< Genesis 48 >

1 Againe after this, one sayd to Ioseph, Loe, thy father is sicke: then hee tooke with him his two sonnes, Manasseh and Ephraim.
Bayan wani lokaci aka faɗa wa Yusuf, “Mahaifinka yana ciwo.” Sai ya ɗauki’ya’yansa maza biyu, Manasse da Efraim suka tafi tare da shi.
2 Also one told Iaakob, and said, Behold, thy sonne Ioseph is come to thee, and Israel tooke his strength vnto him and sate vpon the bed.
Sa’ad da aka faɗa wa Yaƙub, “Ɗanka Yusuf ya zo gare ka,” sai Isra’ila ya ƙoƙarta ya tashi ya zauna a kan gado.
3 Then Iaakob sayde vnto Ioseph, God almightie appeared vnto me at Luz in the land of Canaan, and blessed me.
Yaƙub ya ce wa Yusuf, “Allah Maɗaukaki ya bayyana gare ni a Luz a ƙasar Kan’ana, a can ya albarkace ni
4 And he sayde vnto me, Behold, I wil make thee fruitefull, and will multiplie thee, and will make a great number of people of thee, and will giue this lande vnto thy seede after thee for an euerlasting possession.
ya kuma ce mini, ‘Zan sa ka yi ta haihuwa ka kuma riɓaɓɓanya, za ka ƙaru a yawa. Zan mai da kai al’ummar mutane, zan kuma ba ka wannan ƙasa tă zama madawwamiyar mallaka ga zuriyarka a bayanka.’
5 And now thy two sonnes, Manasseh and Ephraim, which are borne vnto thee in the lande of Egypt, before I came to thee into Egypt, shall be mine, as Reuben and Simeon are mine.
“To, yanzu,’ya’ya mazanka biyu da aka haifa maka a Masar kafin in zo a nan za su zama nawa; Efraim da Manasse za su zama nawa, kamar yadda Ruben da Simeyon suke nawa.
6 But the linage, which thou hast begotten after them, shalbe thine: they shall be called after the names of their brethren in their inheritance.
Duk waɗansu’ya’yan da aka haifa maka bayansu za su zama naka; a yankin da suka gāda za a lissafa a ƙarƙashin sunayen’yan’uwansu.
7 Nowe when I came from Padan, Rahel died vpon mine hande in the lande of Canaan, by the way when there was but halfe a dayes iourney of grounde to come to Ephrath: and I buryed her there in the way to Ephrath: the same is Beth-lehem.
Yayinda nake dawowa daga Faddan Aram, cikin baƙin cikina Rahila ta rasu a ƙasar Kan’ana yayinda muke kan hanya,’yar rata daga Efrata. Saboda haka na binne ta a can kusa da hanya zuwa Efrata” (wato, Betlehem).
8 Then Israel beheld Iosephs sonnes and sayd, Whose are these?
Sa’ad da Isra’ila ya ga’ya’yan Yusuf maza, sai ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan?”
9 And Ioseph sayd vnto his father, They are my sonnes, which God hath giuen mee here. Then he sayd, I pray thee, bring them to me, that I may blesse them:
Yusuf ya ce wa mahaifinsa, “Su ne’ya’yan da Allah ya ba ni a nan.” Sa’an nan Isra’ila ya ce, “Kawo mini su saboda in albarkace su.”
10 (For the eyes of Israel were dimme for age, so that hee coulde not well see) Then he caused them to come to him, and he kissed them and embraced them.
Yanzu fa idanun Isra’ila sun fara rasa ƙarfi saboda tsufa, har ba ya iya gani sosai. Saboda haka Yusuf ya kawo’ya’yansa maza kusa da shi, sai mahaifinsa ya sumbace su ya rungume su.
11 And Israel sayde vnto Ioseph, I had not thought to haue seene thy face: yet lo, God hath shewed me also thy seede.
Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Ban yi tsammani zan ga fuskarka kuma ba, yanzu kuwa Allah ya bar ni in ga’ya’yanka su ma.”
