< Job 29 >

1 So Iob proceeded and continued his parable, saying,
Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2 Oh that I were as in times past, when God preserued me!
“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
3 When his light shined vpon mine head: and when by his light I walked thorowe the darkenesse,
lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
4 As I was in the dayes of my youth: when Gods prouidence was vpon my tabernacle:
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
5 When the almightie was yet with me, and my children round about me.
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
6 When I washed my pathes with butter, and when the rocke powred me out riuers of oyle:
lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
7 When I went out to the gate, euen to the iudgement seat, and when I caused them to prepare my seate in the streete.
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
8 The yong men saw me, and hid themselues, and the aged arose, and stood vp.
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
9 The princes stayed talke, and layde their hand on their mouth.
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
10 The voyce of princes was hidde, and their tongue cleaued to the roofe of their mouth.
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11 And when the eare heard me, it blessed me: and when the eye sawe me, it gaue witnesse to me.
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
12 For I deliuered the poore that cryed, and the fatherlesse, and him that had none to helpe him.
domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
13 The blessing of him that was ready to perish, came vpon me, and I caused the widowes heart to reioyce.
Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
14 I put on iustice, and it couered me: my iudgement was as a robe, and a crowne.
Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
15 I was the eyes to the blinde, and I was the feete to the lame.
Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
16 I was a father vnto the poore, and when I knewe not the cause, I sought it out diligently.
Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
17 I brake also the chawes of the vnrighteous man, and pluckt the praye out of his teeth.
Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
18 Then I sayde, I shall die in my nest, and I shall multiplie my dayes as the sand.
“Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
19 For my roote is spread out by the water, and the dewe shall lye vpon my branche.
Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
20 My glory shall renue towarde me, and my bowe shall be restored in mine hand.
Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
21 Vnto me men gaue eare, and wayted, and helde their tongue at my counsell.
“Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
22 After my wordes they replied not, and my talke dropped vpon them.
Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
23 And they wayted for me, as for the raine, and they opened their mouth as for the latter rayne.
Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
24 If I laughed on them, they beleeued it not: neither did they cause the light of my countenance to fall.
Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
25 I appoynted out their way, and did sit as chiefe, and dwelt as a King in the army, and like him that comforteth the mourners.
Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.

< Job 29 >