< Daniel 2 >

1 And in the seconde yeere of the raygne of Nebuchad-nezzar, Nebuchad-nezzar dreamed dreames wherewith his spirite was troubled, and his sleepe was vpon him.
A shekara ta biyu ta mulkinsa, Nebukadnezzar ya yi mafarkai; hankalinsa ya tashi har ya kāsa barci.
2 Then the King commanded to call the inchanters, and the astrologians and the sorcerers, and the Caldeans for to shewe the King his dreames: so they came and stoode before the King.
Sai sarki ya sa aka tattara masa masu sihiri da masu dabo da bokaye da masanan taurari domin su faɗi abin da ya yi mafarki a kai. Da suka shigo suka tsaya a gaban sarki,
3 And the King sayde vnto them, I haue dreamed a dreame, and my spirite was troubled to knowe the dreame.
sai ya ce musu, “Na yi mafarkin da ya dame ni kuma ina so in san me yake nufi.”
4 Then spake the Caldeans to the King in the Aramites language, O King, liue for euer: shewe thy seruants thy dreame, and wee shall shewe the interpretation.
Sai masanan taurarin suka amsa wa sarki da Arameyanci “Ran sarki yă daɗe! Ka faɗa wa bayinka mafarkin, mu kuma sai mu fassara.”
5 And the King answered and sayd to the Caldeans, The thing is gone from me. If ye will not make me vnderstande the dreame with the interpretation thereof, ye shall be drawen in pieces, and your houses shall be made a iakes.
Sai sarki ya amsa wa masanan taurarin ya ce, “Na mance da abin, idan ba ku tuno mini mafarkin, duk da fassararsa ba, to, za a daddatse ku gunduwa-gunduwa, a mai da gidajenku juji.
6 But if yee declare the dreame and the interpretation thereof, ye shall receyue of me gifts and rewardes, and great honour: therefore shewe me the dreame and the interpretation of it.
Amma in har kuka faɗa mini mafarkina kuka kuma bayyana fassararsa, za ku sami lada mai girma. Saboda haka ku faɗa mini mafarkin da kuma fassararsa.”
7 They answered againe, and sayde, Let the King shewe his seruantes the dreame, and wee will declare the interpretation thereof.
Sai suka sāke amsa masa suka ce, “Ran sarki yă daɗe, faɗa wa bayinka mafarkin, mu kuma za mu fassara shi.”
8 Then the King answered, and sayd, I knowe certeinly that ye would gaine the time, because ye see the thing is gone from me.
Sai sarki ya amsa ya ce, “Na gane cewa kuna ƙoƙari ku ɓata lokaci ne kawai domin ku ga na manta da abin.
9 But if ye will not declare mee the dreame, there is but one iudgement for you: for ye haue prepared lying and corrupt wordes, to speake before me till the time bee changed: therefore tell me the dreame, that I may knowe, if yee can declare me the interpretation thereof.
In ba ku faɗa mini mafarkin ba, akwai hukunci guda ɗaya kurum dominku. Kun haɗa baki domin ku faɗa mini munanan al’amura domin ku ruɗe ni har lokaci yă wuce. Sai ku faɗa mini mafarkin, ta haka kuwa zan sani za ku iya yi mini fassararsa.”
10 Then the Caldeans answered before the King, and sayde, There is no man vpon earth that can declare the Kings matter: yea, there is neither king nor prince nor lorde that asked such things at an inchanter or astrologian or Caldean.
Sai masanan taurarin suka amsa wa sarki suka ce, “Babu wani mutum a duniyan nan da zai iya yin abin da sarki yake nema! Babu wani sarki mai daraja da girma wanda ya taɓa yin irin wannan tambaya ga masu sihiri ko masu dabo ko masanan taurari.
11 For it is a rare thing that the King requireth, and there is none other that can declare it before the King, except the gods whose dwelling is not with flesh.
Abin da sarki yake nema yana da wuya matuƙa. Babu wani da zai iya bayyana wannan ga sarki sai dai alloli; kuma ba su zama tare da’yan adam.”
12 For this cause the king was angrie and in great furie, and commanded to destroy all the wise men of Babel.
Wannan ya sa sarki ya fusata ƙwarai, ya ba da umarni a tafi da dukan masu hikima na Babilon a kashe su.
13 And when sentence was giuen, the wise men were slayne: and they sought Daniel and his fellowes to be put to death.
Sai aka ba da dokar da za a kashe masu hikima, sa’an nan aka aika mutane su je su nemo Daniyel da abokansa domin a kashe su.
