< Acts 25 >

1 When Festus was then come into the prouince, after three dayes he went vp from Caesarea vnto Hierusalem.
Da Festas ya shiga lardin, kuma bayan kwana uku, ya tashi daga Kaisariya ya tafi Urushalima.
2 Then the high Priest, and the chiefe of the Iewes appeared before him against Paul: and they besought him,
Sai babban firist da manyan Yahudawa suka kawo wa Festas sara a kan Bulus.
3 And desired fauour against him, that hee would send for him to Hierusalem: and they layd waite to kill him by the way.
Suka roki tagomashi wurin Festas ya kira Bulus zuwa Urushalima domin su kashe shi a hanya.
4 But Festus answered, that Paul should bee kept at Caesarea, and that he himselfe would shortly depart thither.
Amma Festas ya amsa masu cewa, Bulus dan sarka ne a Kaisariya, kuma ba da dadewa ba shi da kansa zai koma can.
5 Let them therefore, saide he, which among you are able, come downe with vs: and if there be any wickednes in the man, let them accuse him.
“Saboda haka duk wadanda za su iya, su biyo mu. Idan akwai wani laifi game da mutumin, sai ku zarge shi.”
6 Now when he had taried among them no more then ten dayes, hee went downe to Caesarea, and the next day sate in the iudgement seat, and commanded Paul to be brought.
Bayan kwana takwas ko goma, sai ya gangara zuwa Kaisariya. Washegari ya zauna bisa kursiyin shari'a ya bada umarni a kawo Bulus a gabansa.
7 And when hee was come, the Iewes which were come from Hierusalem, stoode about him and layd many and grieuous complaints against Paul, whereof they could make no plaine proofe,
Da Bulus ya iso, Yahudawa daga Urushalima suka tsaya kusa, suka yi ta kawo kararraki, amma basu iya tabbatar da su ba.
8 Forasmuch as he answered, that he had neither offended any thing against the lawe of the Iewes, neither against ye temple, nor against Caesar.
Bulus ya kare kansa ya ce, “Ban yi wa kowa laifi ba, ko Yahudawa, ko haikali, ko kuma Kaisar.”
9 Yet Festus willing to get fauour of the Iewes, answered Paul and saide, Wilt thou goe vp to Hierusalem, and there be iudged of these things before mee?
Amma Festas yana neman farin jini wajen Yahudawa, sabo da haka ya tambayi Bulus ya ce, “Kana so ka je Urushalima in shari'anta ka a can game da wadannan abubuwa?”
10 Then said Paul, I stand at Caesars iudgment seate, where I ought to be iudged: to the Iewes I haue done no wrong, as thou very well knowest.
Bulus ya ce, “Ina tsaye a Ddakalin Shari'ar Kaisar inda dole a shari'anta ni. Ban yi wa Yahudawa laifi ba, kamar yadda ka sani sosai.
11 For if I haue done wrong, or committed any thing worthie of death, I refuse not to die: but if there be none of these things whereof they accuse me, no man, to pleasure them, can deliuer me to them: I appeale vnto Caesar.
Idan lallai na yi laifi kuma na yi abin da ya chanchanci mutuwa, ban ki ba in mutu. Amma idan zarginsu karya ne, kada kowa ya bashe ni gare su. Ina daukaka kara zuwa ga Kaisar.”
12 Then when Festus had spoken with the Council, hee answered, Hast thou appealed vnto Caesar? vnto Caesar shalt thou goe.
Bayan Festas ya tattauna da majalisa ya amsa ya ce, “Kana kira ga Kaisar; za ka tafi wurin Kaisar.”
13 And after certaine dayes, King Agrippa and Bernice came downe to Caesarea to salute Festus.
Bayan wadansu kwanaki, sarki Agaribas da Barniki suka iso Kaisariya domin su ziyarci Festas.
14 And when they had remained there many dayes, Festus declared Pauls cause vnto the King, saying, There is a certaine man left in prison by Felix,
Da ya kasance kwanaki da yawa, Festas ya fada wa sarki labarin Bulus ya ce, “Akwai wani mutum dan sarka da Filikus ya bari a kurkuku.
