< Luke 22 >
1 Now the feast of vnleauened bread drewe neere, which is called the Passeouer.
Yanzu fa, Bikin Burodi Marar Yistin da ake kira Bikin Ƙetarewa ya yi kusa,
2 And the hie Priests and Scribes sought how they might kill him: for they feared the people.
manyan firistoci da malaman dokoki kuma suna neman yadda za su kashe Yesu a ɓoye, don suna tsoron mutane.
3 Then entred Satan into Iudas, who was called Iscariot, and was of the nomber of the twelue.
Shaiɗan kuwa ya shiga Yahuda, wanda ake kira Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun.
4 And he went his way, and communed with the hie Priestes and captaines, how he might betray him to them.
Sai Yahuda ya je ya tattauna da manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, a kan yadda zai ba da Yesu a gare su.
5 So they were glad, and agreed to giue him money.
Suka kuwa yi murna, suka yarda su ba shi kuɗi.
6 And he consented, and sought opportunitie to betraye him vnto them, when the people were away.
Ya ko yarda, ya fara neman zarafin da zai ba da Yesu a gare su, sa’ad da taro ba sa nan tare da shi.
7 Then came the day of vnleauened bread, when the Passeouer must be sacrificed.
Sai ranar Bikin Burodi Marar Yisti ta kewayo, wato, ranar hadayar ɗan ragon kafara na Bikin Ƙetarewa.
8 And he sent Peter and Iohn, saying, Go and prepare vs the Passeouer, that we may eate it.
Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yohanna, ya ce musu, “Ku je ku yi shirye-shiryen Bikin Ƙetarewar da za mu ci.”
9 And they saide to him, Where wilt thou, that we prepare it?
Suka tambaye shi suka ce, “Ina kake so mu je mu yi shirin?”
10 Then he said vnto them, Beholde, when ye be entred into the citie, there shall a man meete you, bearing a pitcher of water: folowe him into the house that he entreth in,
Ya amsa ya ce, “Sa’ad da kuka shiga cikin gari, za ku sadu da wani mutum yana ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi zuwa gidan da zai shiga.
11 And say vnto the good man of the house, The Master saith vnto thee, Where is the lodging where I shall eate my Passeouer with my disciples?
Ku ce wa maigidan, Malam ya aike mu mu ce maka, ‘Ina ɗakin baƙi, inda ni da almajiraina za mu ci abincin Bikin Ƙetarewa?’
12 Then he shall shewe you a great hie chamber trimmed: there make it ready.
Zai nuna muku wani babban ɗakin sama a shirye. Nan za ku yi shirin.”
13 So they went, and found as he had said vnto them, and made readie the Passeouer.
Sai suka tafi, suka kuma iske kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
14 And when the houre was come, hee sate downe, and the twelue Apostles with him.
Da lokaci ya yi, sai Yesu ya zauna tare da manzanninsa don cin abinci.
15 Then he saide vnto them, I haue earnestly desired to eate this Passeouer with you, before I suffer.
Sai ya ce musu, “Na yi marmari ƙwarai don in ci wannan Bikin Ƙetarewa tare da ku, kafin in sha wahala.
16 For I say vnto you, Hencefoorth I will not eate of it any more, vntill it bee fulfilled in the kingdome of God.
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara cinsa ba, sai ya sami cika a mulkin Allah.”
17 And hee tooke the cup, and gaue thankes, and said, Take this, and deuide it among you,
Bayan ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, sai ya ce, “Ku karɓa, ku rarraba wa junanku.
18 For I say vnto you, I will not drinke of the fruite of the vine, vntill the kingdome of God be come.
Ina dai gaya muku, ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai mulkin Allah ya zo.”
19 And he tooke bread, and when he had giuen thankes, he brake it, and gaue to them, saying, This is my body, which is giuen for you: doe this in the remembrance of me.
Sai ya ɗauki burodi ya yi godiya, ya kakkarya ya ba su, da cewa, “Wannan jikina ne, da aka bayar dominku. Ku riƙa yin haka don tunawa da ni.”
