< Ezekiel 46 >

1 Thus sayth the Lord God, The gate of the inner court, that turneth toward the East, shall be shut the sixe working dayes: but on the Sabbath it shalbe opened, and in the day of the newe moone it shalbe opened.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a rufe ƙofa ta fili na can cikin da take fuskantar gabas ranaku shida na aiki, amma a ranar Asabbaci da kuma a ranar ganin Sabuwar Wata a buɗe ta.
2 And the prince shall enter by the way of the porch of that gate without, and shall stande by the post of the gate, and the Priests shall make his burnt offring, and his peace offrings, and he shall worship at the threshold of the gate: after, he shall go foorth, but the gate shall not be shut till the euening.
Sarki zai shiga daga waje ta shirayin hanyar shiga yă tsaya a madogarar ƙofa. Firistoci za su miƙa hadayarsa ta ƙonawa da hadayunsa na salama. Zai yi sujada a madogarar ƙofar hanyar shiga sa’an nan ya fita, amma ba za a rufe ƙofar ba sai da yamma.
3 Likewise the people of the lande shall worshippe at the entrie of this gate before the Lord on the Sabbaths, and in the newe moones.
A Asabbatai da kuma a Sabuwar Wata mutanen ƙasar za su yi sujada a gaban Ubangiji a mashigin wannan hanyar shiga.
4 And the burnt offring that the prince shall offer vnto the Lord on the Sabbath day, shalbe sixe lambs without blemish, and a ram without blemish.
Hadaya ta ƙonawar da sarki ya kawo wa Ubangiji a ranar Asabbaci’yan raguna shida ne da rago guda, dukansu marasa lahani.
5 And the meat offring shalbe an Ephah for a ram: and the meate offring for the lambs a gift of his hand, and an Hin of oyle to an Ephah.
Hadayar garin da aka bayar tare da ragon efa guda ne, hadayar garin da’yan ragunan yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
6 And in the day of the newe moone it shall be a yong bullocke without blemish, and sixe lambes and a ram: they shalbe without blemish.
A ranar Sabuwar Wata zai miƙa ɗan bijimi,’yan raguna guda shida da kuma rago guda, dukansu marasa lahani.
7 And he shall prepare a meat offring, euen an Ephah for a bullocke, and an Ephah for a ram, and for the lambes according as his hand shall bring, and an Hin of oyle to an Ephah.
Zai tanada a matsayin hadaya ta gari, efa guda tare da bijimi, efa guda tare da’yan raguna, da kuma’yan raguna yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
8 And when the prince shall enter, hee shall goe in by the way of the porche of that gate, and hee shall go foorth by the way thereof.
Sa’ad da sarki zai shiga, zai shiga ta shirayin hanyar shiga, zai kuma fita ta nan.
9 But when the people of the land shall come before the Lord in the solemne feastes, hee that entreth in by the way of the North gate to worship, shall goe out by the way of the South gate: and he that entreth by the way of the South gate, shall goe foorth by the way of the North gate: hee shall not returne by the way of the gate whereby hee came in, but they shall goe forth ouer against it.
“‘Sa’ad da mutanen ƙasar suka zo gaban Ubangiji a ƙayyadaddun bukukkuwa, duk wanda ya shiga ta ƙofar arewa don yă yi sujada sai ya fita ta ƙofar kudu; kuma duk wanda ya shiga ta ƙofar kudu sai ya fita ta ƙofar arewa. Ba wanda zai koma ta ƙofar da ya shiga, amma kowa zai fita a ƙofar ɗaura da wadda ya shiga.
10 And the prince shall be in the middes of them: hee shall go in when they goe in, and when they goe forth, they shall goe forth together.
Sarki zai kasance a cikinsu, zai shiga sa’ad da suke shiga ya kuma fita sa’ad da suka fita.
11 And in the feastes, and in the solemnities the meat offring shalbe an Ephah to a bullocke, and an Ephah to a ram, and to the lambes, the gift of his hand, and an Hin of oyle to an Ephah.
“‘A bukukkuwa da ƙayyadaddun bukukkuwa, hadaya ta gari zai zama efa tare da bijimi, efa da rago, da kuma’yan raguna da ya ga dama, haɗe da kwalabar mai.
12 Nowe when the prince shall make a free burnt offring or peace offrings freely vnto the Lord, one shall then open him the gate, that turneth towarde the East, and hee shall make his burnt offring and his peace offrings, as he did on the Sabbath day: after, hee shall goe foorth, and when he is gone forth, one shall shut the gate.
