< Job 9 >

1 Then Iob answered, and sayd,
Sai Ayuba ya amsa,
2 I knowe verily that it is so: for howe should man compared vnto God, be iustified?
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 If I would dispute with him, hee could not answere him one thing of a thousand.
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 He is wise in heart, and mighty in strength: who hath bene fierce against him and hath prospered?
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
5 He remoueth the mountaines, and they feele not when he ouerthroweth them in his wrath.
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
6 Hee remooueth the earth out of her place, that the pillars thereof doe shake.
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
7 He commandeth the sunne, and it riseth not: hee closeth vp the starres, as vnder a signet.
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
8 Hee himselfe alone spreadeth out the heauens, and walketh vpon the height of the sea.
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
9 He maketh the starres Arcturus, Orion, and Pleiades, and the climates of the South.
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
10 He doeth great things, and vnsearcheable: yea, marueilous things without nomber.
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
11 Lo, when he goeth by me, I see him not: and when he passeth by, I perceiue him not.
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
12 Behold, when he taketh a pray, who can make him to restore it? who shall say vnto him, What doest thou?
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
13 God will not withdrawe his anger, and the most mightie helpes doe stoupe vnder him.
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
14 Howe much lesse shall I answere him? or howe should I finde out my words with him?
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15 For though I were iust, yet could I not answere, but I would make supplication to my Iudge.
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16 If I cry, and he answere me, yet woulde I not beleeue, that he heard my voyce.
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17 For he destroyeth mee with a tempest, and woundeth me without cause.
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18 He wil not suffer me to take my breath, but filleth me with bitternesse.
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19 If we speake of strength, behold, he is strog: if we speake of iudgement, who shall bring me in to pleade?
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20 If I woulde iustifie my selfe, mine owne mouth shall condemne mee: if I would be perfite, he shall iudge me wicked.
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21 Though I were perfite, yet I knowe not my soule: therefore abhorre I my life.
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
22 This is one point: therefore I said, Hee destroyeth the perfite and the wicked.
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
23 If the scourge should suddenly slay, should God laugh at the punishment of the innocent?
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
24 The earth is giuen into the hand of ye wicked: he couereth the faces of the iudges therof: if not, where is he? or who is he?
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
25 My dayes haue bene more swift then a post: they haue fled, and haue seene no good thing.
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
26 They are passed as with the most swift ships, and as the eagle that flyeth to the pray.
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
27 If I say, I wil forget my complaynt, I will cease from my wrath, and comfort mee,
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
28 Then I am afrayd of all my sorowes, knowing that thou wilt not iudge me innocent.
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
29 If I be wicked, why labour I thus in vaine?
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
30 If I wash my selfe with snowe water, and purge mine hands most cleane,
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
31 Yet shalt thou plunge mee in the pit, and mine owne clothes shall make me filthie.
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
32 For he is not a man as I am, that I shoulde answere him, if we come together to iudgement.
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
33 Neyther is there any vmpire that might lay his hand vpon vs both.
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
34 Let him take his rod away from me, and let not his feare astonish me:
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
35 Then will I speake, and feare him not: but because I am not so, I holde me still.
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.

< Job 9 >