< Ezekiel 37 >

1 The hand of the Lord was vpon me, and caryed me out in ye spirit of ye Lord, and set me downe in ye mids of the field, which was full of bones.
Hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma fitar da ni ta wurin Ruhun Ubangiji ya sa ni a tsakiyar kwarin; yana cike da ƙasusuwa.
2 And he led me round about by them, and beholde, they were very many in the open fielde, and lo, they were very drie.
Ya sa na kai na komo a ciki, na kuma ga ƙasusuwa masu girma da yawa a ƙasar kwarin, ƙasusuwan da suka bushe ƙwarai.
3 And he sayde vnto me, Sonne of man, can these bones liue? And I answered, O Lord God, thou knowest.
Sai ya tambaye ni cewa, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa za su iya rayu?” Ni kuwa na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai kaɗai ka sani.”
4 Againe he sayde vnto me, Prophecie vpon these bones and say vnto them, O ye dry bones, heare the word of the Lord.
Sai ya ce mini, “Ka yi wa waɗannan ƙasusuwa annabci ka ce musu, ‘Busassun ƙasusuwa, ku ji maganar Ubangiji!
5 Thus saith the Lord God vnto these bones, Behold, I wil cause breath to enter into you, and ye shall liue.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa waɗannan ƙasusuwa. Zan sa numfashi ya shiga muku, za ku kuwa rayu.
6 And I will lay sinewes vpon you, and make flesh growe vpon you, and couer you with skinne, and put breath in you, that ye may liue, and yee shall know that I am the Lord.
Zan harhaɗa muku jijiyoyi in sa muku tsoka in kuma rufe ku da fata; zan sa numfashi a cikinku, za ku kuwa rayu. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
7 So I prophecied, as I was commanded: and as I prophecied, there was a noyse, and beholde, there was a shaking, and the bones came together, bone to his bone.
Saboda haka sai na yi annabci yadda aka umarce ni. Da nake annabcin, sai aka ji motsi, ƙarar girgiza, sai ƙasusuwan suka harhaɗu, ƙashi ya haɗu da ƙashi.
8 And when I beheld, loe, the sinewes, and the flesh grewe vpon them, and aboue, the skinne couered them, but there was no breath in them.
Na duba, sai ga jijiyoyi da nama suka bayyana a kansu fata kuma ta rufe su, amma ba numfashi a cikinsu.
9 Then sayd he vnto me, Prophecie vnto the winde: prophecie, sonne of man, and say to the winde, Thus sayth the Lord God, Come from the foure windes, O breath, and breathe vpon these slayne, that they may liue.
Sa’an nan ya ce mini, “Ka yi annabci wa numfashi; ka yi annabci, ɗan mutum, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka fito daga kusurwoyi huɗu, ya numfashi, ka kuma numfasa cikin waɗannan matattu, don su rayu.’”
10 So I prophecied as hee had commanded me: and the breath came into them, and they liued, and stood vp vpon their feete, an exceeding great armie.
Saboda haka na yi annabci yadda aka umarce ni, sai numfashi ya shiga musu; suka rayu suka kuma miƙe tsaye a ƙafafunsu babbar runduna ce ƙwarai.
11 Then he sayd vnto me, Sonne of man, these bones are the whole house of Israel. Behold, they say, Our bones are dried, and our hope is gone, and we are cleane cut off.
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa su ne dukan gidan Isra’ila. Suna cewa, ‘Ƙasusuwanmu sun bushe, sa zuciyarmu duk ya tafi; an share mu ƙaf.’
12 Therefore prophecie, and say vnto them, Thus saith the Lord God, Beholde, my people, I will open your graues, and cause you to come vp out of your sepulchres, and bring you into the lande of Israel,
Saboda haka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ya mutanena, zan buɗe kaburburanku in fitar da ku daga cikinsu; zan mai da ku ƙasar Isra’ila.
13 And yee shall knowe that I am the Lord, when I haue opened your graues, O my people, and brought you vp out of your sepulchres,
Sa’an nan ku, mutanena, za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na buɗe kaburburanku na fitar da ku daga cikinsu.
14 And shall put my Spirit in you, and ye shall liue, and I shall place you in your owne land: then yee shall knowe that I the Lord haue spoken it, and performed it, sayth the Lord.
Zan sa Ruhuna a cikinku za ku kuwa rayu, zan kuma zaunar da ku a ƙasarku. Sa’an nan za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata, in ji Ubangiji.’”