Sa’ad da sarki ya ba da hadaya ta yardar rai ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa ce ko hadayun salama ne, sai a buɗe masa ƙofar da take fuskantar gabas. Zai miƙa hadayarsa ta ƙonawa ko hadayarsa ta salama yadda yakan yi a ranar Asabbaci. Sa’an nan ya fita, bayan kuma ya fita, sai a rufe ƙofar.
13 Thou shalt dayly make a burnt offring vnto the Lord of a lambe of one yere without blemish: thou shalt doe it euery morning.
“‘Kullum za ku tanada ɗan rago bana ɗaya marar lahani don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji; kowace safiya za ku tanada shi.
14 And thou shalt prepare a meate offring for it euery morning, the sixt part of an Ephah, and the thirde part of an Hin of oyle, to mingle with the fine flowre: this meate offring shalbe continually by a perpetuall ordinance vnto the Lord.
Tare da shi za ku tanada hadaya ta gari kowace safiya, da ya haɗa da kashi ɗaya bisa shida na efa tare da kashi ɗaya bisa uku na mai ga garin da aka cuɗa. Miƙawar wannan hadaya ta gari ga Ubangiji dawwammamiyar farilla ce.
15 Thus shall they prepare the lambe, and the meate offring and the oyle euery morning, for a continual burnt offring.
Saboda haka za a tanada ɗan rago da hadaya ta gari da kuma mai kowace safiya don hadaya ta ƙonawa ta kullum.
16 Thus saith the Lord God, If the prince giue a gift of his inheritance vnto any of his sonnes, it shalbe his sonnes, and it shall bee their possession by inheritance.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa in sarkin ya ba wa ɗaya daga cikin’ya’yansa kyauta daga gādonsa, zai kuwa zama na zuriyar; zai kuwa zama mallakarsu ta wurin gādo.
17 But if hee giue a gift of his inheritance to one of his seruantes, then it shall bee his to the yere of libertie: after, it shall returne to ye prince, but his inheritance shall remaine to his sonnes for them.
In kuma ya ba wa ɗaya daga cikin bayinsa kyauta daga gadonsa, bawan zai iya riƙe shi sai shekarar’yantarwa; sa’an nan ya mayar wa sarkin. Gādon sarki na’ya’yansa maza ne kaɗai; na su ne.
18 Moreouer the prince shall not take of the peoples inheritance, nor thrust them out of their possession: but he shall cause his sonnes to inherit of his owne possession, that my people be not scattered euery man from his possession.
Kada sarki ya ƙwace gādon mutane, yana korinsu daga mallakarsu. Zai ba wa’ya’yansa maza gādonsu daga cikin mallakarsa, don kada a raba wani daga mutanena da mallakarsa.’”
19 After, he brought me through the entrie, which was at the side of the gate, into the holy chambers of the Priestes, which stoode towarde the North: and beholde, there was a place at the West side of them.
Sa’an nan mutumin ya fitar da ni ta ƙofar shiga a gefen ƙofar zuwa tsarkakakkun ɗakuna waɗanda suke fuskantar arewa, waɗanda suke na firistoci, ya kuma nuna mini wani wuri daga can ƙurewar yamma.
20 Then saide he vnto me, This is the place where the Priestes shall see the the trespasse offering and the sinne offering, where they shall bake the meat offring, that they should not beare them into the vtter court, to sanctifie ye people.
Ya ce mini, “Wannan shi ne wurin da firistoci za su dafa hadaya don laifi, da hadaya don zunubi, a nan ne kuma za su toya hadaya ta gari, domin kada su kai su a filin da yake waje, su tsarkake mutane.”
21 Then he brought me foorth into the vtter court, and caused me to goe by the foure corners of the court: and beholde, in euery corner of the court, there was a court.
Sa’an nan ya kawo ni filin da yake waje ya kuma bi da ni kewaye da kusurwoyi huɗunsa, na kuma ga kowace kusurwa na wani fili.
22 In the foure corners of the court there were courts ioyned of fourty cubits long, and thirty broad: these foure corners were of one measure.
A kusurwoyi huɗu na filin da yake waje akwai waɗansu filaye a haɗe, tsawonsu kamu arba’in fāɗinsu kuwa kamu talatin; kowane fili a kusurwoyi huɗun nan girmansu ɗaya ne.
23 And there went a wall about them, euen about those foure, and kitchins were made vnder the walles rounde about.
Kewaye da cikin kowane filin huɗun nan akwai ginin dutse, da murhu da aka gina a kewaye a ƙarƙashin ginin.
24 Then said he vnto me, This is the kitchin where the ministers of the house shall seethe the sacrifice of the people.
Sai ya ce mini, “Waɗannan su ne ɗakunan dahuwa inda masu hidima a haikali za su dafa hadayun da jama’a.”

< Ezekiel 46 >