< Jeremiah 24 >

1 The Lord shewed me, and beholde, two baskets of figges were set before the Temple of the Lord, after that Nebuchad-nezzar King of Babel had caryed away captiue Ieconiah ye sonne of Iehoiakim King of Iudah, and the princes of Iudah with the workemen, and cunning men of Ierusalem, and had brought them to Babel.
Bayan Nebukadnezzar ya kwashi Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda da fadawa, da masu sana’a da masu zane zanen Yahuda daga Urushalima zuwa Babilon zaman bauta, Ubangiji ya nuna mini kwanduna biyu na’ya’yan ɓaure ajiye a gaban haikalin Ubangiji.
2 One basket had verie good figges, euen like the figges that are first ripe: and the other basket had verie naughtie figges, which could not be eaten, they were so euill.
Kwando guda yana da’ya’yan ɓaure masu kyau sosai, kamar waɗanda suka nuna da wuri; ɗayan kwandon kuma yana da’ya’yan ɓaure marasa kyau, sun yi muni har ba a iya ci.
3 Then saide the Lord vnto mee, What seest thou, Ieremiah? And I said, Figges: ye good figges verie good, and the naughtie verie naughtie, which cannot be eaten, they are so euill.
Sa’an nan Ubangiji ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani, Irmiya?” Na ce, “’Ya’yan ɓaure. Masu kyau ɗin suna da kyau sosai, amma munanan sun yi muni har ba a iya ci.”
4 Againe the worde of the Lord came vnto me, saying,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
5 Thus sayeth the Lord, the God of Israel, Like these good figges, so will I knowe them that are caryed away captiue of Iudah to bee good, whome I haue sent out of this place, into the land of the Caldeans.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar’ya’yan ɓauren nan masu kyau, haka zan kula da mutanen Yahuda waɗanda aka kwaso waɗanda na fisshe su daga wannan wuri zuwa ƙasar Babiloniyawa
6 For I wil set mine eyes vpon them for good, and I will bring them againe to this lande, and I will build them, and not destroy them, and I will plant them, and not roote them out,
Idanuna za su kula da su don kyautatawarsu, zan kuma komo da su wannan ƙasa. Zan gina su ba zan rushe su ba; zan dasa su ba kuwa zan tumɓuke su ba.
7 And I will giue them an heart to knowe me, that I am the Lord, and they shalbe my people, and I wil be their God: for they shall returne vnto mee with their whole heart.
Zan ba su zuciya don su san ni, cewa ni ne Ubangiji. Za su zama mutanena, zan zama Allahnsu, gama za su komo gare ni da dukan zuciyarsu.
8 And as the naughtie figges which can not bee eaten, they are so euill (surely thus saith the Lord) so wil I giue Zedekiah the King of Iudah, and his princes, and the residue of Ierusalem, that remaine in this lande, and them that dwell in the lande of Egypt:
“‘Amma kamar’ya’yan ɓauren nan marasa kyau, waɗanda sun yi muni har ba a iya ci,’ in ji Ubangiji, ‘haka zan yi da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da sauran mutanen da suka tsira a Urushalima, ko suna a wannan ƙasa ko suna zama a Masar.
9 I will euen giue them for a terrible plague to all the kingdomes of the earth, and for a reproche, and for a prouerbe, for a common talke, and for a curse, in all places where I shall cast them.
Zan mai da su abin ƙyama da masifa ga dukan mulkokin duniya, abin zargi da abin karin magana, abin ba’a da abin la’ana a duk inda zan kore su zuwa.
10 And I will sende the sworde, the famine, and the pestilence among them, till they bee consumed out of the land, that I gaue vnto them and to their fathers.
Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu sai an hallaka su sarai daga ƙasar da na ba su da kuma kakanninsu.’”

< Jeremiah 24 >