< Ezekiel 36 >

1 Also thou sonne of man, prophesie vnto the mountaines of Israel, and say, Ye mountaines of Israel, heare the word of the Lord.
“Ɗan mutum, ka yi annabci wa duwatsun Isra’ila ka ce, ‘Ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji.
2 Thus saith the Lord God, because the enemie hath sayde against you, Aha, euen the hye places of the world are ours in possession,
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa abokin gāba yana magana game da ku cewa, “Yauwa! Tsofaffin tuddai sun zama mallakarmu yanzu.”’
3 Therefore prophesie, and say, Thus sayth the Lord God, Because that they haue made you desolate, and swallowed you vp on euery side, that ye might be a possession vnto the residue of the heathen, and ye are come vnto the lippes and tongues of men, and vnto the reproch of the people,
Saboda haka ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin sun lalace ku suka kuma maishe ku kufai marar amfani a kowane gefe saboda ku zama mallakar sauran al’ummai da kuma abin magana da tsegumi ga mutane,
4 Therefore ye mountaines of Israel, heare the worde of the Lord God, Thus sayth the Lord God to the mountaines and to the hilles, to the riuers, and to the valleys, and to the waste, and desolate places, and to the cities that are forsaken: which are spoyled and had in derision of the residue of the heathen that are round about.
saboda haka, ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana faɗa wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, wa kufai da garuruwan da suka zama kango waɗanda aka washe aka wulaƙanta suka zama ganimar sauran al’ummai da suke kewaye da ku,
5 Therefore thus saith the Lord God, Surely in the fire of mine indignation haue I spoken against the residue of the heathen, and against all Idumea, which haue taken my lande for their possession, with the ioy of all their heart, and with despitefull mindes to cast it out for a pray.
ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa cikin kishina mai ƙuna na yi magana gāba da sauran al’ummai, da kuma gāba da Edom, gama da farin ciki da reni a zukatansu suka mai da ƙasata mallakarsu don su washe wuraren kiwonta.’
6 Prophesie therfore vpon the land of Israel, and say vnto the mountaines, and to the hilles, to the riuers, and to the valleys, Thus sayth the Lord God, Behold, I haue spoken in mine indignation, and in my wrath, because yee haue suffered the shame of the heathen,
Saboda haka ka yi annabci game da ƙasar Isra’ila ka kuma ce wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ga shi, na yi magana da kishina da hasalata saboda sun sha zargi wurin al’ummai.
7 Therefore thus saith the Lord God, I haue lifted vp mine hand, surely the heathen that are about you, shall beare their shame.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa na ɗaga hannuna sama na rantse cewa al’ummai da suke kewaye da ku za su sha ba’a.
8 But you, O mountaines of Israel, yee shall shoote forth your branches, and bring foorth your fruite to my people of Israel: for they are ready to come.
“‘Amma ku, ya duwatsun Isra’ila, za ku miƙa rassanku ku ba da amfani ga mutanena Isra’ila, gama ba da daɗewa ba za su komo gida.
9 For behold, I come vnto you, and I wil turne vnto you, and ye shalbe tilled and sowen.
Na damu da ku kuma zan dube ku da tausayi; za ku nome ku kuma shuka,
10 And I wil multiply the men vpon you, euen all the house of Israel wholly, and the cities shalbe inhabited, and the desolate places shalbe builded.
zan kuma riɓaɓɓanya mutane a kanku, dukan gidan Isra’ila ke nan. Za a zauna a birane a kuma sāke gina rusassun wurare.
11 And I wil multiply vpon you man and beast, and they shall encrease, and bring fruite, and I will cause you to dwell after your olde estate, and I will bestowe benefites vpon you more then at the first, and ye shall know that I am the Lord.
Zan sa mutane da dabbobi su yi yawa a kanku, za su kuma ba da’ya’ya su kuma yi yawa. Zan zaunar da mutane a kanku kamar dā zan kuma sa ku wadaita fiye da dā. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
12 Yea, I wil cause men to walke vpon you, euen my people Israel, and they shall possesse you, and ye shalbe their inheritance, and ye shall no more henceforth depriue them of men.
