< Acts 22 >
1 Ye men, brethren and Fathers, heare my defence nowe towards you.
“’Yan’uwa da iyaye, ku saurari kāriyata yanzu.”
2 (And when they heard that he spake in the Hebrewe tongue to them, they kept the more silence, and he sayd)
Da suka ji ya yi musu magana da Arameyik, sai suka yi tsit. Sai Bulus ya ce,
3 I am verely a man, which am a Iew, borne in Tarsus in Cilicia, but brought vp in this citie at the feete of Gamaliel, and instructed according to the perfect maner of the Lawe of the Fathers, and was zealous toward God, as ye all are this day.
“Ni mutumin Yahuda ne haifaffen Tarshish na Silisiya, amma a nan birnin ne aka rene ni. Aka horar da ni sosai cikin dokokin kakanninmu a ƙarƙashin Gamaliyel ni ma dā mai himma ne cikin bauta wa Allah kamar yadda kowannenku yake a yau.
4 And I persecuted this way vnto the death, binding and deliuering into prison both men and women.
Na tsananta wa masu bin wannan Hanyar har ga mutuwarsu, ina kama maza da mata ina kuma jefa su cikin kurkuku,
5 As also ye chiefe Priest doeth beare me witnes, and al the company of the Elders: of whom also I receiued letters vnto the brethren, and went to Damascus to bring them which were there, bound vnto Hierusalem, that they might be punished.
kamar yadda babban firist da dukan Majalisa za su iya shaida. Na ma karɓi wasiƙu daga gare su zuwa ga’yan’uwansu a Damaskus, na kuma tafi can don in kawo waɗannan mutane a daure zuwa Urushalima don a hukunta su.
6 And so it was, as I iourneyed and was come neere vnto Damascus about noone, that suddenly there shone from heauen a great light round about me.
“Wajen tsakar rana da na yi kusa da Damaskus, ba zato ba tsammani sai wani babban haske daga sama ya haskaka kewaye da ni.
7 So I fell vnto the earth, and heard a voyce, saying vnto me, Saul, Saul, why persecutest thou mee?
Sai na fāɗi a ƙasa na kuma ji wata murya ta ce mini, ‘Shawulu! Shawulu! Don me kake tsananta mini?’
8 Then I answered, Who art thou, Lord? And he said to me, I am Iesus of Nazareth, whom thou persecutest.
“Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ya amsa ya ce, ‘Ni ne Yesu Banazare, wanda kake tsanantawa.’
9 Moreouer they that were with me, sawe in deede a light and were afraide: but they heard not the voyce of him that spake vnto me.
Abokan tafiyata suka ga hasken, amma ba su fahimci muryar mai magana da ni ba.
10 Then I sayd, What shall I doe, Lord? And the Lord sayde vnto me, Arise, and goe into Damascus: and there it shall be tolde thee of all things, which are appointed for thee to doe.
“Sai na yi tambaya, na ce, ‘Me zan yi, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Tashi, ka tafi cikin Damaskus. A can za a faɗa maka duk abin da aka shirya za ka yi.’
11 So when I could not see for the glory of that light, I was led by the hand of them that were with me, and came into Damascus.
Abokan tafiyata suka ja ni a hannu zuwa cikin Damaskus, saboda ƙarfin hasken ya makanta ni.
12 And one Ananias a godly man, as perteining to the Lawe, hauing good report of all the Iewes which dwelt there,
“Wani mutumin da ake kira Ananiyas ya zo ya gan ni. Shi mai ibada ne wajen kiyaye dokoki wanda dukan Yahudawan da suke zama a can suna girmama shi ƙwarai.
13 Came vnto me, and stoode, and sayd vnto me, Brother Saul, receiue thy sight: and that same houre I looked vpon him.
Ya tsaya kusa da ni ya ce, ‘Ɗan’uwa Shawulu, ka sami ganin garinka!’ A daidai lokacin kuwa na iya ganinsa.
14 And he sayd, The God of our fathers hath appointed thee, that thou shouldest knowe his wil, and shouldest see that Iust one, and shouldest heare the voyce of his mouth.
“Sa’an nan ya ce, ‘Allah na kakanninmu ya zaɓe ka ka san nufinsa ka kuma ga Mai Adalcin nan ka kuma ji kalmomi daga bakinsa.