14 Then Daniel answered with counsel and wisedome to Arioch the Kings chiefe stewarde, which was gone foorth to put to death the wise men of Babel.
Sa’ad da Ariyok, shugaban ƙungiyar matsaran sarki, ya fita domin yă kashe masu hikima na Babilon, sai Daniyel ya yi masa magana cikin hikima da dabara.
15 Yea, he answered and sayde vnto Arioch the kings captaine, Why is the sentence so hastie from the king? Then Arioch declared the thing to Daniel.
Ya tambayi mai tsaro na sarki, “Me ya sa sarki ya fitar da wannan doka haka da fushi?” Sai Ariyok ya yi wa Daniyel bayanin batun.
16 So Daniel went and desired the king that he woulde giue him leasure and that he woulde shewe the king the interpretation thereof.
Da jin haka sai Daniyel ya tafi wurin sarki ya nemi ƙarin lokaci, domin yă bayyana wa sarki mafarkin da kuma fassararsa.
17 The Daniel went to his house and shewed the matter to Hananiah, Mishael, and Azariah his companions,
Sa’an nan Daniyel ya komo gida ya kuma sanar wa abokansa Hananiya, Mishayel da Azariya, batun nan duka.
18 That they should beseech the God of heauen for grace in this secrete, that Daniel and his fellowes should not perish with the rest of ye wise men of Babel.
Ya roƙe su su roƙi jinƙan Allah na sama domin wannan mafarki, saboda kada a kashe shi da abokansa tare da sauran masu hikima na Babilon.
19 Then was the secret reueiled vnto Daniel in a vision by night: therefore Daniel praysed the God of heauen.
A wannan dare sai aka bayyana wa Daniyel mafarkin cikin wahayi. Daniyel kuwa ya ɗaukaka Allah na sama.
20 And Daniel answered and sayde, The Name of God be praysed for euer and euer: for wisedome and strength are his,
Ya ce, “Yabo ya tabbata ga sunan Allah har abada abadin; hikima da iko nasa ne.
21 And hee changeth the times and seasons: he taketh away kings: he setteth vp kings: he giueth wisedome vnto the wise, and vnderstanding to those that vnderstand.
Yana sāke lokuta, yana tuɓe sarakuna yana kuma naɗa waɗansu. Yana ba da hikima ga masu hikima kuma ilimi ga masu basira.
22 Hee discouereth the deepe and secrete things: he knoweth what is in darkenes, and the light dwelleth with him.
Yakan bayyana zurfafa da ɓoyayyun abubuwa; ya san abin da yake cikin dare, haske kuwa yana zaune tare da shi.
23 I thanke thee and prayse thee, O thou God of my fathers, that thou hast giuen mee wisedome and strength, and hast shewed me nowe the thing that wee desired of thee: for thou hast declared vnto vs the kings matter.
Na gode maka ina yabonka, Allah na kakannina. Kai ka san hikima da iko, ka sanar da ni abin da muka tambaye ka, ka kuma sanar da mu mafarkin sarki.”
24 Therefore Daniel went vnto Arioch, whome the King had ordeyned to destroy the wise men of Babel: he went and sayde thus vnto him, Destroy not the wise men of Babel, but bring me before the King, and I will declare vnto the King the interpretation.
Sai Daniyel ya tafi wurin Ariyok, wanda sarki ya sa yă kashe masu hikiman Babilon, ya kuma ce masa, “Kada ka kashe masu hikiman Babilon ka kai ni wurin sarki, ni kuma zan fassara masa mafarkinsa.”
25 Then Arioch brought Daniel before the King in all haste, and sayd thus vnto him, I haue found a man of the children of Iudah that were brought captiues, that will declare vnto the King the interpretation.
Sai Ariyok ya kai Daniyel wurin sarki nan take ya ce masa, “Na gano wani mutum daga cikin kamammun kabilar Yahuda wanda zai faɗa wa sarki abin da mafarkin yake nufi.”
26 Then answered the King, and sayde vnto Daniel, whose name was Belteshazzar, Art thou able to shew me the dreame, which I haue seene, and the interpretation thereof?
Sarki ya tambayi Daniyel (wanda ake kira Belteshazar), za ka iya faɗa mini mafarkin da na yi ka kuma fassara shi?
27 Daniel answered in the presence of the King, and sayd, The secret which the King hath demanded, can neither the wise, the astrologians, the inchanters, nor the southsayers declare vnto the King.
