< Luke 6 >
1 And it came to passe on a second solemne Sabbath, that hee went through the corne fieldes, and his disciples plucked the eares of corne, and did eate, and rub them in their hands.
A wata ranar Asabbaci, Yesu yana bi ta gonakin hatsi, sai almajiran suka fara kakkarya kan hatsi suna murjewa a hannuwansu suna ci.
2 And certaine of the Pharises sayde vnto them, Why doe ye that which is not lawfull to doe on the Sabbath dayes?
Sai waɗansu Farisiyawa suka ce, “Me ya sa kuke yin abin da doka ta hana yi a ranar Asabbaci?”
3 Then Iesus answered them, and said, Haue ye not read this, that Dauid did when he himselfe was an hungred, and they which were with him,
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi, sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa ba?
4 Howe he went into the house of God, and tooke, and ate the shewbread, and gaue also to them which were with him, which was not lawful to eate, but for the Priests onely?
Ya shiga gidan Allah, ya ɗauki keɓaɓɓen burodi, sa’an nan ya ci abin da firistoci kaɗai sukan ci bisa ga doka. Ya kuma ba wa abokan tafiyarsa?”
5 And he sayd vnto them, The Sonne of man is Lord also of the Sabbath day.
Sai Yesu ya ce musu, “Ai, Ɗan Mutum ne Ubangijin Asabbaci.”
6 It came to passe also on another Sabbath, that hee entred into the Synagogue, and taught, and there was a man, whose right hand was dryed vp.
A wata ranar Asabbaci kuma, Yesu ya shiga majami’a yana koyarwa. To, a nan kuwa akwai wani mutumin da hannun damansa ya shanye.
7 And the Scribes and Pharises watched him, whether he would heale on the Sabbath day, that they might finde an accusation against him.
Farisiyawa da malaman dokoki suka zuba wa Yesu ido, su ga ko zai warkar a ranar Asabbaci, don su sami dalilin zarginsa.
8 But he knew their thoughts, and sayd to the man which had the withered hand, Arise, and stand vp in the middes. And hee arose, and stoode vp.
Amma Yesu ya san abin da suke tunani. Sai ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.” Sai ya tashi ya tsaya.
9 Then sayd Iesus vnto them, I will aske you a question, Whether is it lawfull on the Sabbath dayes to doe good, or to doe euill? to saue life, or to destroy?
Yesu ya ce musu, “Ina tambayarku, me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a hallaka shi?”
10 And he behelde them all in compasse, and sayd vnto the man, Stretch forth thine hand. And he did so, and his hand was restored againe, as whole as the other.
Sai ya kalle su duka, sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙe, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
11 Then they were filled full of madnes, and communed one with another, what they might doe to Iesus.
Amma Farisiyawa da malaman Doka suka fusata, suka fara tattauna da junansu a kan abin da za su yi wa Yesu.
12 And it came to passe in those dayes, that he went into a mountaine to praye, and spent the night in prayer to God.
Wata rana, a cikin kwanakin nan, Yesu ya je wani dutse domin yă yi addu’a, ya kuma kwana yana addu’a ga Allah.
13 And when it was day, he called his disciples, and of them he chose twelue which also he called Apostles.
Da gari ya waye, sai ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya zaɓi guda goma sha biyu daga cikinsu, waɗanda ya kira su, Manzanni.
14 (Simon whome he named also Peter, and Andrew his brother, Iames and Iohn, Philippe and Bartlemewe:
Siman (wanda ya kira Bitrus), ɗan’uwansa Andarawus, Yaƙub, Yohanna, Filibus, Bartolomeyu,
15 Matthewe and Thomas: Iames the sonne of Alpheus, and Simon called Zelous,
Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Siman wanda ake kira Zilot,
16 Iudas Iames brother, and Iudas Iscariot, which also was the traitour.)
Yahuda ɗan Yaƙub, da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
17 Then he came downe with them, and stood in a plaine place, with the company of his disciples, and a great multitude of people out of all Iudea, and Hierusalem, and from the sea coast of Tyrus and Sidon, which came to heare him, and to be healed of their diseases:
Sai ya sauko tare da su, ya tsaya a wani fili. A can, akwai taro mai yawa na almajiransa, da kuma mutane masu yawan gaske daga ko’ina a Yahudiya, Urushalima da kuma Taya da Sidon da suke bakin teku,
18 And they that were vexed with foule spirits, and they were healed.
waɗanda suka zo domin su ji shi, a kuma warkar da cututtukansu. Waɗanda suke fama da mugayen ruhohi kuwa aka warkar da su.