20 Likewise also after supper he tooke the cup, saying, This cup is that newe Testament in my blood, which is shed for you.
Haka kuma, bayan abincin, ya ɗauki kwaf ruwan inabi ya ce, “Wannan kwaf ruwan inabi shi ne, na sabon alkawari cikin jinina, da aka zubar dominku.
21 Yet beholde, the hand of him that betrayeth me, is with me at the table.
Amma hannun wanda zai ci amanata, yana cin abincin tare da ni.
22 And truely the Sonne of man goeth as it is appointed: but woe be to that man, by whom he is betrayed.
Ɗan Mutum zai mutu kamar yadda aka ƙaddara, amma kaiton mutumin da zai bashe shi.”
23 Then they began to enquire among themselues which of them it should be, that should do that.
Sai suka fara tambayar junansu, ko wane ne a cikinsu zai yi wannan.
24 And there arose also a strife among them, which of them should seeme to be ye greatest.
Gardama ta tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma.
25 But hee saide vnto them, The Kings of the Gentiles reigne ouer them, and they that beare rule ouer them, are called bountifull.
Yesu ya ce musu, “Sarakunan Al’ummai suna nuna iko a kan mutanensu, kuma waɗanda suke nuna iko a kansu, suna kiran kansu Masu Taimakon mutane.
26 But yee shall not be so: but let the greatest among you be as the least: and the chiefest as he that serueth.
Amma ku, kada ku zama haka. A maimakon haka, sai dai wanda ya fi girma a cikinku, ya zama kamar wanda ya fi ƙanƙanta, wanda kuma ke mulki, ya zama kamar mai hidima.
27 For who is greater, he that sitteth at table, or he that serueth? Is not he that sitteth at table? And I am among you as he that serueth.
Wane ne ya fi girma? Wanda yake zaune a tebur ne, ko kuma shi da yake yin hidima? Ashe, ba wanda yake zaune a tebur ba ne? Amma ga ni, ni mai yin hidima ne a cikinku.
28 And yee are they which haue continued with me in my tentations.
Ku ne kuka tsaya tare da ni a gwaje-gwajen da na sha.
29 Therefore I appoint vnto you a kingdome, as my Father hath appointed vnto me,
Daidai kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka ni ma nake ba ku.
30 That ye may eate, and drinke at my table in my kingdome, and sit on seates, and iudge the twelue tribes of Israel.
Saboda ku ci, ku sha a teburina a cikin mulkina. Kuma ku zauna a kan gadon sarauta, ku yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
31 And the Lord saide, Simon, Simon, beholde, Satan hath desired you, to winowe you as wheate.
“Siman, Siman, Shaiɗan ya nemi izini ya sheƙe kakamar alkama.
32 But I haue prayed for thee, that thy faith faile not: therefore when thou art conuerted, strengthen thy brethren.
Amma na yi maka addu’a, Siman, domin kada bangaskiyarka ta kāsa. Bayan ka juyo, ka ƙarfafa’yan’uwanka.”
33 And he said vnto him, Lord, I am ready to goe with thee into prison, and to death.
Amma ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina a shirye in tafi tare da kai har kurkuku, ko mutuwa ma.”
34 But he said, I tell thee, Peter, the cocke shall not crowe this day, before thou hast thrise denied that thou knewest me.
Yesu ya ce, “Ina gaya maka Bitrus, kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
35 And he saide vnto them, When I sent you without bagge, and scrip, and shooes, lacked ye any thing? And they said, Nothing.
Sai Yesu ya tambaye, su ya ce, “Lokacin da na aike ku ba tare da jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma ba, kun rasa wani abu?” Suka amsa, “Babu.”
36 Then he said to them, But nowe he that hath a bagge, let him take it, and likewise a scrip: and hee that hath none, let him sell his coate, and buy a sworde.
Ya ce musu, “Amma yanzu, in kuna da jakar kuɗi, ko jaka, ku ɗauka. In kuma ba ku da takobi, ku sayar da rigarku, ku saya.
