< Isaiah 25 >

1 O Lord, thou art my God: I will exalt thee, I will prayse thy Name: for thou hast done wonderfull things, according to the counsels of old, with a stable trueth.
Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka, gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki, abubuwan da aka shirya tun da.
2 For thou hast made of a citie an heape, of a strong citie, a ruine: euen the palace of strangers of a citie, it shall neuer be built.
Ka mai da birnin tsibin tarkace, ka lalatar da gari mai katanga, birnin baƙi mai ƙarfi, ta ɓace; ba za a ƙara gina ta ba.
3 Therefore shall the mightie people giue glory vnto thee: the citie of the strong nations shall feare thee.
Saboda haka mutane masu ƙarfi za su girmama ka; biranen mugayen al’ummai za su ji tsoronka.
4 For thou hast bene a strength vnto the poore, euen a strength to the needie in his trouble, a refuge against the tempest, a shadow against the heate: for the blaste of the mightie is like a storme against the wall.
Kai ka zama mafakar matalauta, mafaka don mabukata cikin damuwa, wurin ɓuya daga hadari, inuwa kuma daga zafin rana. Gama numfashin mugaye yana kamar da hadari mai bugun bango
5 Thou shalt bring downe the noyse of the strangers, as the heate in a drie place: he wil bring downe the song of the mightie, as the heate in the shadowe of a cloude.
kuma kamar zafin hamada. Ka kwantar da hayaniyar baƙi; kamar yadda inuwar girgije kan rage zafin rana, haka ake kwantar da waƙar mugaye.
6 And in this mountaine shall the Lord of hostes make vnto all people a feast of fat thinges, euen a feast of fined wines, and of fat thinges full of marow, of wines fined and purified.
A kan wannan dutse Ubangiji Maɗaukaki zai shirya bikin abinci mai kyau don dukan mutane, liyafar ajiyayyen ruwan inabi da nama mafi kyau da ruwan inabi mafi kyau.
7 And he will destroy in this mountaine the couering that couereth all people, and the vaile that is spread vpon all nations.
A wannan dutse zai kawar da baƙin cikin da ya lulluɓe dukan mutane, ƙyallen da ya rufe dukan al’ummai;
8 He wil destroy death for euer: and the Lord God wil wipe away the teares from all faces, and the rebuke of his people will he take away out of all the earth: for the Lord hath spoken it.
zai haɗiye mutuwa har abada. Ubangiji Mai Iko Duka zai share hawaye daga dukan fuskoki; zai kawar da kunyar mutanensa daga dukan duniya. Ubangiji ne ya faɗa.
9 And in that day shall men say, Loe, this is our God: we haue waited for him, and he wil saue vs. This is the Lord, we haue waited for him: we will reioyce and be ioyfull in his saluation.
A wannan rana za su ce, “Tabbatacce wannan shi ne Allah; mun dogara a gare shi, ya kuma cece mu. Wannan shi ne Ubangiji, mun dogara a gare shi; bari mu yi murna mu kuma yi farin ciki a cikin cetonsa.”
10 For in this mountaine shall the hand of the Lord rest, and Moab shalbe threshed vnder him, euen as strawe is thresshed in Madmenah.
Hannun Ubangiji zai zauna a kan wannan dutse; amma za a tattake Mowab a ƙarƙashinsa kamar yadda ake tattaka kara a cikin taki.
11 And he shall stretche out his hande in the middes of them (as he that swimmeth, stretcheth them out to swimme) and with the strength of his handes shall he bring downe their pride.
Za su buɗe hannuwansa a cikinsa, yadda mai iyo kan buɗe hannuwansa don yă yi iyo. Allah ya ƙasƙantar da girmankansu duk da wayon hannuwansu.
12 The defence also of the height of thy walles shall he bring downe and lay lowe, and cast them to the ground, euen vnto the dust.
Zai rurrushe manyan katangar kagaru ya kuma ƙasƙantar da su; zai rushe su har ƙasa, su zama ƙura.

< Isaiah 25 >