Zan sa mutanena Isra’ila su yi tafiya a kanku. Za su mallake ku, za ku kuma zama gādonsu; ba za ku ƙara sa su rasa’ya’yansu ba.
13 Thus sayth the Lord God, because they say vnto you, Thou land deuourest vp men, and hast bene a waster of thy people,
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin mutane suna magana game da ku cewa, “Kun cinye mutane kuka kuma sa al’ummarku ta rasa’ya’yanta,”
14 Therefore thou shalt deuoure men no more, neither waste thy people henceforth, sayth the Lord God,
saboda haka ba za ku ƙara cinye mutane ko ku sa al’ummarku ta rasa’ya’ya ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Neither will I cause men to heare in thee the shame of the heathen any more, neither shalt thou beare the reproche of the people any more, neither shalt cause thy folke to fal any more, saith the Lord God.
Ba zan ƙara bari ku ji maganar banza ta al’ummai ba, ba kuwa za ku ƙara shan ba’ar mutane ko in sa al’ummarku ta fāɗi ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
16 Moreouer the word of the Lord came vnto me, saying,
Maganar Ubangiji ta sāke zuwa mini cewa,
17 Sonne of man, when the house of Israel dwelt in their owne lande, they defiled it by their owne wayes, and by their deedes: their way was before me as the filthinesse of the menstruous.
“Ɗan mutum, sa’ad da mutanen Isra’ila suke zama a ƙasarsu, sun ƙazantar da ita ta wurin halinsu da kuma ayyukansu. Halinsu ya yi kamar rashin tsarkin mace a lokacin al’adarta a gabana.
18 Wherfore I powred my wrath vpon them, for the blood that they had shed in the land, and for their idoles, wherewith they had polluted it.
Saboda haka na husata da su domin sun yi kisankai a ƙasar kuma domin sun ƙazantar da ita da gumakansu.
19 And I scattered them among the heathen, and they were dispersed through the countries for according to their wayes, and according to their deedes, I iudged them.
Na warwatsa su cikin al’ummai, suka kuwa warwatsu cikin dukan ƙasashe; na hukunta su gwargwadon halinsu da ayyukansu.
20 And when they entred vnto the heathen, whither they went, they polluted mine holy Name, when they sayd of them, These are the people of the Lord, and are gone out of his land.
Kuma ko’ina da suka tafi a cikin al’ummai sun ɓata sunana mai tsarki, gama an yi magana a kansu cewa, ‘Waɗannan mutanen Ubangiji ne, duk da haka dole su bar ƙasarsa.’
21 But I fauoured mine holy Name which the house of Israel had polluted among the heathen, whither they went.
Na damu saboda sunana mai tsarki, wanda gidan Isra’ila ya ɓata a cikin al’ummai inda suka tafi.
22 Therfore say vnto the house of Israel, Thus saith ye Lord God, I doe not this for your sakes, O house of Israel, but for mine holy Names sake, which yee polluted among the heathen whither ye went.
“Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba dominku ba ne, ya gidan Isra’ila da nake yin waɗannan abubuwa, amma saboda sunana ne mai tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al’ummai inda kuka tafi.
23 And I wil sanctifie my great Name, which was polluted among the heathen, among whome you haue polluted it, and the heathen shall know that I am the Lord, sayth the Lord God, when I shalbe sanctified in you before their eyes.
Zan nuna tsarkin girman sunana, wanda aka ɓata a cikin al’umma, sunana da kuka ɓata a cikinsu. Sa’an nan al’ummai za su san cewa ni ne Ubangiji, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinku a idanunsu.
24 For I will take you from among the heathen, and gather you out of all countries, and will bring you into your owne land.
“‘Gama zan fitar da ku daga al’ummai; zan tattara ku daga dukan ƙasashe in komo da ku zuwa ƙasarku.
25 Then wil I powre cleane water vpon you, and ye shalbe cleane: yea, from all your filthines, and from all your idoles wil I clense you.