37 For I say vnto you, That yet the same which is written, must be perfourmed in me, Euen with the wicked was he nombred: for doubtlesse those things which are written of me, haue an ende.
A rubuce yake cewa, ‘An lissafta shi tare da masu zunubi.’ Ina kuwa gaya muku, dole wannan ya cika a kaina. I, abin da aka rubuta a kaina yana kusan cikawa.”
38 And they said, Lord, beholde, here are two swordes. And he said vnto them, It is ynough.
Almajiran suka ce, “Duba Ubangiji, ga takuba biyu.” Yesu ya ce, “Ya isa.”
39 And he came out, and went (as he was wont) to the mount of Oliues: and his disciples also followed him.
Yesu ya fita zuwa Dutsen Zaitun kamar yadda ya saba, almajiransa kuma suka bi shi.
40 And when hee came to the place, hee said to them, Pray, lest ye enter into tentation.
Da ya kai wurin, sai ya ce musu, “Ku yi addu’a don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
41 And he was drawen aside from them about a stones cast, and kneeled downe, and prayed,
Sai ya janye daga wurinsu, misalin nisan jifa, ya durƙusa a ƙasa ya yi addu’a,
42 Saying, Father, if thou wilt, take away this cuppe from mee: neuerthelesse, not my will, but thine be done.
“Uba, in ka yarda, ka ɗauke mini wannan kwaf, amma ba nufina ba, sai dai naka.”
43 And there appeared an Angell vnto him from heauen, comforting him.
Wani mala’ika daga sama ya bayyana gare shi, ya ƙarfafa shi.
44 But being in an agonie, hee prayed more earnestly: and his sweate was like drops of blood, trickling downe to the ground.
Domin tsananin azaba, sai ya ƙara himma cikin addu’a, zuffansa kuma na ɗigowa ƙasa kamar jini.
45 And he rose vp from prayer, and came to his disciples, and found them sleeping for heauinesse.
Da ya tashi daga addu’a, ya koma inda almajiransa suke, sai ya iske su suna barci, daga gajiyar baƙin ciki.
46 And he said vnto them, Why sleepe ye? rise and pray, least ye enter into tentation.
Ya tambaye su, “Don me kuke barci? Ku tashi ku yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
47 And while he yet spake, beholde, a companie, and he that was called Iudas one of the twelue, went before them, and came neere vnto Iesus to kisse him.
Yana cikin magana sai ga taro sun zo. Mutumin nan da ake kira Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun, shi ya bi da su. Sai ya matso kusa da Yesu don yă yi masa sumba.
48 And Iesus saide vnto him, Iudas, betrayest thou the Sonne of man with a kisse?
Amma Yesu ya tambaye shi ya ce, “Yahuda, ashe, da sumba za ka bashe Ɗan Mutum?”
49 Now when they which were about him, saw what would follow, they said vnto him, Lord, shall we smite with sworde?
Da masu bin Yesu suka ga abin da zai faru, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takubanmu ne?”
50 And one of them smote a seruant of the hie Priest, and strooke off his right eare.
Sai ɗayansu ya kai sara ga bawan babban firist, ya sare kunnen damansa.
51 Then Iesus answered, and said, Suffer them thus farre: and he touched his eare, and healed him.
Amma Yesu ya amsa ya ce, “Kada a ƙara yin wannan!” Sai ya taɓa kunnen mutumin da aka sara, ya warkar da shi.
52 Then Iesus said vnto the hie Priests, and captaines of the Temple, and the Elders which were come to him, Bee ye come out as vnto a theefe with swordes and staues?
Sai Yesu ya ce wa manyan firistoci, da ma’aikatan’yan gadin haikali, da dattawa, waɗanda suka zo don su kama shi, “Ina jagoran wani tawaye ne, da za ku zo da takuba da sanduna?
53 When I was dayly with you in the Temple, yee stretched not foorth the handes against mee: but this is your very houre, and the power of darkenesse.
