< Isaiah 63 >

1 Who is this that commeth from Edom, with red garments from Bozrah? hee is glorious in his apparel and walketh in his great strength: I speake in righteousnesse, and am mightie to saue.
Wane ne wannan mai zuwa daga Edom, daga Bozra, saye da jajjayen rigunarsa? Wane ne wannan, sanye cikin daraja, tafe cikin girmar ƙarfinsa? “Ni ne, mai magana cikin adalci, mai ikon ceto.”
2 Wherefore is thine apparel red, and thy garments like him that treadeth in ye wine presse?
Me ya sa rigunanka suka yi ja, sai ka ce na wanda yake tattaka’ya’yan inabi?
3 I haue troden the wine presse alone, and of all people there was none with mee: for I will treade them in mine anger, and tread them vnder foote in my wrath, and their blood shalbe sprinkled vpon my garments, and I will staine all my raiment.
“Na tattake’ya’yan inabi ni kaɗai; cikin al’ummai kuma babu wani tare da ni. Na tattake su cikin fushina Na matse su cikin hasalata; jininsu ya fantsamar wa rigunana, na kuma ɓata dukan tufafina.
4 For the day of vengeance is in mine heart, and the yeere of my redeemed is come.
Gama ranar ɗaukan fansa tana a cikin zuciyata, kuma shekarar fansata ta zo.
5 And I looked, and there was none to helpe, and I wondered that there was none to vpholde: therefore mine owne arme helped me, and my wrath it selfe sustained me.
Na duba, amma babu wanda zai taimaka, na yi mamaki cewa ba wanda ya goyi baya; saboda haka hannuna ya yi mini ceto, fushina kuma ya rayar da ni.
6 Therefore I wil tread downe the people in my wrath, and make them drunken in mine indignation, and wil bring downe their strength to the earth.
Na tattake al’ummai cikin fushina; cikin hasalata kuma na sa sun bugu na kuma zub da jininsu a ƙasa.”
7 I wil remember the mercies of the Lord and the prayses of the Lord according vnto all that the Lord hath giuen vs, and for the great goodnesse toward the house of Israel, which hee hath giuen them according to his tender loue, and according to his great mercies.
Zan ba da labarin alherin Ubangiji, ayyukan da suka sa a yabe shi, bisa ga dukan abubuwan da Ubangiji ya yi mana, I, ayyuka masu kyan da ya yi domin gidan Isra’ila, bisa ga jinƙansa da yawan alheransa.
8 For he saide, Surely they are my people, children that wil not lie: so he was their Sauiour.
Ya ce, “Babu shakka su mutanena ne,’ya’ya maza waɗanda ba za su ruɗe ni ba”; ta haka ya zama Mai Cetonsu.
9 In all their troubles he was troubled, and the Angel of his presence saued them: in his loue and in his mercie he redeemed them, and he bare them and caried them alwayes continually.
Cikin dukan damuwarsu shi ma ya damu, mala’ikan da yake gabansa ya cece su. Cikin ƙauna da jinƙai ya fanshe su; ya kuma ɗaga su ya riƙe su dukan kwanakin dā
10 But they rebelled and vexed his holy Spirit: therefore was hee turned to be their enemie and he fought against them.
Duk da haka suka yi tawaye suka ɓata wa Ruhu Mai Tsarki rai. Saboda haka ya juya ya kuma zama abokin gābansu shi kansa kuma ya yaƙe su.
11 Then he remembred the olde time of Moses and his people, saying, Where is hee that brought them vp out of the Sea with the shepheard of his sheepe? where is he that put his holy Spirit within him?
Sa’an nan mutanensa suka tuna kwanakin dā, kwanakin Musa da mutanensa, ina yake shi wanda ya fitar da su ta teku, da makiyayan garkensa? Ina shi yake wanda ya sa Ruhunsa Mai Tsarki a cikinsu,
12 He led them by the right hand of Moses with his owne glorious arme, deuiding the water before them, to make himselfe an euerlasting Name.
wanda ya aika hannu ɗaukakarsa mai iko ya kasance a hannun dama na Musa, wanda ya raba ruwaye a gabansu, don yă sami wa kansa madawwamin suna,
13 Hee led them through the deepe, as an horse in the wildernesse, that they should not stumble,
wanda ya bishe su cikin zurfafa? Kamar doki a fili, ba su yi tuntuɓe ba;
14 As the beast goeth downe into the valley, the Spirite of the Lord gaue them rest: so diddest thou leade thy people, to make thy selfe a glorious Name.
kamar shanun da suke gangarawa zuwa kwari, haka Ruhun Ubangiji ya ba su hutu. Ga yadda ka bishe mutanenka don ka ba wa kanka suna mai ɗaukaka.
15 Looke downe from heauen, and beholde from the dwelling place of thine holines, and of thy glory. Where is thy zeale and thy strength, the multitude of thy mercies, and of thy compassions? they are restrained from me.
Ka duba daga sama ka gani daga kursiyinka da yake bisa, mai tsarki da kuma mai ɗaukaka. Ina kishinka da kuma ikonka? Ka janye juyayi da kuma tausayin da kake yi mana daga gare mu.
16 Doutles thou art our Father: though Abraham be ignorant of vs, and Israel knowe vs not, yet thou, O Lord, art our Father, and our redeemer: thy Name is for euer.
Amma kai Ubanmu ne, ko Ibrahim bai san mu ba Isra’ila kuma bai yarda da mu ba; kai, ya Ubangiji, kai ne Ubanmu, Mai Fansarmu tun fil azal ne sunanka.
17 O Lord, why hast thou made vs to erre from thy wayes? and hardened our heart from thy feare? Returne for thy seruants sake, and for the tribes of thine inheritance.
Don me, ya Ubangiji, ka sa muna barin hanyoyinka muka kuma taurare zukatanmu don kada mu girmama ka? Ka komo domin darajar bayinka, kabilan da suke abin gādonka.
18 The people of thine holinesse haue possessed it, but a litle while: for our aduersaries haue troden downe thy Sanctuarie.
Gama a ɗan lokaci mutanenka suka mallaki wurinka mai tsarki, amma yanzu abokan gābanmu sun tattake wurinka mai tsarki.
19 We haue bene as they, ouer whome thou neuer barest rule, and vpon whom thy Name was not called.
Mu naka tun fil azal; ba ka taɓa yin mulki a kansu ba, ba a taɓa kira su da sunanka ba.

< Isaiah 63 >