< Acts 1 >

1 I have made the former treatise, O Theophilus, of al that Jesus began to doe and teach,
A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
2 Vntill the day that hee was taken vp, after that hee through the holy Ghost, had giuen commandements vnto the Apostles, whome hee had chosen:
har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
3 To whome also he presented himselfe aliue after that he had suffered, by many infallible tokens, being seene of them by the space of fourtie daies, and speaking of those thinges which appertaine to the kingdome of God.
Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
4 And when he had gathered them together, he commanded them, that they should not depart from Hierusalem, but to waite for the promise of the Father, which sayde hee, yee haue heard of me.
A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
5 For Iohn in deede baptized with water, but ye shall be baptized with the holy Ghost within these fewe daies.
Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
6 When they therefore were come together, they asked of him, saying, Lord, wilt thou at this time restore the kingdome to Israel?
Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
7 And hee saide vnto them, It is not for you to know the times, or the seasons, which the Father hath put in his owne power,
Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
8 But yee shall receiue power of the holy Ghost, when he shall come on you: and ye shalbe witnesses vnto me both in Hierusalem and in all Iudea, and in Samaria, and vnto the vttermost part of the earth.
Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
9 And when he had spoken these things, while they behelde, he was taken vp: for a cloude tooke him vp out of their sight.
Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
10 And while they looked stedfastly towarde heauen, as hee went, beholde, two men stoode by them in white apparell,
Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
11 Which also sayde, Yee men of Galile, why stande yee gasing into heauen? This Iesus which is taken vp from you into heauen, shall so come, as yee haue seene him goe into heauen.
Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
12 Then returned they vnto Hierusalem from the mount that is called the mount of Oliues, which is neere to Hierusalem, being from it a Sabbath daies iourney.
Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
13 And when they were come in, they went vp into an vpper chamber, where abode both Peter and Iames, and Iohn, and Andrew, Philip, and Thomas, Bartlemew, and Matthewe, Iames the sonne of Alpheus, and Simon Zelotes, and Iudas Iames brother.
Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
14 These all continued with one accorde in prayer and supplication with the women, and Marie the mother of Iesus, and with his brethren.
Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
15 And in those dayes Peter stoode vp in the middes of the disciples, and sayde (nowe the nomber of names that were in one place were about an hundreth and twentie.)
A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
16 Yee men and brethren, this scripture must needes haue beene fulfilled, which the holy Ghost by the mouth of Dauid spake before of Iudas, which was guide to them that tooke Iesus.
ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
17 For hee was nombred with vs, and had obteined fellowship in this ministration.
dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
18 He therefore hath purchased a field with the reward of iniquitie: and when he had throwen downe himselfe headlong, hee brast asunder in the middes, and all his bowels gushed out.
(Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
19 And it is knowen vnto all the inhabitants of Hierusalem, in so much, that that field is called in their owne language, Aceldama, That is, the field of blood.
Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
20 For it is written in the booke of Psalmes, Let his habitation be void, and let no man dwel therein: also, Let another take his charge.
Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
21 Wherefore of these men which haue companied with vs, all the time that the Lord Iesus was conuersant among vs,
Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
22 Beginning from the baptisme of Iohn vnto the day that hee was taken vp from vs, must one of them bee made a witnesse with vs of his resurrection.
farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
23 And they presented two, Ioseph called Barsabas, whose surname was Iustus, and Matthias.
Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
24 And they praied, saying, Thou Lord, which knowest the hearts of all men, shewe whether of these two thou hast chosen,
Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
25 That he may take the roume of this ministration and Apostleship, from which Iudas hath gone astray, to goe to his owne place.
ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
26 Then they gaue foorth their lottes: and the lotte fell on Matthias, and hee was by a common consent counted with the eleuen Apostles.
Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.

< Acts 1 >