12 And Ioseph tooke them away from his knees, and did reuerence downe to the ground.
Sa’an nan Yusuf ya ɗauke su daga gwiwoyin Isra’ila ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
13 Then tooke Ioseph them both, Ephraim in his right hand towarde Israels left hand, and Manasseh in his left hand toward Israels right hand, so he brought them vnto him.
Yusuf ya ɗauke su biyu, Efraim a damansa zuwa hagun Isra’ila, Manasse kuma a hagunsa zuwa hannun daman Isra’ila, ya kuma kawo su kusa da shi.
14 But Israel stretched out his right hand, and layde it on Ephraims head, which was the yonger, and his left hande vpon Manassehs head (directing his handes of purpose) for Manasseh was the elder.
Amma Isra’ila ya miƙa hannun damansa ya sa shi a kan Efraim, ko da yake shi ne ƙaramin, ta wurin harɗewa hannuwansa, ya sa hannun hagunsa a kan Manasse, ko da yake Manasse ne ɗan farinsa.
15 Also he blessed Ioseph and sayde, The God, before whom my fathers Abraham and Izhak did walke, the God, which hath fed me al my life long vnto this day, blesse thee.
Sa’an nan ya albarkaci Yusuf ya ce, “Bari Allah a gaban wanda kakannina Ibrahim da Ishaku suka yi tafiya, Allahn da ya zama makiyayina dukan raina zuwa wannan rana,
16 The Angel, which hath deliuered me from all euill, blesse the children, and let my name be named vpon them, and the name of my fathers Abraham and Izhak, that they may growe as fish into a multitude in the middes of the earth.
Mala’ikan da ya cece ni daga dukan cuta bari yă albarkaci samarin nan. Bari a kira su da sunana da sunayen kakannina Ibrahim da Ishaku bari kuma su ƙaru ƙwarai a bisa duniya.”
17 But when Ioseph sawe that his father layde his right hande vpon the head of Ephraim, it displeased him: and he stayed his fathers hand to remooue it from Ephraims head to Manassehs head.
Sa’ad da Yusuf ya ga mahaifinsa yana sa hannun damansa a kan Efraim bai ji daɗi ba; saboda haka ya ɗauke hannun mahaifinsa ya cire shi daga kan Efraim zuwa kan Manasse.
18 And Ioseph sayde vnto his father, Not so, my father, for this is the eldest: put thy right hand vpon his head.
Yusuf ya ce masa, “A’a, mahaifina, wannan shi ne ɗan farin; ka sa hannunka na dama a kansa.”
19 But his father refused, and sayd, I know well, my sonne, I know well: he shalbe also a people, and he shalbe great likewise: but his yonger brother shalbe greater then he, and his seede shall be full of nations.
Amma mahaifinsa ya ƙi ya ce, “Na sani, ɗana, na sani. Shi ma zai zama mutane, zai kuma zama mai girma. Duk da haka ɗan’uwansa zai zama mai girma fiye da shi, kuma zuriyarsa za tă zama ƙungiyar al’ummai.”
20 So he blessed them that day, and sayde, In thee Israel shall blesse, and say, God make thee as Ephraim and as Manasseh. and he set Ephraim before Manasseh.
Ya albarkace su a wannan rana ya ce, “A cikin sunanku Isra’ila zai sa wannan albarka ‘Bari Allah yă sa ku zama kamar Efraim da Manasse.’” Saboda haka ya sa Efraim gaban Manasse.
21 Then Israel said vnto Ioseph, Behold, I die, and God shall be with you, and bring you againe vnto the land of your fathers.
Sa’an nan Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Ina gab da mutuwa, amma Allah zai kasance tare da ku
22 Moreouer, I haue giuen vnto thee one portion aboue thy brethren, which I gate out of the hand of the Amorite by my sworde and by my bowe.
Kuma gare ka, a matsayi wanda yake kan’yan’uwanka, na ba da gonar da na karɓe daga Amoriyawa da takobi da kuma bakana.”

< Genesis 48 >