< Genesis 7 >

1 And the Lord said vnto Noah, Enter thou and all thine house into the Arke: for thee haue I seene righteous before me in this age.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
2 Of euery cleane beast thou shalt take to thee by seuens, the male and his female: but of vncleane beastes by couples, the male and his female.
Ka ɗauki bakwai na kowace iri tsabtaccen dabba tare da kai, namiji da ta mace, da kuma biyu na kowace dabba marar tsabta, namiji da ta mace,
3 Of the foules also of the heauen by seuens, male and female, to keepe seede aliue vpon the whole earth.
da kuma bakwai na kowane iri tsuntsu, namiji da ta mace, domin a bar kowane irinsu da rai a dukan duniya.
4 For seuen dayes hence I will cause it raine vpon the earth fourtie dayes and fourtie nightes, and all the substance that I haue made, will I destroy from off the earth.
Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arba’in da dare arba’in, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
5 Noah therefore did according vnto all that the Lord commanded him.
Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
6 And Noah was sixe hundreth yeeres olde, when the flood of waters was vpon the earth.
Nuhu yana da shekaru 106 ne sa’ad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
7 So Noah entred and his sonnes, and his wife, and his sonnes wiues with him into the Arke, because of the waters of the flood.
Nuhu da matarsa da’ya’yansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
8 Of the cleane beastes, and of the vncleane beastes, and of the foules, and of all that creepeth vpon the earth,
Biyu-biyu daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da tsuntsaye da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa,
9 There came two and two vnto Noah into the Arke, male and female, as God had commanded Noah.
namiji da ta mace, suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi, kamar yadda Allah ya umarce Nuhu.
10 And so after seuen dayes the waters of the flood were vpon the earth.
Bayan kwana bakwai kuwa ambaliya ruwa ta sauko a bisa duniya.
11 In the sixe hundreth yeere of Noahs life in the second moneth, the seuetenth day of the moneth, in the same day were all the fountaines of the great deepe broken vp, and the windowes of heauen were opened,
A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe.
12 And the raine was vpon the earth fourtie dayes and fourtie nightes.
Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arba’in da dare arba’in.
13 In the selfe same day entred Noah with Shem, and Ham and Iapheth, the sonnes of Noah, and Noahs wife, and the three wiues of his sonnes with them into the Arke.
A wannan rana Nuhu tare da matarsa da’ya’yansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
14 They and euery beast after his kinde, and all cattell after their kinde, and euery thing that creepeth and moueth vpon the earth after his kinde, and euery foule after his kinde, euen euery bird of euery fether.
Tare da su kuwa, akwai kowane naman jeji bisa ga irinsa, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinta, da kowane tsuntsun gida da na jeji bisa ga irinsa, da dukan abu mai fiffike.
15 For they came to Noah into ye Arke, two and two, of all flesh wherein is ye breath of life.
Biyu-biyu na dukan halittu masu numfashi suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi.
16 And they entring in, came male and female of all flesh, as God had commanded him: and the Lord shut him in.
Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
17 Then ye flood was fourtie dayes vpon the earth, and the waters were increased, and bare vp the Arke, which was lift vp aboue the earth.
Kwana arba’in ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, sa’ad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
18 The waters also waxed strong, and were increased exceedingly vpon the earth, and the Arke went vpon the waters.
Ruwa ya taso, ya ƙaru ƙwarai a duniya, jirgin kuma ya yi ta yawo a bisa ruwa.
19 The waters preuailed so exceedingly vpon the earth, that all the high mountaines, that are vnder the whole heauen, were couered.
Ruwa ya ƙaru ƙwarai a duniya, ya kuma rufe dukan duwatsu masu tsawo a ƙarƙashin sammai.
20 Fifteene cubites vpwarde did the waters preuaile, when the mountaines were couered.
Ruwan ya taso ya rufe duwatsu, zurfin ruwa daga duwatsun zuwa inda jirgin yake ya fi ƙafa ashirin.
21 Then all flesh perished that moued vpon the earth, both foule and cattell and beast, and euery thing that creepeth and moueth vpon the earth, and euery man.
Kowane abu mai rai da yake tafiya a duniya ya hallaka, tsuntsaye, dabbobin gida, namun jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe a duniya, da kuma dukan mutane.
22 Euery thing in whose nostrels the spirit of life did breathe, whatsoeuer they were in the drie land, they died.
Kome a busasshiyar ƙasa da yake numfashi a hancinsa ya mutu.
23 So he destroyed euery thing that was vpon the earth, from man to beast, to ye creeping thing, and to the foule of the heauen: they were euen destroyed from the earth. And Noah onely remained; and they that were with him in ye Arke.
Aka kawar da kowane abu mai rai, mutane da dabbobi da halittu masu rarrafe a ƙasa, da tsuntsayen sama a doron ƙasa, duka aka kawar da su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari da waɗanda suke tare da shi a cikin jirgi.
24 And the waters preuailed vpon the earth an hundreth and fiftie dayes.
Ruwa ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.

< Genesis 7 >

The Great Flood
The Great Flood