< Joshua 3 >

1 Then Ioshua rose very earely, and they remoued from Shittim, and came to Iorden, he, and all the children of Israel, and lodged there, before they went ouer.
Kashegari Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Shittim suka nufi Urdun inda suka sauka kafin su haye.
2 And after three dayes the officers went throughout the hoste,
Bayan kwana uku sai shugabannin suka zazzaga sansani, suna
3 And commanded the people, saying, When ye see the Arke of the couenat of the Lord your God, and the Priestes of the Leuites bearing it, ye shall depart from your place, and goe after it.
ba da umarni ga mutane, suna cewa, “Lokacin da kuka ga akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku, da firistoci waɗanda su ne Lawiyawa, suna ɗauke da shi, sai ku tashi daga inda kuke, ku bi shi.
4 Yet there shalbe a space betweene you and it, about two thousande cubites by measure: ye shall not come neere vnto it, that ye may knowe the way, by the which ye shall goe: for ye haue not gone this way in times past.
A ta haka za ku san inda za ku bi, gama ba ku taɓa bin hanyar ba. Sai dai ku ɗan ba da rata wajen yadi ɗari tara tsakaninku da akwatin alkawari, kada ku kusace shi.”
5 (Nowe Ioshua had saide vnto the people, Sanctifie your selues: for to morowe the Lord will doe wonders among you)
Yoshuwa ya ce wa mutane, “Ku tsarkake kanku, gama gobe Ubangiji zai yi abubuwan al’ajabi a cikinku.”
6 Also Ioshua spake vnto the Priestes, saying, Take vp the Arke of the couenant, and goe ouer before the people: so they tooke vp the Arke of the couenant, and went before the people.
Yoshuwa ya ce wa firistoci, “Ku ɗauki akwatin alkawari ku sha gaba.” Sai suka ɗauki akwatin alkawari suka wuce gaban sauran jama’a.
7 Then the Lord saide vnto Ioshua, This day will I begin to magnifie thee in the sight of all Israel, which shall knowe, that as I was with Moses, so will I be with thee.
Ubangiji kuwa ya ce wa Yoshuwa, “Yau, zan fara ɗaukaka ka a gaban Isra’ilawa duka don su sani cewa ina tare da kai kamar yadda na kasance tare da Musa.
8 Thou shalt therefore command the Priests that beare the Arke of the Couenant, saying, When ye are come to the brinke of the waters of Iorden, ye shall stande still in Iorden.
Ka ce wa firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawari, ‘Sa’ad da kuka kai bakin Urdun, ku shiga cikin ruwan ku tsaya.’”
9 Then Ioshua said vnto the children of Israel, Come hither, and heare the wordes of the Lord your God.
Yoshuwa ya ce wa Isra’ilawa, “Ku zo nan ku ji maganar Ubangiji Allahnku.
10 And Ioshua said, Hereby ye shall know that the liuing God is among you, and that he will certainely cast out before you the Canaanites, and the Hittites, and the Hiuites, and the Perizzites, and the Girgashites, and the Amorites, and the Iebusites.
Ta haka ne za ku san cewa Allah mai rai yana tare da ku, kuma ba shakka a gabanku za ku gani zai kore Kan’aniyawa, Hittiyawa, Hiwiyawa, Ferizziyawa, Girgashiyawa, Amoriyawa da Yebusiyawa.
11 Beholde, the Arke of the couenant of the Lord of all the worlde passeth before you into Iorden.
Ku duba, akwatin alkawarin Ubangiji na dukan duniya zai yi gaba cikin Urdun kafin ku.
12 Nowe therefore take from among you twelue men out of the tribes of Israel, out of euery tribe a man.
Yanzu sai ku zaɓi mutum goma sha biyu daga kabilan Isra’ila, ɗaya daga kowace kabila.
13 And assoone as the soles of the feete of the Priestes (that beare the Arke of the Lord God the Lord of all the worlde) shall stay in the waters of Iorden, the waters of Iorden shall be cut off: for the waters that come from aboue, shall stande still vpon an heape.
Kuma da firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji, Ubangiji dukan duniya, sun sa ƙafa cikin ruwan kogin Urdun, ruwan da yake gudu a rafin zai tsaya cik yă taru a wuri ɗaya.”
14 Then when the people were departed from their tentes to goe ouer Iorden, the Priestes bearing the Arke of the Couenant, went before people.
Saboda haka sa’ad da mutanen suka tashi don su ƙetare Urdun, firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawarin suka sha gaba.
15 And as they that bare the Arke came vnto Iorden, and the feete of the Priestes that bare the Arke were dipped in the brinke of the water, (for Iorden vseth to fill all his bankes all the time of haruest)
Da kaka Urdun yakan cika makil da ruwa. Duk da haka da zarar firistoci masu ɗauke da akwatin alkawari suka tsoma ƙafafunsu a gefen ruwa,
16 Then the waters that came downe from aboue, stayed and rose vpon an heape and departed farre from the citie of Adam, that was beside Zaretan: but the waters that came downe towarde the Sea of the wildernes, euen the salt Sea, failed, and were cut off: so the people went right ouer against Iericho.
sai ruwan da yake gangarowa ya tsaya, ya tattaru a wuri ɗaya ya yi tudu daga nan har zuwa wani garin da ake kira Adam kusa da Zaretan, ruwan da yake gangarowa zuwa Tekun Araba (Tekun Gishiri) kuma ya yanke gaba ɗaya. Sai mutane suka ƙetare kusa da Yeriko.
17 But the Priestes that bare the Arke of the couenant of the Lord, stoode drie within Iorden readie prepared, and all the Israelites went ouer dry, vntill all the people were gone cleane ouer through Iorden.
Firistocin kuwa da suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji suka tsaya daram a kan busasshiyar ƙasa a tsakiyar Urdun a lokacin da Isra’ilawa suka ƙetarewa, har sai da dukan mutane suka gama ƙetarewa.

< Joshua 3 >