< Ezekiel 20 >

1 And in the seuenth yeere, in the fift moneth, the tenth day of the moneth, came certaine of the elders of Israel to enquire of the Lord, and sate before me.
A shekara ta bakwai, a wata na biyar a rana ta goma, waɗansu dattawan Isra’ila suka zo don su nemi nufin Ubangiji, suka kuwa zauna a ƙasa a gabana.
2 Then came the worde of the Lord vnto me, saying,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
3 Sonne of man, speake vnto the Elders of Israel, and say vnto them, Thus saith the Lord God, Are ye come to enquire of me? as I liue, sayth the Lord God, when I am asked, I wil not answer you.
“Ɗan mutum, ka yi magana da dattawan Isra’ila ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kun zo ne ku nemi shawarata? Muddin ina raye, ba zan bari ku nemi shawarata ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
4 Wilt thou iudge them, sonne of man? wilt thou iudge them? cause them to vnderstand the abominations of their fathers,
“Za ka hukunta su? Za ka hukunta su, ɗan mutum? To, sai ka kalubalance su da ayyukan banƙyamar kakanninsu
5 And say vnto them, Thus saith the Lord God, In the day when I chose Israel, and lift vp mine hand vnto the seede of the house of Iaakob, and made my selfe knowen vnto them in the land of Egypt, when I lift vp mine hand vnto them, and sayd, I am the Lord your God,
ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na zaɓi Isra’ila, na ɗaga hannuna, na rantse wa zuriyar gidan Yaƙub na kuma bayyana kaina gare su a Masar da hannun da na ɗaga na ce musu, “Ni ne Ubangiji Allahnku.”
6 In the day that I lift vp mine hand vnto them to bring them forth of the land of Egypt, into a land that I had prouided for them, flowing with milke and hony which is pleasant among all lands,
A ranar na yi musu rantsuwa cewa zan fitar da su daga Masar zuwa ƙasar da na samo musu, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe.
7 Then sayd I vnto them, Let euery man cast away the abominations of his eyes, and defile not your selues with the idols of Egypt: for I am the Lord your God.
Na kuma ce musu, “Kowannenku ya zubar da mugayen siffofin da kuka kafa idanunku a kai, kuma kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
8 But they rebelled against me, and would not heare me: for none cast away the abominations of their eyes, neither did they forsake the idoles of Egypt: then I thought to powre out mine indignation vpon them, and to accomplish my wrath against them in the mids of the land of Egypt.
“‘Amma sai suka yi tawaye a kaina ba su kuwa saurare ni ba; ba su zubar da mugayen siffofin da suka kafa idanunsu a kai ba, balle su ƙi gumakan Masar. Saboda haka zan zubo hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a Masar.
9 But I had respect to my Name, that it should not be polluted before the heathen, among whome they were, and in whose sight I made my selfe knowen vnto them in bringing them forth of the land of Egypt.
Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da suka zauna a ciki da kuma a idanun al’ummai da na bayyana kaina ga Isra’ilawa ta wurin fitar da su daga Masar.
10 Nowe I caried them out of the land of Egypt, and brought them into the wildernes.
Saboda haka na fisshe su daga Masar na kawo su cikin hamada.
11 And I gaue them my statutes, and declared my iudgements vnto them, which if a man doe, he shall liue in them.
Na ba su ƙa’idodina na kuma sanar musu da dokokina, gama mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu.
12 Moreouer I gaue them also my Sabbaths to be a signe betweene me and them, that they might knowe that I am the Lord, that sanctifie them.
Na kuma ba su Asabbataina kamar alama tsakaninmu, domin su san cewa Ni Ubangiji ne yake tsarkake su.
13 But the house of Israel rebelled against me in the wildernes: they walked not in my statutes, and they cast away my iudgements, which if a man doe, he shall liue in them, and my Sabbaths haue they greatly polluted: then I thought to powre out mine indignation vpon them in the wildernes to consume them,
“‘Duk da haka mutanen Isra’ila suka yi mini tawaye a cikin hamada. Ba su bi ƙa’idodina ba amma suka ki dokokina, ko da yake mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu, suka ɓata Asabbataina ƙwarai. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma hallaka su a hamada.
14 But I had respect to my Name, that it shoulde not bee polluted before the heathen in whose sight I brought them out.
Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
15 Yet neuerthelesse, I lift vp mine hande vnto them in the wildernes that I would not bring them into the lande, which I had giuen them, flowing with milke and hony, which was pleasant aboue all landes,
Na kuma ɗaga hannu na rantse musu a hamada cewa ba zan kawo su ƙasar da na ba su ba, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe,
16 Because they cast away my iudgments, and walked not in my statutes, but haue polluted my Sabbaths: for their heart went after their idoles.
domin sun ƙi dokokina ba su kuwa bi ƙa’idodina ba suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Gama zukatansu sun fi so su bauta wa gumakansu.
17 Neuerthelesse, mine eye spared them, that I would not destroye them, neither would I consume them in the wildernes.
Duk da haka na dube su ta tausayi ba zan hallaka su ko in kawo ƙarshensu a hamada ba.