Zan yayyafa muku ruwa mai tsabta, zan kuwa tsarkake ku daga dukan ƙazantarku daga kuma dukan gumakanku.
26 A newe heart also will I giue you, and a new spirit wil I put within you, and I will take away the stonie heart out of your body, and I will giue you an heart of flesh.
Zan ba ku sabuwa zuciya in kuma sa sabon ruhu a cikinku; zan fid da zuciyar dutse in kuma ba ku zuciyar nama.
27 And I will put my spirite within you, and cause you to walke in my statutes, and ye shall keepe my iudgements and do them.
Zan kuma sa Ruhuna a cikinku in kuma motsa ku ku bi ƙa’idodina ku kuma kiyaye dokokina.
28 And ye shall dwell in the land, that I gaue to your fathers, and ye shalbe my people, and I will be your God.
Za ku zauna a ƙasar da na ba wa kakanninku; za ku zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
29 I will also deliuer you from all your filthinesse, and I will call for corne, and will increase it, and lay no famine vpon you.
Zan cece ku daga dukan rashin tsabtarku. Zan sa hatsi ya yi yalwa ba zan kawo yunwa a kanku ba.
30 For I will multiplie the fruite of the trees, and the increase of the fielde, that ye shall beare no more the reproch of famine among the heathen.
Zan ƙara’ya’yan itatuwa da amfanin gona, saboda kada ku ƙara shan kunya a cikin al’ummai saboda yunwa.
31 Then shall ye remember your owne wicked wayes, and your deedes that were not good, and shall iudge your selues worthie to haue bene destroyed for your iniquities, and for your abominations.
Sa’an nan za ku tuna mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda zunubanku da kuma ayyukanku na banƙyama.
32 Be it knowen vnto you that I do not this for your sakes, sayth the Lord God: therefore, O ye house of Israel, be ashamed, and confounded for your owne wayes.
Ina so ku san cewa ba na yi wannan saboda ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku ji kunya ku kuma giggita saboda halinku, ya gidan Isra’ila!
33 Thus sayth the Lord God, What time as I shall haue clensed you from all your iniquities, I will cause you to dwel in the cities, and the desolate places shalbe builded.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na tsarkake ku daga dukan zunubanku, zan sāke zaunar da ku a garuruwanku, a kuma sāke gina kufai.
34 And the desolate land shalbe tilled, whereas it lay waste in the sight of all that passed by.
Ƙasar da take kango a dā za ku nome ta a maimakon zama kango a idon dukan masu ratsawa a cikinta.
35 For they sayd, This waste land was like the garden of Eden, and these waste and desolate and ruinous cities were strong, and were inhabited.
Za su ce, “Wannan ƙasar da take kango a dā ta zama kamar lambu Eden; biranen da dā suke kufai, kango da kuma aka lalata, yanzu suna da katanga ana kuma zama a ciki.”
36 Then the residue of the heathen that are left round about you, shall know that I the Lord builde the ruinous places, and plant the desolate places: I the Lord haue spoken it, and wil do it.
Sa’an nan al’ummai kewaye da ku da suka rage za su san cewa Ni Ubangiji na sāke gina abin da aka lalace na kuma sāke shuka abin da yake kango. Ni Ubangiji na faɗa, kuma zan aikata.’
37 Thus saith the Lord God, I will yet for this be sought of ye house of Israel, to performe it vnto them: I wil encrease them with men like a flocke.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa har yanzu zan ji roƙon gidan Isra’ila in kuma yi musu wannan. Zan sa mutanensu su yi yawa kamar tumaki,
38 As the holy flocke, as the flocke of Ierusalem in their solemne feastes, so shall the desolate cities be filled with flockes of men, and they shall know, that I am the Lord.
yawansu ya yi kamar garken tumaki don hadaya a Urushalima a ƙayyadaddun lokuta bukukkuwarta. Haka biranen da suke kufai za su cika da ɗumbun mutane. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ezekiel 36 >