< Isaiah 11 >

1 But there shall come a rodde foorth of the stocke of Ishai, and a grasse shall growe out of his rootes.
Toho zai fito daga kututturen Yesse; daga saiwarsa Reshe zai ba da’ya’ya.
2 And the Spirite of the Lord shall rest vpon him: the Spirite of wisedome and vnderstanding, the Spirite of counsell and strength, the Spirite of knowledge, and of the feare of the Lord,
Ruhun Ubangiji zai kasance a kansa, Ruhun hikima da na fahimta, Ruhun shawara da na iko, Ruhun sani da na tsoron Ubangiji,
3 And shall make him prudent in the feare of the Lord: for he shall not iudge after the sight of his eies, neither reproue by ye hearing of his eares.
zai kuwa ji daɗin tsoron Ubangiji. Ba zai yi hukunci ta wurin abin da ya gani da idanunsa ba, ba zai kuwa yanke shawara ta wurin abin da ya ji da kunnuwansa ba;
4 But with righteousnesse shall he iudge the poore, and with equitie shall he reprooue for the meeke of the earth: and he shall smite the earth with the rod of his mouth, and with the breath of his lippes shall he slay the wicked.
amma da adalci zai yi wa masu bukata shari’a, da gaskiya zai yanke shawarwari saboda matalautan duniya. Kamar sanda zai bugi duniya da maganar bakinsa; da numfashin leɓunansa zai yanke mugaye.
5 And iustice shall be ye girdle of his loynes, and faithfulnesse the girdle of his reines.
Adalci ne zai zama abin ɗamararsa aminci kuma igiyar da zai ɗaura kewaye da gindinsa.
6 The wolfe also shall dwell with the lambe, and the leopard shall lie with the kid, and the calfe, and the lyon, and the fat beast together, and a litle childe shall leade them.
Kyarkeci zai zauna tare da ɗan rago damisa za tă kwanta tare da akuya, ɗan maraƙi da zaki da ɗan saniya za su yi kiwo tare; ɗan yaro ne zai lura da su.
7 And the kow and the beare shall feede: their yong ones shall lie together: and the lyon shall eate strawe like the bullocke.
Saniya da beyar za su yi kiwo tare, ƙananansu za su kwanta tare, zaki kuma zai ci ciyawa kamar saniya.
8 And the sucking childe shall play vpon the hole of the aspe, and the wained childe shall put his hand vpon the cockatrice hole.
Jariri zai yi wasa kurkusa da ramin gamsheƙa, ɗan yaro kuma zai sa hannunsa a ramin maciji mai mugun dafi.
9 Then shall none hurt nor destroy in all the mountaine of mine holines: for the earth shalbe full of the knowledge of the Lord, as the waters that couer the sea.
Ba za su yi lahani ko su hallaka wani a dutsena mai tsarki ba, gama duniya za tă cika da sanin Ubangiji kamar yadda ruwaye suka rufe teku.
10 And in that day the roote of Ishai, which shall stand vp for a signe vnto the people, the nations shall seeke vnto it, and his rest shall be glorious.
A wannan rana Saiwar Yesse zai miƙe kamar tuta don mutanenta; al’ummai za su tattaru wurinsa, wurin hutunsa kuma zai zama mai daraja.
11 And in the same day shall the Lord stretche out his hand againe the second time, to possesse the remnant of his people, (which shalbe left) of Asshur, and of Egypt, and of Pathros, and of Ethiopia, and of Elam, and of Shinear, and of Hamath, and of the yles of the sea.
A wannan rana Ubangiji zai miƙa hannunsa sau na biyu don yă maido da raguwar da ta rage na mutanensa daga Assuriya, daga Masar ta Ƙasa, daga Masar ta Bisa, daga Kush, daga Elam, daga Babiloniya, daga Hamat da kuma daga tsibiran teku.
12 And he shall set vp a signe to the nations, and assemble the dispersed of Israel, and gather the scattered of Iudah from the foure corners of the worlde.
Zai tā da tuta saboda al’ummai yă kuma tattara masu zaman bauta na Isra’ila; zai tattara mutanen Yahuda da suke a warwatse kusurwoyi huɗu na duniya.
13 The hatred also of Ephraim shall depart, and the aduersaries of Iudah shalbe cut off: Ephraim shall not enuie Iudah, neither shall Iudah vexe Ephraim:
Kishin Efraim zai ɓace, za a kuma kau da abokan gāban Yahuda; Efraim ba zai yi kishin Yahuda ba, haka ma Yahuda ba zai yi gāba da Efraim ba.
14 But they shall flee vpon the shoulders of the Philistims toward the West: they shall spoyle them of the East together: Edom and Moab shall be the stretching out of their hands, and the children of Ammon in their obedience.
Tare za su fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi daga yamma; tare za su washe mutane wajen gabas. Za su ɗibiya hannuwa a kan Edom da Mowab, Ammonawa kuma za su yi musu biyayya.
15 The Lord also shall vtterly destroy the tongue of the Egyptians sea, and with his mightie winde shall lift vp his hand ouer the riuer, and shall smite him in his seuen streames, and cause men to walke therein with shooes.
Ubangiji zai busar da bakin tekun Masar; da iska mai zafi zai share hannunsa a bisa Kogin Yuferites Zai rarraba shi yă zama ƙanana rafuffuka bakwai saboda mutane su iya hayewa da ƙafa.
16 And there shalbe a path to the remnant of his people, which are left of Asshur, like as it was vnto Israel in the day that he came vp out of the land of Egypt.
Za a yi babbar hanya saboda raguwa mutanensa da ta rage daga Assuriya, kamar yadda ta kasance wa Isra’ila sa’ad da suka fito daga Masar.

< Isaiah 11 >