< James 2 >

1 My brethren, haue not the faith of our glorious Lord Iesus Christ in respect of persons.
Ya ku 'yan'uwana, muddin kuna rike da bangaskiyar ku ga Ubangijinmu Yesu Almasihu, Ubangijin daukaka, kada ku nuna bambanci ga wadansu mutane.
2 For if there come into your company a man with a golde ring, and in goodly apparell, and there come in also a poore man in vile raiment,
Idan wani mutum ya halarci taron ku da zobban zinariya da tufafi masu kyau, wani matalauci kuma ya shigo da tufafi marasa tsabta.
3 And ye haue a respect to him that weareth the gaie clothing; and say vnto him, Sit thou here in a goodly place, and say vnto the poore, Stand thou there, or sit here vnder my footestoole,
Sa'adda kuka kula da mai tufafi masu kyau nan, har kuka ce masa, “Idan ka yarda ka zauna a nan wuri mai kyau,'' mataulacin nan kuwa kuka ce masa, “Kai ka tsaya daga can,” ko kuwa, “Zauna a nan kasa a gaba na,”
4 Are yee not partiall in your selues, and are become iudges of euill thoughts?
Ashe ba kuna zartar da hukunci a tsakanin ku ba ke nan? Ba kun zama alkalai na mungayen tunani kenan ba?
5 Hearken my beloued brethren, hath not God chosen the poore of this worlde, that they should be rich in faith, and heires of the kingdome which he promised to them that loue him?
Ku saurara, ya 'yan'uwana kaunatattu, ashe, Allah bai zabi matalautan duniyar nan su zama mawadata cikin bangaskiya ba, su kuma zama magada a cikin mulkin nan da ya yi wa masu kaunar sa alkawari ba?
6 But ye haue despised the poore. Doe not the riche oppresse you by tyrannie, and doe not they drawe you before the iudgement seates?
Amma, kun wulakanta matalauta! Ashe, ba masu arzikin ne suke matsa maku ba? Ba su ne kuwa suke jan ku zuwa gaban shari'a ba?
7 Doe nor they blaspheme the worthie Name after which yee be named?
Ba kuma sune ke sabon sunan nan mai girma da ake kiran ku da shi ba?
8 But if yee fulfill the royall Lawe according to the Scripture, which saith, Thou shalt loue thy neighbour as thy selfe, yee doe well.
Duk da haka, idan kuka cika muhimmiyar shari'ar da nassi ya ce, “Ka kaunaci makwabcin ka kamar kanka,” to, madalla.
9 But if yee regarde the persons, yee commit sinne, and are rebuked of the Lawe, as transgressours.
Amma in kun nuna bambanci, kun yi zunubi kenan, shari'a ta same ku da laifin keta umarni.
10 For whosoeuer shall keepe the whole Lawe, and yet faileth in one poynt, hee is guiltie of all.
Duk wanda yake kiyaye dukan shari'a, amma ya yi tuntube a hanya daya kadai, ya sabi shari'a gaba daya ke nan.
11 For he that saide, Thou shalt not commit adulterie, saide also, Thou shalt not kill. Nowe though thou doest none adulterie, yet if thou killest, thou art a transgressour of the Lawe.
Domin wanda ya ce, “Kada ka yi zina,” shi ne kuma ya ce, “Kada ka yi kisan kai.” Idan ba ka yi zina ba amma ka yi kisan kai, ai, ka zama mai taka shari'a kenan.
12 So speake ye, and so doe, as they that shall be iudged by the Lawe of libertie.
Saboda haka, ku yi magana ku kuma yi aiki kamar wadanda za a hukunta ta wurin 'yantacciyar shari'a.
13 For there shalbe condemnation merciles to him that sheweth not mercie, and mercie reioyceth against condemnation.
Gama hukunci yana zuwa ba tare da jinkai ba ga wadanda ba su nuna jinkai. Jinkai ya yi nasara a kan hukunci.
14 What auaileth it, my brethren, though a man saith he hath faith, when he hath no workes? can that faith saue him?
Ina amfanin haka, 'yan'uwana, idan wani ya ce yana da bangaskiya, kuma ba shi da ayyuka? Wannan bangaskiyar ba za ta cece shi ba, ko za ta iya?
15 For if a brother or a sister bee naked and destitute of daily foode,
Misali, idan wani dan'uwa ko 'yar'uwa ba su da tufa mai kyau ko suna rashin abincin yini.
16 And one of you say vnto them, Depart in peace: warme your selues, and fil your bellies, notwithstading ye giue them not those things which are needefull to the body, what helpeth it?
Misali, idan waninku kuma ya ce masu, “Ku tafi cikin salama, ku kasance da dumi ku koshi.” Idan baku ba su abubuwan da jiki ke bukata ba, ina amfanin wannnan?
17 Euen so the faith, if it haue no woorkes, is dead in it selfe.
Haka ma, bangaskiya ita kadai, ba tare da aikin da ya nuna ta ba, matacciya ce.
18 But some man might say, Thou hast the faith, and I haue woorkes: shewe me thy faith out of thy woorkes, and I will shewe thee my faith by my woorkes.
To, wani zai ce, “Ai, kai kana da bangaskiya, ni kuwa ina da ayyuka.” Nuna mani bangaskiyar ka ba tare da ayyuka ba, ni kuma in nuna maka bangaskiya ta ta wurin ayyuka na.
19 Thou beleeuest that there is one God: thou doest well: the deuils also beleeue it, and tremble.
Ka gaskanta cewa Allah daya ne; ka yi daidai. Amma ko aljannu ma sun gaskata, kuma suna rawar jiki.
20 But wilt thou vnderstand, O thou vaine man, that the faith which is without workes, is dead?
Kana so ka sani, kai marar azanci, cewa bangaskiya ba tare da ayyuka ba banza ce?
21 Was not Abraham our father iustified through workes, when he offred Isaac his sonne vpon the altar?
Ba an baratar da Ibrahim mahaifinmu ta wurin ayyuka ba, sa'adda ya mika Ishaku dansa a bisa bagadi?
22 Seest thou not that the faith wrought with his workes? and through the workes was the faith made perfect.
Ka gani, ashe, bangaskiyar sa ta yi aiki da ayyukan sa, kuma da cewa ta wurin ayyuka bangaskiyar sa ta ginu sosai.
23 And the Scripture was fulfilled which sayeth, Abraham beleeued God, and it was imputed vnto him for righteousnesse: and hee was called the friende of God.
Nassi kuma ya cika da ya ce, “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lisafta masa ita a matsayin adalci.” Aka kuma kira shi abokin Allah.
24 Ye see then howe that of workes a man is iustified, and not of faith onely.
Kun ga, ta wurin ayyuka ne mutum yake samu baratarwa ba ta wurin bangaskiya kadai ba.
25 Likewise also was not Rahab the harlot iustified through workes, when she had receiued ye messengers, and sent them out another way?
Ta wannan hanyar kuma, ba Rahab karuwar nan ta samu baratarwa ta wurin ayyuka, da ta marabci masu leken asirin nan ta fitar da su ta wata hanya dabam ba?
26 For as the body without ye spirit is dead, euen so the faith without workes is dead.
Kamar yadda jiki idan ba tare da ruhu ba matacce ne, haka kuma, bangaskiya ba tare da ayyuka ba matacciya ce.

< James 2 >