18 But I said vnto their children in the wildernes, Walke ye not in the ordinances of your fathers, neither obserue their maners, nor defile your selues with their idoles.
Na faɗa wa’ya’yansu a hamada, “Kada ku bi farillai kakanninku ko ku kiyaye dokokinsu ko ku ƙazantar da kanku da gumakansu.
19 I am the Lord your God: walke in my statutes, and keepe my iudgements and doe them,
Ni ne Ubangiji Allahnku; ku bi ƙa’idodina ku kuma kula ku kiyaye dokokina.
20 And sanctifie my Sabbaths, and they shall bee a signe betweene mee and you, that ye may knowe that I am the Lord your God.
Ku kiyaye Asabbataina da tsarki, don su zama alama tsakaninmu. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Allahnku.”
21 Notwithstanding the children rebelled against mee: they walked not in my statutes, nor kept my iudgements to doe them, which if a man doe, hee shall liue in them, but they polluted my Sabbaths: then I thought to powre out mine indignation vpon them, and to accomplish my wrath against them in the wildernes.
“‘Amma’ya’yan suka yi mini tawaye. Ba su bi ƙa’idodina ba, ba su kula su kiyaye dokokina ba, ko da yake mutumin da ya kiyaye su zai rayu ta wurinsu, suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a hamada.
22 Neuerthelesse I withdrew mine hand and had respect to my Name that it should not be polluted before the heathen, in whose sight I brought them foorth.
Amma na janye hannuna, kuma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
23 Yet I lift vp mine hande vnto them in the wildernes, that I would scatter them among the heathen, and disperse them through the countreys,
Na kuma ɗaga hannu na rantse musu cewa zan watsar da su cikin al’ummai in kuma warwatsa su cikin ƙasashe,
24 Because they had not executed my iudgements, but had cast away my statutes and had polluted my Sabbaths, and their eyes were after their fathers idoles.
domin ba su kiyaye dokokina ba amma suka ƙi ƙa’idodina suka kuma ƙazantar da Asabbataina, idanunsu suka yi sha’awar gumakan kakanninsu.
25 Wherefore I gaue them also statutes that were not good, and iudgements, wherein they should not liue.
Na kuma ba da su ga farillan da ba su da kyau da dokokin da ba za su rayu ta wurinsu ba;
26 And I polluted them in their owne giftes in that they caused to passe by the fire all that first openeth ye wombe, that I might destroy them, to the ende, that they might know that I am ye Lord.
na bari suka ƙazantu ta wurin kyautai, hadayar kowane ɗan fari don in cika su da abin tsoro domin su san cewa ni ne Ubangiji.’
27 Therefore, sonne of man, speake vnto the house of Israel, and say vnto them, Thus saith the Lord God, Yet in this your fathers haue blasphemed me, though they had before grieuously transgressed against me.
“Saboda haka, ɗan mutum, ka yi magana da mutanen Isra’ila ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a wannan kuma kakanninku suka saɓe ni ta wurin yashe ni.
28 For when I had brought them into the land, for the which I lifted vp mine hand to giue it to them, then they saw euery hie hill, and all the thicke trees, and they offred there their sacrifices, and there they presented their offering of prouocation: there also they made their sweete sauour, and powred out there their drinke offerings.
Sa’ad da na kawo su cikin ƙasar da na rantse zan ba su suka kuma ga tudu mai tsawo ko itace mai ganye, a can suka miƙa hadayunsu, suka yi sadakokin da suka tsokane ni na yi fushi, suka miƙa turaren ƙanshinsu suka kuma zuba sadakokinsu na sha.
29 Then I saide vnto them, What is the hie place whereunto ye goe? And the name thereof was called Bamah vnto this day.
Sai na ce musu, Wane ɗakin tsafi kuke tafiya?’” (Ana ce da shi Bama har wa yau.)
30 Wherefore, say vnto the house of Israel, Thus saith the Lord God, Are ye not polluted after the maner of your fathers? and commit ye not whoredome after their abominations?
“Domin haka ka faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa za ku ƙazantar da kanku yadda kakanninku suka yi ne ku yi sha’awar mugayen siffofinsu?
31 For when you offer your giftes, and make your sonnes to passe through the fire, you pollute your selues with all your idoles vnto this day: shall I answere you when I am asked, O house of Israel? As I liue, saith the Lord God, I wil not answere you when I am asked.
Sa’ad da kuka miƙa kyautai naku, hadayar’ya’yanku maza a wuta, kuna cin gaba da ƙazantar da kanku da duka gumakanku har wa yau. Zan bari ku nemi shawarata, ya gidan Isra’ila? Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba zan bari ku nemi shawarata ba.
32 Neither shall that be done that commeth into your minde: for ye say, We wil be as the heathen, and as the families of the countreys, and serue wood, and stone.
“‘Kukan ce, “Kuna so ku zama kamar sauran al’ummai, kamar sauran mutanen duniya, waɗanda suke bauta wa itace da dutse.” Amma abin da kuke tunani ba zai taɓa faruwa ba.
