< Job 30 >

1 Bvt now they that are yonger then I, mocke me: yea, they whose fathers I haue refused to set with the dogges of my flockes.
“Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
2 For whereto shoulde the strength of their handes haue serued mee, seeing age perished in them?
Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
3 For pouertie and famine they were solitary, fleeing into the wildernes, which is darke, desolate and waste.
Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
4 They cut vp nettels by the bushes, and the iuniper rootes was their meate.
A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
5 They were chased forth from among men: they shouted at them, as at a theefe.
An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
6 Therfore they dwelt in the clefts of riuers, in the holes of the earth and rockes.
An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
7 They roared among the bushes, and vnder the thistles they gathered themselues.
Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
8 They were the children of fooles and the children of villaines, which were more vile then the earth.
Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
9 And now am I their song, and I am their talke.
“Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
10 They abhorre me, and flee farre from mee, and spare not to spit in my face.
Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
11 Because that God hath loosed my corde and humbled mee, they haue loosed the bridle before me.
Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
12 The youth rise vp at my right hand: they haue pusht my feete, and haue trode on me as on the paths of their destruction.
A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
13 They haue destroyed my paths: they tooke pleasure at my calamitie, they had none helpe.
Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
14 They came as a great breach of waters, and vnder this calamitie they come on heapes.
Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
15 Feare is turned vpon mee: and they pursue my soule as the winde, and mine health passeth away as a cloude.
Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
16 Therefore my soule is nowe powred out vpon me, and the dayes of affliction haue taken holde on me.
“Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
17 It pearceth my bones in the night, and my sinewes take no rest.
Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
18 For the great vehemencie is my garment changed, which compasseth me about as the colar of my coate.
A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
19 He hath cast me into the myre, and I am become like ashes and dust.
Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
20 Whe I cry vnto thee, thou doest not heare me, neither regardest me, when I stand vp.
“Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
21 Thou turnest thy selfe cruelly against me, and art enemie vnto mee with the strength of thine hand.
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
22 Thou takest me vp and causest mee to ride vpon the winde, and makest my strength to faile.
Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
23 Surely I knowe that thou wilt bring mee to death, and to the house appoynted for all the liuing.
Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
24 Doubtles none can stretch his hand vnto the graue, though they cry in his destruction.
“Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
25 Did not I weepe with him that was in trouble? was not my soule in heauinesse for the poore?
Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
26 Yet when I looked for good, euill came vnto me: and when I waited for light, there came darkenesse.
Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
27 My bowels did boyle without rest: for the dayes of affliction are come vpon me.
Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
28 I went mourning without sunne: I stood vp in the congregation and cryed.
Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
29 I am a brother to the dragons, and a companion to the ostriches.
Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
30 My skinne is blacke vpon me, and my bones are burnt with heate.
Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
31 Therefore mine harpe is turned to mourning, and mine organs into the voyce of them that weepe.
Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.

< Job 30 >