Kullum ina tare da ku a filin haikali, amma ba ku kama ni ba. Amma wannan ne sa’a naku, lokacin da duhu yake mulki.”
54 Then tooke they him, and led him, and brought him to the hie Priestes house. And Peter followed afarre off.
Sai suka kama shi suka kai shi gidan babban firist. Bitrus ya bi su daga nesa.
55 And when they had kindled a fire in the middes of the hall, and were set downe together, Peter also sate downe among them.
Amma da suka hura wuta a tsakiyar harabar gidan, kowa ya zauna, sai Bitrus ya zo ya zauna tare da su.
56 And a certaine mayde behelde him as hee sate by the fire, and hauing well looked on him, said, This man was also with him.
Wata baiwa ta gan shi zaune kusa da wutar. Ta dube shi sosai sa’an nan, ta ce, “Ai, wannan mutum ma yana tare da shi.”
57 But he denied him, saying, Woman, I know him not.
Amma ya yi mūsu ya ce, “Mace, ban san shi ba!”
58 And after a little while, another man sawe him, and saide, Thou art also of them. But Peter said, Man, I am not.
Bayan ɗan lokaci kaɗan, wani dabam ya gan shi ya ce, “Kai ma ɗayansu ne.” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ba na cikinsu!”
59 And about the space of an houre after, a certaine other affirmed, saying. Verely euen this man was with him: for he is also a Galilean.
Bayan kamar sa’a ɗaya, sai wani mutum ya ce, “Ba shakka, mutumin nan ma yana tare da shi, don shi mutumin Galili ne.”
60 And Peter saide, Man, I knowe not what thou sayest. And immediatly while hee yet spake, the cocke crewe.
Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ban ma san abin da kake magana a kai ba!” Yana cikin magana, sai zakara ya yi cara.
61 Then the Lord turned backe, and looked vpon Peter: and Peter remembred the worde of the Lord, how he had said vnto him, Before the cocke crowe, thou shalt denie me thrise.
Ubangiji kuma ya juya ya kafa wa Bitrus ido. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Ubangiji ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
62 And Peter went out, and wept bitterly.
Sai ya fita waje, ya yi kuka mai zafi.
63 And the men that helde Iesus, mocked him, and strooke him.
Mutanen da suke gadin Yesu suka fara masa ba’a da dūka.
64 And when they had blindfolded him, they smote him on the face, and asked him, saying, Prophecie who it is that smote thee.
Suka rufe masa idanu suna tambaya cewa, “Ka yi annabci! Wa ya mare ka?”
65 And many other thinges blasphemously spake they against him.
Suka kuma yi masa waɗansu baƙaƙen maganganu masu yawa.
66 And assoone as it was day, the Elders of the people, and the hie Priests and the Scribes came together, and led him into their councill,
Da gari ya waye, sai majalisar dattawa na mutane, da manyan firistoci, da malaman dokoki, suka taru wuri ɗaya. Sai aka kawo Yesu a gabansu.
67 Saying, Art thou that Christ? tell vs. And he said vnto them, If I tell you, ye wil not beleeue it.
Suka ce, “Ka faɗa mana, ko kai ne Kiristi?” Yesu ya amsa ya ce, “Ko na gaya muku, ba za ku gaskata ni ba,
68 And if also I aske you, you will not answere me, nor let me goe.
in kuma na yi muku tambaya ba za ku iya ba ni amsa ba.
69 Hereafter shall the Sonne of man sit at the right hand of the power of God.
Amma daga yanzu, Ɗan Mutum zai zauna a hannun dama na Allah Mai Iko.”
70 Then sayd they all, Art thou then ye Sonne of God? And he sayd to them, Ye say, that I am.
Sai dukansu suka yi tambaya suka ce, “Wato, kai Ɗan Allah ke nan?” Ya amsa ya ce, “Kun faɗa daidai, ni ne.”
71 Then sayd they, What neede we any further witnes? for we our selues haue heard it of his owne mouth.
Sai suka ce, “Wace shaida kuma muke nema? Ai, mun ji abin da ya ce da bakinsa.”