vessell through the Temple.
Ya hana kowa ya dauki wani abu da za a i ya sayarwa a cikin haikalin.
17 And he taught, saying vnto them, Is it not written, Mine house shalbe called the house of prayer vnto all nations? but you haue made it a denne of theeues.
Sai ya koyar da su cewa, “Ashe ba rubuce yake ba, “Za a kira gidana gidan addu'a na dukan al'ummai? Amma ku kun mayar da shi kogon yan fashi”.
18 And the Scribes and hie Priestes heard it, and sought howe to destroy him: for they feared him, because the whole multitude was astonied at his doctrine.
Da mayan Faristoci da marubutan attaura suka ji maganar da ya yi, sai suka nami hanyar da za su kashe shi. Amma suka ji tsoronsa domin dukkan taron na mamakin koyarwarsa.
19 But when euen was come, Iesus went out of the citie.
Kowace yamma kuma, sukan fita gari.
20 And in the morning as they iourneyed together, they saw the figge tree dried vp from the rootes.
Da safe suna wucewa, sai suka ga bauren nan ya bushe.
21 Then Peter remembred, and said vnto him, Master, beholde, the figge tree which thou cursedst, is withered.
Bitrus kuwa ya tuna ya ce “Malam, dubi! Baurenan da ka la'anta ya bushe.”
22 And Iesus answered, and said vnto them, Haue the faith of God.
Yesu ya amsa masu ya ce, “ku gaskata da Allah.”
23 For verely I say vnto you, that whosoeuer shall say vnto this mountaine, Be thou taken away, and cast into the sea, and shall not wauer in his heart, but shall beleeue that those things which he saieth, shall come to passe, whatsoeuer he saieth, shall be done to him.
Hakika, ina gaya maku, duk wanda ya ce wa dutsen nan tashi ka fada cikin tekun', bai kuwa yi shakka a zuciyarsa ba, amma ya gaskata haka kuwa zai faru, haka kuwa Allah zai yi.
24 Therefore I say vnto you, Whatsoeuer ye desire when ye pray, beleeue that ye shall haue it, and it shalbe done vnto you.
Saboda haka ina dai gaya maku, komai kuka yi addu'a kuka roka, ku gaskata cewa samamme ne, zai kuma zama naku.
25 But when ye shall stand, and pray, forgiue, if ye haue any thing against any man, that your Father also which is in heauen, may forgiue you your trespasses.
Duk sa'add da kuke addu'a ku gafarta wa wadanda suka yi maku laifi, domin Ubanku shima zai gafarta maku naku laifi.”
26 For if you will not forgiue, your Father which is in heauen, will not pardon you your trespasses.
(Amma in baku gafartawa mutane laifofinsu ba, Ubanku ma da ke sama ba zai gafarta maku ba.)
27 Then they came againe to Hierusalem: and as he walked in the Temple, there came to him ye hie Priestes, and the Scribes, and the Elders,
Da suka sake dawowa Urushalima. Yasu na tafiya cikin haikali, sai manyan firistoci, da marubuta, da dattawa suka zo wurinsa,
28 And said vnto him, By what authoritie doest thou these things? and who gaue thee this authoritie, that thou shouldest doe these things?
suka ce masa, “Da wanne iko kake yin wadanan abubuwa? Ko kuwa wa ya ba ka ikon yinsu? “
29 Then Iesus answered, and saide vnto them, I will also aske of you a certaine thing, and answere ye me, and I will tell you by what authoritie I do these things.
Sai Yesu ya ce masu, “Zan yi maku wata tambaya. ku ba ni amsa, ni kuwa zan gaya maku ko da wanne iko ne nake yin wadannan abubuwan.
30 The baptisme of Iohn, was it from heauen, or of men? answere me.
Baftismar da Yahaya yayi, daga sama take ko kuwa daga mutum take? ku bani amsa”.
31 And they thought with themselues, saying, If we shall say, From heauen, he will say, Why then did ye not beleeue him?
Sai suka yi mahuwara da juna, suka ce, “in kuwa muka ce, 'daga sama take,' za ya ce, “To, don me ba ku gaskata shi ba?
32 But if we say, Of men, we feare the people: for all men counted Iohn, that he was a Prophet in deede.
In kuwa muka ce, “amma in muka ce ta mutum ce zasu jejjefemu domi suna jin tsoron jama'a, don duk kowa ya tabbata, cewa Yahaya annabi ne.
33 Then they answered, and saide vnto Iesus, We cannot tell. And Iesus answered, and said vnto them, Neither will I tell you by what authoritie I doe these things.
Sai suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba” Yesu ya ce masu, “Haka ni kuma ba zan fada muku ko da wanne iko nake yin abubuwan nan ba.”

< Mark 11 >