Daniyel ya amsa, “Babu wani mai hikima, ko mai sihiri, ko mai dabo ko mai duban da zai iya warware wa sarki wannan matsala da ta dame shi,
28 But there is a God in heauen that reueileth secrets, and sheweth the King Nebuchad-nezzar what shall bee in the latter dayes. Thy dreame, and the things which thou hast seene in thine heade vpon thy bed, is this.
amma akwai Allahn da yake a sama wanda yake bayyana asirai, ya nuna wa sarki Nebukadnezzar abin da zai faru a kwanaki masu zuwa. Mafarkinka da wahayin da ya wuce cikin tunaninka a sa’ad da kake kwance a gadonka su ne,
29 O King, when thou wast in thy bedde, thoughts came into thy mind, what should come to passe hereafter, and he that reueyleth secretes, telleth thee, what shall come.
“A sa’ad da kake kwance, ya sarki, tunaninka ya ga al’amuran da suke zuwa, kuma shi mai bayyana al’amuran ya bayyana maka asiran abubuwan da za su faru.
30 As for me, this secret is not shewed mee for any wisedome that I haue, more then any other liuing, but onely to shewe the King the interpretation, and that thou mightest knowe the thoughts of thine heart.
Amma ba a bayyana mini wannan asiri saboda ina da wata hikima fiye da sauran mutane ba, sai dai domin a sanar wa sarki da fassarar, ka kuma san tunanin da ya shiga zuciyarka.
31 O King, thou sawest, and beholde, there was a great image: this great image whose glory was so excellent, stood before thee, and the forme thereof was terrible.
“Ya sarki, ka ga wata babbar siffa, mai girma, siffa ce mai haske, abar bantsoro tana tsaye a gabanka.
32 This images head was of fine golde, his breast and his armes of siluer, his bellie and his thighs of brasse,
An yi kan wannan siffa da zinariya zalla, ƙirjinta da kuma hannuwanta an yi su da azurfa, cikinta da kuma cinyarta da tagulla ne.
33 His legges of yron, and his feete were part of yron, and part of clay.
An yi ƙafafun da ƙarfe, tafin ƙafafunta kuma an yi rabi da ƙarfe rabi kuma da yumɓu.
34 Thou beheldest it til a stone was cut without hands, which smote the image vpon his feete, that were of yron and clay, and brake them to pieces.
A lokacin da kake dubawa, sai aka yanko wani dutse, amma ba da hannun mutum ba. Ya fāɗa a kan ƙafafun siffar na ƙarfen da aka haɗa da yumɓu aka kuma ragargaje su.
35 Then was the yron, the clay, the brasse, the siluer and the golde broken all together, and became like the chaffe of the sommer floures, and the winde caryed them away, that no place was founde for them: and the stone that smote the image, became a great mountaine, and filled the whole earth.
Sai ƙarfen da yambun da tagulla da azurfan da kuma zinariyan suka ragargaje a lokaci ɗaya ya zama kamar ƙaiƙayi a masussuka a lokacin kaka. Sai iska ta kwashe su ta tafi, har ba a iya ganin ko alamarsu. Amma dutsen da ya fāɗo a siffar ya girke ya zama tsauni ya kuma cika dukan duniya.
36 This is the dreame, and we will declare before the King the interpretation thereof.
“Wannan shi ne mafarkin, yanzu kuma za mu fassara ta wa sarki.
37 O King, thou art a king of Kings: for the God of heauen hath giuen thee a kingdome, power, and strength, and glorie.
Ya, sarki, kai ne sarkin sarakuna. Allah na sama ya ba ka iko da girma da suna;
38 And in all places where the children of men dwell, the beasts of the fielde, and the foules of the heauen hath he giuen into thine hand, and hath made thee ruler ouer them al: thou art this heade of golde.
a cikin hannunka ya sanya ɗan adam, da namun jeji da tsuntsayen sama. A duk inda suke zaune, ya maishe ka ka yi mulki a bisansu kai ne kan zinariyan nan na siffar.
39 And after thee shall rise another kingdome, inferiour to thee, of siluer, and another third kingdome shalbe of brasse, which shall beare rule ouer all the earth.
“A bayanka, za a yi wani mulki, wanda bai kai naka ba. A gaba kuma, za a yi mulki na uku wanda yake na tagulla, zai yi mulkin dukan duniya.