15 Of whom when I came to Hierusalem, the high Priestes and Elders of the Iewes informed me, and desired to haue iudgement against him.
Sa'anda nake a Urushalima, babban firist da dattawan Yahudawa suka kawo kararsa gare ni, suka roka a kashe shi.
16 To whome I answered, that it is not the maner of the Romanes for fauour to deliuer any man to the death, before that hee which is accused, haue the accusers before him, and haue place to defend himselfe, concerning the crime.
Game da wannan na amsa na ce masu, ba al'adar Romawa ba ce a ba da mutum tagomashi; sai wanda ake kararsa an bashi zarafi ya kare kansa a gaban masu kararsa, ya kuma bada hujjojinsa game da kararakin.
17 Therefore when they were come hither, without delay the day following I sate on the iudgement seate, and commanded the man to be brought foorth.
Saboda haka, da duk suka taru ban bata lokaci ba, washegari na zauna a kujerar shari'a, na ba da umarni a kawo mutumin.
18 Against whom when the accusers stood vp, they brought no crime of such things as I supposed:
Da masu karar suka fadi kararsu, sai na fahimci karar ba wani muhimmin abu a cikinta.
19 But had certaine questions against him of their owne superstition, and of one Iesus which was dead, whom Paul affirmed to be aliue.
Sai dai na ga cewa jayayya ce tsakanin su ta addini a kan wani Yesu da ya mutu, wanda Bulus ya ce yana da rai.
20 And because I doubted of such maner of question, I asked him whether he would goe to Hierusalem, and there be iudged of these things.
Na rasa yadda zan bincike wannan al'amarin, sai na tambaye shi ko zai je Urushalima a shari'anta shi kan wadannan abubuwa.
21 But because he appealed to be reserued to the examination of Augustus, I commanded him to be kept, till I mght send him to Cesar.
Amma da Bulus ya nemi a lura da shi, Kaisar ya shari'anta shi, sai na ba da umarni a ajiye shi har sai na aika shi wurin Kaisar.”
22 Then Agrippa sayd vnto Festus, I would also heare the man my selfe. To morowe, sayd he, thou shalt heare him.
Agaribas yace wa Festas. “Zan so ni ma in saurari mutumin nan.” “Gobe za ka ji shi,” in ji Fostus.
23 And on the morowe when Agrippa was come and Bernice with great pompe, and were entred into the Common hall with the chiefe captaines and chiefe men of the citie, at Festus commandement Paul was brought forth.
Washegari Agaribas da Barniki suka zo tare da kasaitaccen taro suka shiga dakin taro tare da hafsoshi da shugabanin gari. Da Festas ya ba da umarni, aka fito da Bulus wurinsu.
24 And Festus sayd, King Agrippa, and all men which are present with vs, ye see this man, about whom all the multitude of the Iewes haue called vpon me, both at Hierusalem, and here, crying, that he ought not to liue any longer.
Festas ya ce, “Sarki Agaribas da dukanku da kuke tare da mu a nan, kun ga mutumin nan, dukan Yahudawa sun gana da ni a Urushalima da nan kuma. Suna mani ihu cewa, bai chanchanta a bar shi da rai ba.
25 Yet haue I found nothing worthy of death, that he hath committed: neuertheles, seeing that he hath appealed to Augustus, I haue determined to send him.
Na gane bai yi wani abin da ya chanchanci mutuwa ba; amma saboda ya daukaka kara zuwa Kaisar, na yanke shawara in aika shi.
26 Of whome I haue no certaine thing to write vnto my Lord: wherefore I haue brought him forth vnto you, and specially vnto thee, King Agrippa, that after examination had, I might haue somewhat to write.
Amma ba ni da wani dalili na musamman da zan rubuta wasika ga Kaisar. Saboda wannan dalili na kawo shi gabanku, masamman kai ya sarki Agaribas. Domin in sami karin abin da zan rubuta game da shi.
27 For me thinketh it vnreasonable to send a prisoner, and not to shewe the causes which are layde against him.
Gama a ganina wauta ce in aika dan sarka ba tare da na rubuta laifi a kansa ba.”

< Acts 25 >