19 And the whole multitude sought to touch him: for there went vertue out of him, and healed them all.
Kuma dukan mutane suka yi ƙoƙari su taɓa shi, domin iko yana fitowa daga gare shi, ya kuwa warkar da su duka.
20 And hee lifted vp his eyes vpon his disciples, and sayd, Blessed be ye poore: for yours is the kingdome of God.
Da ya dubi almajiransa, sai ya ce, “Masu albarka ne ku da kuke matalauta, gama mulkin Allah naku ne.
21 Blessed are ye that hunger nowe: for ye shalbe satisfied: blessed are ye that weepe now: for ye shall laugh.
Masu albarka ne ku da kuke jin yunwa yanzu, gama za ku ƙoshi. Masu albarka ne ku da kuke kuka yanzu, gama za ku yi dariya.
22 Blessed are ye when men hate you, and when they separate you, and reuile you, and put out your name as euill, for the Sonne of mans sake.
Masu albarka ne sa’ad da mutane suka ƙi ku, suka ware ku, suka zage ku, suna ce da ku mugaye, saboda Ɗan Mutum.
23 Reioyce ye in that day, and be glad: for beholde, your reward is great in heauen: for after this maner their fathers did to the Prophets.
“Ku yi farin ciki a wannan rana, ku kuma yi tsalle don murna, saboda ladarku yana da yawa a sama. Gama haka kakanninsu suka yi wa annabawa.
24 But wo be to you that are rich: for ye haue receiued your consolation.
“Amma kaitonku da kuke da arziki, gama kun riga kun sami ta’aziyyarku.
25 Wo be to you that are full: for ye shall hunger. Wo be to you that now laugh: for ye shall wayle and weepe.
Kaitonku da kuke ƙosassu yanzu, gama za ku zauna da yunwa. Kaitonku da kuke dariya yanzu, gama za ku yi makoki da kuka.
26 Wo be to you when all men speake well of you: for so did their fathers to the false prophets.
Kaitonku sa’ad da dukan mutane suna magana mai kyau a kanku, gama haka kakanninsu suka yi da annabawan ƙarya.
27 But I say vnto you which heare, Loue your enemies: doe well to them which hate you.
“Amma ina faɗa muku, ku da kuke ji na, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku yi wa masu ƙinku alheri.
28 Blesse them that curse you, and pray for them which hurt you.
Ku albarkaci waɗanda suke la’anta ku, ku kuma yi wa waɗanda suke wulaƙanta ku addu’a.
29 And vnto him that smiteth thee on ye one cheeke, offer also the other: and him that taketh away thy cloke, forbid not to take thy coate also.
In wani ya mare ka a wannan kumatu, juya masa ɗayan ma, in wani ya ƙwace maka babban riga, kada ma ka hana masa’yar cikin ma.
30 Giue to euery man that asketh of thee: and of him that taketh away the things that be thine, aske them not againe.
Duk wanda ya roƙe ka abu, ka ba shi. In kuma wani ya yi maka ƙwace, kada ka nema yă mayar maka.
31 And as ye would that men should doe to you, so doe ye to them likewise.
Ka yi wa waɗansu abin da kai kake so su yi maka.
32 For if yee loue them which loue you, what thanke shall ye haue? for euen the sinners loue those that loue them.
“In kana ƙaunar masu ƙaunarka ne kawai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma suna ƙaunar waɗanda suke ƙaunarsu.
33 And if ye do good for them which do good for you, what thanke shall ye haue? for euen the sinners doe the same.
In kuma kana yin alheri ga masu yi maka ne kaɗai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma suna yin haka.
34 And if ye lend to them of whom ye hope to receiue, what thanke shall yee haue? for euen the sinners lend to sinners, to receiue the like.
In kana ba da bashi ga mutanen da za su iya biyan ka ne kawai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma, suna ba da bashi ga masu zunubi, da fata za a biya su tsab.
35 Wherefore loue ye your enemies, and doe good, and lend, looking for nothing againe, and your rewarde shalbe great, and ye shalbe the children of the most High: for he is kinde vnto the vnkinde, and to the euill.
Amma, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku kuma yi musu alheri, ku ba su bashi, ba da sa zuciya sai an biya ku ba. Ta yin haka ne kawai, za ku sami lada mai yawa, ku kuma zama’ya’yan Mafi Ɗaukaka, gama shi mai alheri ne ga marasa godiya da mugaye.
36 Be ye therefore mercifull, as your Father also is mercifull.
Ku zama masu jinƙai, kamar yadda Ubanku mai jinƙai ne.