33 As I liue, saith the Lord God, I will surely rule you with a mightie hand, and with a stretched out arme, and in my wrath powred out,
Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan yi mulki a kanku da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
34 And will bring you from the people, and will gather you out of the countreys, wherein ye are scattered, with a mighty hand, and with a stretched out arme, and in my wrath powred out,
Zan fitar da ku daga al’ummai in tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
35 And I will bring you into the wildernes of the people, and there wil I pleade with you face to face.
Zan kawo ku cikin hamadar al’ummai a can kuwa, fuska da fuska, zan hukunta ku.
36 Like as I pleaded with your fathers in the wildernes of the lande of Egypt, so will I pleade with you, saith the Lord God.
Yadda na hukunta kakanninku a hamadar ƙasar Masar, haka zan hukunta ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
37 And I wil cause you to passe vnder the rod, and wil bring you into the bond of the couenant.
Zan lura da ku yayinda kuke wucewa ƙarƙashin sanda, zan kuma kawo ku cikin daurin alkawari.
38 And I wil chuse out from among you the rebels, and them that transgresse against mee: I will bring them out of the land where they dwel, and they shall not enter into the lande of Israel, and you shall knowe that I am the Lord.
Zan fitar da waɗanda suke mini tayarwa da kuma’yan tawaye. Ko da yake zan fitar da su daga ƙasar da suke zama, duk da haka ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
39 As for you, O house of Israel, thus saith the Lord God, Goe you, and serue euery one his idole, seeing that ye will not obey me, and pollute mine holy Name no more with your giftes and with your idoles.
“‘Game da ku, ya gidan Isra’ila, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tafi ku bauta wa gumakanku, kowannenku! Amma daga baya tabbatacce za ku saurare ni ba kuwa za ku ƙara ɓata sunana mai tsarki da hadayunku da gumakanku ba.
40 For in mine holy mountaine, euen in the hie mountaine of Israel, saith the Lord God, there shall all the house of Israel, and all in the lande, serue me: there will I accept them, and there will I require your offrings and the first fruites of your oblations, with all your holy things.
Gama a kan dutsena mai tsarki, dutse mai tsayi na Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, a can a ƙasar gidan Isra’ila gaba ɗaya za su bauta mini, a can kuwa zan karɓe su. A can zan bukaci hadayunku da sadake sadakenku mafi kyau, tare da dukan tsarkakan hadayunku.
41 I will accept your sweete sauour, when I bring you from the people, and gather you out of the countreys, wherein ye haue bene scattered, that I may be sanctified in you before ye heathen.
Zan karɓe ku kamar turare mai ƙanshi sa’ad da na fitar da ku daga al’ummai na kuma tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, zan kuma nuna kaina mai tsarki a cikinku a idon al’ummai.
42 And ye shall knowe, that I am the Lord, when I shall bring you into the land of Israel, into the land, for the which I lifted vp mine hande to giue it to your fathers.
Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na kawo ku cikin ƙasar Isra’ila, ƙasar da na ɗaga hannu na rantse zan ba wa kakanninku.
43 And there shall ye remember your wayes, and all your workes, wherein ye haue bene defiled, and ye shall iudge your selues worthy to be cut off, for all your euils, that ye haue committed.
A can za ku tuna da halinku da kuma dukan ayyukanku waɗanda kuka ɓata kanku da su, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda mugayen abubuwan da kuka aikata.
44 And ye shall knowe, that I am the Lord, when I haue respect vnto you for my Names sake, and not after your wicked wayes, nor according to your corrupt workes, O ye house of Israel, saith the Lord God.
Za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na yi muku haka saboda sunana ba bisa ga mugayen hanyoyinku da ayyukanku marasa kyau ba, ya gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
45 Moreouer, the worde of the Lord came vnto me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
46 Sonne of man, set thy face toward the way of Teman, and drop thy word toward the South, and prophecie towarde the forest of the fielde of the South,
“Ɗan mutum, ka kafa fuskarka wajen kudu; ka yi wa’azi a kan kudu ka kuma yi annabci a kan kurmin ƙasar kudu.
47 And say to the forest of the South, Heare the worde of the Lord: thus saith the Lord God, Beholde, I will kindle a fire in thee, and it shall deuoure all the greene wood in thee, and all the drie wood: the continuall flame shall not bee quenched, and euery face from the South to the North shall be burnt therein.
Ka faɗa wa kurmin kudanci, ‘Ji maganar Ubangiji. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da sa maka wuta, za tă kuwa cinye dukan itatuwanki sarai, da ɗanye da busasshe. Ba za a kashe wutar da take ci ba, kuma kowace fuska a kudu zuwa arewa za tă ƙone.
48 And all flesh shall see, that I the Lord haue kindled it, and it shall not bee quenched.
Kowa zai san cewa Ni Ubangiji ne ya ƙuna ta; ba za a kashe ta ba.’”
49 Then saide I, Ah Lord God, they say of me, Doeth not he speake parables?
Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Suna zance a kaina cewa, ‘Ba misalai kawai yake yi ba?’”

< Ezekiel 20 >