< James 1 >

1 Iames a seruant of God, and of the Lord Iesus Christ, to the twelue Tribes, which are scattered abroade, salutation.
Yaƙub, bawan Allah da kuma na Ubangiji Yesu Kiristi, Zuwa ga kabilan nan goma sha biyu, da suke warwartse a cikin al’ummai. Gaisuwa mai yawa.
2 My brethren, count it exceeding ioy, when ye fall into diuers tentations,
Ku ɗauki wannan da farin ciki mai tsabta,’yan’uwana, duk sa’ad da gwaje-gwaje na kowane iri suka zo muku,
3 Knowing that ye trying of your faith bringeth forth patience,
domin kun san cewa gwajin bangaskiyarku yakan haifi daurewa.
4 And let patience haue her perfect worke, that ye may be perfect and entier, lacking nothing.
Dole daurewa ta kammala aikinta don ku zama balagaggu da kuma cikakku, ba ku kuma rasa kome ba.
5 If any of you lacke wisedome, let him aske of God, which giueth to all men liberally, and reprocheth no man, and it shalbe giuen him.
In waninku ya rasa hikima, ya kamata yă roƙi Allah, mai bayarwa hannu sake ga kowa ba tare da gori ba, za a kuwa ba shi.
6 But let him aske in faith, and wauer not: for hee that wauereth, is like a waue of the sea, tost of the winde, and caried away.
Amma sa’ad da ya roƙa, dole yă gaskata, ba tare da shakka ba, domin shi mai shakka, yana kama da raƙumar ruwan tekun da iska take kori tana kuma ɓuɓɓugowa.
7 Neither let that man thinke that hee shall receiue any thing of the Lord.
Kada irin wannan mutum yă yi tsammani zai sami wani abu daga Ubangiji;
8 A double minded man is vnstable in all his waies.
shi mai zuciya biyu ne, marar tsai da zuciyarsa wuri ɗaya a cikin duk abin da yake yi.
9 Let the brother of lowe degree reioyce in that he is exalted:
Bari ɗan’uwan da yake cikin halin ƙasƙanci yă yi taƙama a matsayinsa na ɗaukaka.
10 Againe hee that is rich, in that hee is made lowe: for as the flower of the grasse, shall he vanish away.
Amma wanda yake mai arziki, ya kamata yă yi taƙama a matsayinsa na ƙasƙanci, gama ba zai daɗe ba kamar furen jeji.
11 For as when the sunne riseth with heate, then the grasse withereth, and his flower falleth away, and the goodly shape of it perisheth: euen so shall the rich man wither away in all his waies.
Gama in rana ta fito ta yi zafi mai tsanani sai ta sa tsiro yă yanƙwane tsiro; furensa yă kakkaɓe, kyansa kuma yă lalace. Haka ma mai arziki zai shuɗe yayinda yake cikin harkarsa.
12 Blessed is ye man, that endureth tentation: for when he is tried, hee shall receiue the crowne of life, which the Lord hath promised to them that loue him.
Mai albarka ne mutumin da yake daurewa cikin gwaji, gama bayan ya yi nasara da gwajin, zai sami rawanin rai wanda Allah ya yi alkawari ga waɗanda suke ƙaunarsa.
13 Let no man say when hee is tempted, I am tempted of God: for God can not bee tempted with euill, neither tempteth he any man.
Sa’ad da aka jarrabci mutum, kada yă ce, “Allah ne yake jarrabtarsa.” Gama ba ya yiwuwa a jarrabci Allah da mugunta, shi kuma ba ya jarrabtar kowa;
14 But euery man is tempted, when hee is drawen away by his owne concupiscence, and is entised.
amma akan jarrabce kowane mutum sa’ad da muguwar sha’awarsa ta janye shi ta kuma rinjaye shi.
15 Then when lust hath conceiued, it bringeth foorth sinne, and sinne when it is finished, bringeth foorth death.
Sa’an nan, bayan da sha’awar ta yi ciki, takan haifi zunubi; zunubi kuwa, sa’ad da ya balaga yakan haifi mutuwa.
16 Erre not, my deare brethren.
Kada a ruɗe ku,’yan’uwana ƙaunatattu.
17 Euery good giuing, and euery perfect gift is from aboue, and commeth downe from the Father of lights, with whome is no variablenes, neither shadow of turning.
Kowane abu mai kyau da kuma kowace cikakkiyar kyauta daga sama suke, sun sauko ne daga wurin Uban haskoki, wanda ba sauyawa ko wata alamar sākewa a gare shi faufau.
18 Of his owne will begate hee vs with the woorde of trueth, that we shoulde be as the first fruites of his creatures.
Ya zaɓa yă haife mu ta wurin kalmar gaskiya, domin mu zama’ya’yan fari na dukan abin da ya halitta.
19 Wherefore my deare brethren, let euery man be swift to heare, slowe to speake, and slowe to wrath.
’Yan’uwana ƙaunatattu, ku lura da wannan. Ya kamata kowa yă kasance mai saurin saurara, ba mai saurin magana ba, ba kuma mai saurin fushi ba,
20 For the wrath of man doeth not accomplish the righteousnesse of God.
gama fushin mutum ba ya kawo rayuwar adalcin da Allah yake so.
21 Wherefore lay apart all filthinesse, and superfluitie of maliciousnesse, and receiue with meekenes the word that is graffed in you, which is able to saue your soules.
Saboda haka, ku rabu da ƙazamin hali da kuma kowace irin mugunta ku kuma yi na’am da maganar da aka shuka a cikinku da tawali’u, wadda za tă iya cetonku.
22 And be ye doers of the word, and not hearers onely, deceiuing your owne selues.
Kada ku zama masu ji kawai, ku ruɗi kanku. A maimakon haka ku zama masu yin abin da ta ce.
23 For if any heare the woorde, and doe it not, he is like vnto a man, that beholdeth his naturall face in a glasse.
Duk wanda yake ji magana ne kawai, bai kuwa aikata abin da ta ce ba, yana kama da mutumin da ya kalli fuskarsa a madubi
24 For when he hath considered himselfe, hee goeth his way, and forgetteth immediately what maner of one he was.
bayan ya kalli kansa, sa’ad da ya tashi daga wurin, nan da nan sai yă manta da kamanninsa.
25 But who so looketh in the perfect Lawe of libertie, and continueth therein, hee not being a forgetful hearer, but a doer of the woorke, shalbe blessed in his deede.
Amma duk mai duba cikakkiyar ƙa’idan nan ta’yanci, ya kuma nace a kanta, ya zama ba mai ji ne kawai yă mance ba, sai dai mai yi ne yă zartar, to wannan shi za a yi wa albarka a cikin abin da yake yi.
26 If any man amog you seeme religious, and refraineth not his tongue, but deceiueth his owne heart, this mans religion is vaine.
In wani ya ɗauki kansa mai addini ne duk da haka bai ƙame harshensa ba, ruɗin kansa yake yi addininsa kuwa banza ne.
27 Pure religion and vndefiled before God, euen the Father, is this, to visite the fatherlesse, and widdowes in their aduersitie, and to keepe himselfe vnspotted of the world.
Addinin da Allah Ubanmu ya yarda da shi a matsayin mai tsabta da kuma marar aibi shi ne, a kula da marayu da gwauraye cikin damuwoyinsu, a kuma kiyaye kai daga lalacin da duniya take sa wa.

< James 1 >