37 Iudge not, and ye shall not be iudged: condemne not, and ye shall not bee condemned: forgiue, and ye shalbe forgiuen.
“Kada ku ɗora wa wani, ku ma ba za a ɗora muku ba. Kada ku yanke wa wani hukunci, ku ma ba za a yanke muku ba. Ku gafarta, ku ma za a gafarta muku.
38 Giue, and it shalbe giuen vnto you: a good measure, pressed downe, shaken together and running ouer shall men giue into your bosome: for with what measure ye mete, with the same shall men mete to you againe.
Ku bayar, ku ma sai a ba ku mudu a cike, a danƙare, har yă yi tozo, yana zuba, za a juye muku a hannun riga. Mudun da kuka auna da shi, da shi za a auna muku.”
39 And he spake a parable vnto them, Can the blinde leade the blinde? shall they not both fall into the ditche?
Ya kuma faɗa musu wannan misali cewa, “Makaho yana iya jagoran makaho ne? Ba sai dukansu biyu su fāɗa a rami ba?
40 The disciple is not aboue his master: but whosoeuer will be a perfect disciple, shall bee as his master.
Ɗalibi bai fi malaminsa ba, sai dai kowane ɗalibi wanda ya sami cikakkiyar koyarwa, zai zama kamar malaminsa.
41 And why seest thou a mote in thy brothers eye, and considerest not the beame that is in thine owne eye?
“Don me kake duban ɗan tsinke da yake idon ɗan’uwanka, amma ba ka kula da gungumen da yake a naka ido ba?
42 Either howe canst thou say to thy brother, Brother, let me pull out the mote that is in thine eye, when thou seest not the beame that is in thine owne eye? Hypocrite, cast out the beame out of thine owne eye first, and then shalt thou see, perfectly to pull out the mote that is in thy brothers eye.
Yaya za ka ce wa ɗan’uwanka, ‘Ɗan’uwa, bari in cire maka ɗan tsinke da yake idonka,’ alhali kuwa, kai kanka ka kāsa ganin gungumen da yake a naka ido? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen daga idonka, sa’an nan za ka iya gani sosai, ka kuma cire ɗan tsinken da yake a idon ɗan’uwanka.”
43 For it is not a good tree that bringeth foorth euill fruite: neither an euill tree, that bringeth foorth good fruite.
“Ba itace mai kyau da yake ba da munanan’ya’ya. Mummunan itace kuma ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
44 For euery tree is knowen by his owne fruite: for neither of thornes gather men figges, nor of bushes gather they grapes.
Kowane itace da irin’ya’yansa ne ake saninsa. Mutane ba sa tsinke’ya’yan ɓaure daga ƙaya, ko kuwa’ya’yan inabi daga sarƙaƙƙiya.
45 A good man out of the good treasure of his heart bringeth foorth good, and an euill man out of the euill treasure of his heart bringeth foorth euill: for of the aboundance of the heart his mouth speaketh.
Mutumin nagari yakan nuna abubuwa nagari daga cikin nagarta da yake a ɓoye a zuciyarsa, mugun mutum kuwa yakan nuna mugayen abubuwa daga muguntar da take a ɓoye a zuciyarsa. Gama baki yakan faɗa abin da ya cika zuciya ne.”
46 But why call ye me Lord, Lord, and do not the things that I speake?
“Don me kuke ce da ni, ‘Ubangiji, Ubangiji,’ amma ba kwa yin abin da na faɗa?
47 Whosoeuer commeth to mee, and heareth my wordes, and doeth the same, I will shewe you to whome he is like:
Zan nuna muku kwatancin mutumin da yakan zo wurina, yă ji kalmomina, yă kuma aikata.
48 He is like a man which built an house, and digged deepe, and layde the fundation on a rocke: and when the waters arose, the flood beat vpon that house, and coulde not shake it: for it was grounded vpon a rocke.
Yana kama da mutumin da ya gina gida, wanda ya haƙa ƙasa da zurfi, sa’an nan ya kafa tushen ginin a kan dutse. Da ambaliyar ruwa ta taso, ƙarfin ruwa kuwa ya buga gidan, wannan bai jijjiga shi ba, domin an yi masa tushen gini na ainihi.
49 But hee that heareth and doeth not, is like a man that built an house vpon the earth without foundation, against which the flood did beate, and it fell by and by: and the fall of that house was great.
Amma wanda yakan ji kalmomina, ba ya kuma aikata su, yana kama da mutumin da ya gina gida a ƙasa, ba tare da ya kafa tushen gini ba. A sa’ad da ƙarfin ruwa ya buga gidan, sai gidan yă rushe, mummunar rushewa kuwa.”