< Joshua 15 >

1 This then was the lot of the tribe of the children of Iudah by their families: euen to the border of Edom and the wildernesse of Zin, Southward on the Southcoast.
An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
2 And their South border was the salt Sea coast, from the point that looketh Southward.
Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
3 And it went out on the Southside towarde Maaleth-akrabbim, and went along to Zin, and ascended vp on the Southside vnto Kadesh-barnea, and went along to Hezron, and went vp to Adar, and fet a compasse to Karkaa.
zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
4 From thence went it along to Azmon, and reached vnto the riuer of Egypt, and the end of that coast was on the Westside: this shall be your South coast.
Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
5 Also the Eastborder shalbe the salt Sea, vnto the end of Iorden: and the border on the North quarter from the point of the Sea, and from the end of Iorden.
Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
6 And this border goeth vp to Beth-hogla, and goeth along by ye Northside of Beth-arabah: so the border from thence goeth vp to the stone of Bohan the sonne of Reuben.
wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
7 Againe this border goeth vp to Debir from the valley of Achor, and Northwarde, turning toward Gilgal, that lyeth before the going vp to Adummim, which is on the Southside of the riuer: also this border goeth vp to the waters of En-shemesh, and endeth at En-rogel.
Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
8 Then this border goeth vp to the valley of the sonne of Hinnom; on the Southside of the Iebusites: the same is Ierusalem. also this border goeth vp to the top of the mountaine that lyeth before the valley of Hinnom Westward, which is by the end of the valley of ye gyants Northward.
Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
9 So this border compasseth from the top of the mountaine vnto the fountaine of the water of Nephtoah, and goeth out to the cities of mount Ephron: and this border draweth to Baalah, which is Kiriath-iearim.
Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
10 Then this border compasseth from Baalah Westward vnto mount Seir, and goeth along vnto the side of mount Iearim, which is Chesalon on the Northside: so it commeth downe to Bethshemesh, and goeth to Timnah.
Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
11 Also this border goeth out vnto the side of Ekron Northwarde: and this border draweth to Shicron, and goeth along to mount Baalah, and stretcheth vnto Iabneel: and the endes of this coast are to the Sea.
Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
12 And the Westborder is to the great Sea: so this border shalbe the bounds of the children of Iudah round about, according to their families.
Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
13 And vnto Caleb the sonne of Iephunneh did Ioshua giue a part among the children of Iudah, as the Lord commanded him, euen Kiriath-arba of the father of Anak, which is Hebron.
Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
14 And Caleb droue thence three sonnes of Anak, Sheshai, and Ahiman, and Talmai, the sonnes of Anak.
Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
15 And he went vp thence to the inhabitants of Debir: and the name of Debir before time was Kiriath-sepher.
Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
16 Then Caleb sayd, He that smiteth Kiriath-sepher, and taketh it, euen to him wil I giue Achsah my daughter to wife.
Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
17 And Othniel, the sonne of Kenaz, the brother of Caleb tooke it: and he gaue him Achsah his daughter to wife.
Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
18 And as she went in to him, she moued him, to aske of her father a fielde: and she lighted off her asse, and Caleb sayd vnto her, What wilt thou?
Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
19 Then she answered, Giue me a blessing: for thou hast giuen mee the South countrey: giue me also springs of water. And hee gaue her the springs aboue and the springs beneath.
Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
20 This shalbe the inheritance of the tribe of the children of Iudah according to their families.
Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
21 And the vtmost cities of the tribe of the children of Iudah, toward the coastes of Edom Southward were Kabzeel, and Eder, and Iagur,
Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
22 And Kinah, and Dimonah, and Adadah,
Kina, Dimona, Adada,
23 And Kedesh, and Hazor, and Ithnan,
Kedesh, Hazor, Itnan,
24 Ziph, and Telem, and Bealoth,
Zif, Telem, Beyalot,
25 And Hazor, Hadattah, and Kerioth, Hesron (which is Hazor)
Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
26 Amam, and Shema, and Moladah,
Amam, Shema, Molada,
27 And Hazar, Gaddah, and Heshmon, and Beth-palet,
Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
28 And Hasar-shual, and Beersheba, and Biziothiah,
Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
29 Baalah, and Iim, and Azem,
Ba’ala, Iyim, Ezem,
30 And Eltolad, and Chesil, and Hormah,
Eltolad, Kesil, Horma,
31 And Ziklag, and Madmanna, and Sansannah,
Ziklag, Madmanna, Sansanna,
32 And Lebaoth, and Shilhim, and Ain, and Rimmon: all these cities are twentie and nine with their villages.
Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
33 In the lowe countrey were Eshtaol, and Zoreah, and Ashnah,
Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
34 And Zanoah, and En-gannim, Tappuah, and Enam,
Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
35 Iarmuth, and Adullam, Socoh, and Azekah,
Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
36 And Sharaim, and Adithaim, and Gederah, and Gederothaim: fourteene cities with their villages.
Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
37 Zenam, and Hadashah, and Migdal-gad,
Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
38 And Dileam, and Mizpeh, and Ioktheel,
Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
39 Lachish, and Bozkath, and Eglon,
Lakish, Bozkat, Eglon,
40 And Cabbon, and Lahmam, and Kithlish,
Kabbon, Lahman, Kitlish,
41 And Gederoth, Beth-dagon, and Naamah, and Makkedah: sixteene cities with their villages.
Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
42 Lebnah, and Ether, and Ashan,
Libna, Eter, Ashan,
43 And Iipthtah, and Ashnah, and Nezib,
Yefta, Ashna, Nezib,
44 And Keilah, and Aczib, and Mareshah: nine cities with their villages.
Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
45 Ekron with her townes and her villages,
Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
46 From Ekron, euen vnto the Sea, all that lyeth about Ashdod with their villages.
yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
47 Ashdod with her townes and her villages: Azzah with her townes and her villages, vnto the riuer of Egypt, and the great Sea was their coast.
Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
48 And in the mountaines were Shamir, and Iattir, and Socoh,
Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
49 And Dannah, and Kiriath-sannath (which is Debir)
Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
50 And Anab, and Ashtemoth, and Anim,
Anab, Eshtemo, Anim,
51 And Goshen, and Holon, and Giloh: eleuen cities with their villages,
Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
52 Arab, and Dumah, and Eshean,
Arab, Duma, Eshan,
53 And Ianum, and Beth-tappuah, and Aphekah,
Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
54 And Humtah, and Kiriath-arba, (which is Hebron) and Zior: nine cities with their villages.
Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
55 Maon, Carmel, and Ziph, and Iuttah,
Mawon, Karmel, Zif, Yutta
56 And Izreel, and Iokdeam, and Zanoah,
Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
57 Kain, Gibeah, and Timnah: ten cities with their villages.
Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
58 Halhul, Beth-zur, and Gedor,
Halhul, Bet-Zur, Gedor,
59 And Maarah, and Beth-anoth, and Eltekon: sixe cities with their villages.
Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
60 Kiriath-baal, which is Kiriath-iearim, and Rabbah: two cities with their villages.
Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
61 In the wildernes were Beth-arabah, Middin, and Secacah,
Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
62 And Nibshan, and the citie of salt, and Engedi: sixe cities with their villages.
Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
63 Neuerthelesse, the Iebusites that were the inhabitants of Ierusalem, could not the children of Iudah cast out, but the Iebusites dwell with the children of Iudah at Ierusalem vnto this day.
Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.

< Joshua 15 >