40 And the fourth kingdome shall be strong as yron: for as yron breaketh in pieces, and subdueth all things, and as yron bruiseth all these things, so shall it breake in pieces, and bruise all.
A ƙarshe, za a yi mulki na huɗu, mai ƙarfi kamar ƙarfe, Da yake baƙin ƙarfe yakan kakkarya, ya ragargaje abubuwa, haka nan wannan mulki zai ragargaje sauran mulkoki
41 Where as thou sawest the feete and toes, parte of potters clay, and part of yron: the kingdome shalbe deuided, but there shalbe in it of the strength of the yron, as thou sawest the yron mixt with the clay, and earth.
Ka kuma ga an yi ƙafafun da yatsotsin da baƙin ƙarfe gauraye da yumɓu, wato, mulkin zai rabu, amma zai kasance da ƙarfi kamar na baƙin ƙarfe da yake gauraye da yumɓu.
42 And as the toes of the feete were parte of yron, and parte of clay, so shall the kingdome be partly strong, and partly broken.
Kamar yadda yatsotsin rabi na ƙarfe rabi kuma na yumɓu ne, haka wannan mulki zai zama rabi mai ƙarfi rabi kuma marar ƙarfi.
43 And where as thou sawest yron mixt with clay and earth, they shall mingle themselues with the seede of men: but they shall not ioyne one with another, as yron can not bee mixed with clay.
Kamar dai yadda ka ga ƙarfen ya gauraye da yumɓu, haka mutanen za su zama a gauraye amma ba za su haɗu da juna ba, kamar yadda baƙin ƙarfe da yumɓu ba su haɗuwa.
44 And in the dayes of these Kings, shall the God of heauen set vp a kingdome, which shall neuer be destroyed: and this kingdome shall not be giuen to another people, but it shall breake, and destroy al these kingdomes, and it shall stand for euer.
“A lokacin mulkin waɗannan sarakunan, Allah na sama zai kafa mulki da ba zai taɓa rushewa ba, ba kuma za a ba ma waɗansu mutane ba. Zai ragargaje waɗannan mulkokin da kuma kawo su ga ƙarshe, amma shi wannan mulki zai dawwama har abada.
45 Where as thou sawest, that the stone was cut of the mountaine without handes, and that it brake in pieces the yron, the brasse, the clay, the siluer, and the golde: so the great God hath shewed the King, what shall come to passe hereafter, and the dreame is true, and the interpretation thereof is sure.
Wannan shi ne ma’anar wannan wahayin da ka gani na dutsen da aka yanko daga jikin tsaunin, amma ba da hannun ɗan adam ba, dutsen da ya ragargaza ƙarfen, da tagullar, da yumɓun da azurfar da kuma zinariyar. “Allah mai girma ya nuna wa sarki abin da zai faru nan gaba. Mafarkin gaskiya ne, fassararsa kuma abin dogara ne.”
46 Then the King Nebuchad-nezzar fell vpon his face, and bowed himselfe vnto Daniel, and commanded that they should offer meate offrings, and sweete odours vnto him.
Sai sarki Nebukadnezzar ya fāɗi da fuskarsa har ƙasa a gaban Daniyel domin ya girmama shi ya kuma umarta a miƙa hadaya da kuma hadayar ƙonawa ta turare ga Daniyel.
47 Also the King answered vnto Daniel, and said, I know of a trueth that your God is a God of gods, and the Lord of Kings, and the reueiler of secrets, seeing thou couldest open this secret.
Sarki ya kuma ce wa Daniyel, “Tabbatacce Allahnka shi ne Allahn alloli da kuma Sarkin sarakuna da mai bayyana asirai, gama ka iya bayyana wannan asiri.”
48 So the King made Daniel a great man, and gaue him many and great giftes. Hee made him gouernour ouer the whole prouince of Babel, and chiefe of the rulers, and aboue all the wise men of Babel.
Sai sarki ya ɗora Daniyel a babban matsayi ya kuma sanya shi mai mulki a kan dukan yankin ƙasar Babilon; ya kuma ɗora shi yă zama mai kula da duk masu hikima.
49 Then Daniel made request to the King, and hee set Shadrach, Meshach, and Abednego ouer the charge of the prouince of Babel: but Daniel sate in the gate of the King.
Bugu da ƙari, bisa ga bukatar Daniyel sai sarki yă naɗa Shadrak da Meshak da Abednego su zama masu kula da harkokin lardin Babilon, amma Daniyel kuma ya tsaya a fadar sarki.

< Daniel 2 >