15 The word of the Lord came againe vnto me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
16 Moreouer thou sonne of man, take thee a piece of wood, and write vpon it, Vnto Iudah, and to the children of Israel his companions the take another piece of wood, and write vpon it, Vnto Ioseph the tree of Ephraim, and to al the house of Israel his companions.
“Ɗan mutum, ka ɗauki sanda ka rubuta a kansa, ‘Na Yahuda da Isra’ilawan da suke tare da shi.’ Sa’an nan ka ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Sandan Efraim, na Yusuf da dukan gidan Isra’ilan da suke tare da shi.’
17 And thou shalt ioyne the one to another into one tree, and they shalbe as one in thine hand.
Ka haɗa su su zama sanda guda saboda su kasance ɗaya a hannunka.
18 And when the children of thy people shall speake vnto thee, saying, Wilt thou not shewe vs what thou meanest by these?
“In mutanen ƙasarka suka tambaye ka cewa, ‘Ba za ka faɗa mana abin da kake nufi da wannan ba?’
19 Thou shalt answere them, Thus sayeth the Lord God, Behold, I wil take the tree of Ioseph, which is in the hande of Ephraim, and the tribes of Israel his fellowes, and will put them with him, euen with the tree of Iudah, and make them one tree, and they shalbe one in mine hand.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Zan ɗauki sandan Yusuf, wanda yake a hannun Efraim, da na kabilan Isra’ilawan da suke tare da shi, in haɗa shi da sandan Yahuda, in mai da su sanda guda, za su kuwa zama ɗaya a hannuna.’
20 And the pieces of wood, whereon thou writest, shalbe in thine hand, in their sight.
Ka riƙe sandunan da ka yi rubutun a gabansu
21 And say vnto them, Thus saith the Lord God, Beholde, I will take the children of Israel from among the heathen, whither they be gone, and wil gather them on euery side, and bring them into their owne land.
ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan fitar da Isra’ilawa daga al’ummai inda suka tafi. Zan tattara su daga dukan kewaye in komo da su ƙasarsu.
22 And I will make them one people in the lande, vpon the mountaines of Israel, and one king shalbe king to them all: and they shalbe no more two peoples, neither bee deuided any more henceforth into two kingdomes.
Zan mai da su al’umma ɗaya a cikin ƙasar, a kan duwatsun Isra’ila. Za a kasance da sarki guda a kan dukansu ba za su ƙara zama al’ummai biyu ko su rabu su zama masarautai biyu ba.
23 Neither shall they bee polluted any more with their idoles, nor with their abominations, nor with any of their transgressions: but I will saue them out of all their dwelling places, wherein they haue sinned, and will clense them: so shall they be my people, and I will be their God.
Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da mugayen siffofi ko kuma da wani daga laifofinsu ba, gama zan cece su daga dukan zunubinsu na ridda, zan kuma tsarkake su. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu.
24 And Dauid my seruant shalbe king ouer them, and they all shall haue one shepheard: they shall also walke in my iudgements, and obserue my statutes, and doe them.
“‘Bawana Dawuda zai zama sarki a kansu, dukansu kuwa za su kasance da makiyayi guda. Za su bi dokokina su kuma kiyaye ƙa’idodina.
25 And they shall dwell in the lande, that I haue giuen vnto Iaakob my seruant, where your fathers haue dwelt, and they shall dwel therein, euen they, and their sonnes, and their sonnes sonnes for euer, and my seruant Dauid shall bee their prince for euer.
Za su zauna a ƙasar da na ba wa bawana Yaƙub, ƙasar da kakanninsu suka zauna. Su da’ya’yansu da’ya’ya’ya’yansu za su zauna a can har abada, kuma Dawuda bawana zai zama sarkinsu har abada.
26 Moreouer, I will make a couenant of peace with them: it shall be an euerlasting couenant with them, and I wil place them, and multiply them, and wil set my Sanctuarie among them for euermore.
Zan yi alkawarin salama da su; zai zama madawwamin alkawari. Zan kafa su in ƙara yawansu, zan kuma sa wuri mai tsarkina a cikinsu har abada.
27 My tabernacle also shalbe with them: yea, I will be their God, and they shalbe my people.
Mazaunina zai kasance da su; zan kuwa zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
28 Thus the heathen shall knowe, that I the Lord do sanctifie Israel, when my Sanctuarie shall be among them for euermore.
Sa’an nan al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji na mai da Isra’ila mai tsarki, sa’ad da wuri mai tsarkina yana a cikinsu har abada.’”

< Ezekiel 37 >