15 For thou shalt be his witnes vnto all men, of the things which thou hast seene and heard.
Za ka zama mai shaidarsa ga dukan mutane game da abin da ka gani ka kuma ji.
16 Now therefore why tariest thou? Arise, and be baptized, and wash away thy sinnes, in calling on the Name of the Lord.
Yanzu me kake jira? Ka tashi, a yi maka baftisma, a wanke zunubanka, ta wurin kira bisa ga sunansa.’
17 And it came to passe, that when I was come againe to Hierusalem, and prayed in the Temple, I was in a traunce,
“Sa’ad da na dawo Urushalima ina cikin addu’a a haikali, sai na ga wahayi
18 And saw him saying vnto me, Make haste, and get thee quickly out of Hierusalem: for they will not receiue thy witnes concerning me.
na ga Ubangiji yana magana. Ya ce mini, ‘Maza! Ka bar Urushalima, gama ba za su yarda da shaidarka game da ni ba.’
19 Then I sayd, Lord, they know that I prisoned, and beat in euery Synagogue them that beleeued in thee.
“Na amsa na ce, ‘Ubangiji, waɗannan mutane sun san cewa na bi majami’a-majami’a na jefa waɗanda suka gaskata da kai a cikin kurkuku, in kuma yin musu dūka.
20 And when the blood of thy martyr Steuen was shed, I also stood by, and consented vnto his death, and kept the clothes of them that slew him.
Sa’ad da kuma aka zub da jinin Istifanus mashaidinka, na tsaya can ina ba da goyon bayana ina kuma tsaron tufafin masu kisansa.’
21 Then he sayd vnto me, Depart: for I will send thee farre hence vnto the Gentiles.
“Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, ‘Je ka; zan aike ka can nesa a wurin Al’ummai.’”
22 And they heard him vnto this worde, but then they lift vp their voyces, and sayd, Away with such a fellow from the earth: for it is not meete that he should liue.
Taron suka saurari Bulus sai da ya yi wannan magana. Sa’an nan suka ɗaga muryoyinsu suka yi ihu suka ce, “A raba duniya da wannan mutum! Bai cancanci yă rayu ba!”
23 And as they cried and cast off their clothes, and threw dust into the aire,
Da suna ihu suna kaɗa mayafansu suna da tā da ƙura sama,
24 The chiefe captaine commanded him to be led into the castle, and bade that he should be scourged, and examined, that he might knowe wherefore they cryed so on him.
sai shugaban ƙungiyar sojan ya umarta a kai Bulus a barikin soja. Ya ba da umarni a yi masa bulala a kuma tambaye shi abin da ya sa mutane suke masa ihu haka.
25 And as they bound him with thongs, Paul sayd vnto the Centurion that stood by, Is it lawfull for you to scourge one that is a Romane, and not condemned?
Suna kwantar da shi ke nan domin a yi masa bulala, sai Bulus ya ce wa jarumin da yake tsaye a nan, “Ashe, daidai ne bisa ga doka a yi wa ɗan ƙasar Roma bulala wanda ba a ma tabbatar da laifi a kansa ba?”
26 Nowe when the Centurion heard it, hee went, and tolde the chiefe captaine, saying, Take heede what thou doest: for this man is a Romane.
Da jarumin ya ji haka sai ya je wurin shugaban ƙungiyar sojan ya ce masa, “Me kake so yi ne? Wannan mutum ɗan ƙasar Roma ne.”
27 Then the chiefe captaine came, and sayd to him, Tel me, art thou a Romane? And he said, Yea.
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya je ya tambayi Bulus ya ce, “Faɗa mini, kai ɗan ƙasar Roma ne?” Bulus ya ce, “I.”
28 And the chiefe captaine answered, With a great summe obtained I this freedome. Then Paul sayd, But I was so borne.
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya ce, “Sai da na biya kuɗi mai yawa kafin in zama ɗan ƙasa.” Bulus ya ce, “Ni kuwa an haife ni ɗan ƙasa.”
29 Then straightway they departed from him, which should haue examined him: and the chiefe captaine also was afrayd, after he knewe that hee was a Romane, and that he had bound him.
Waɗanda dā suke shirin yin masa tambayoyi suka ja da baya nan da nan. Shugaban ƙungiyar sojan kansa ya tsorata da ya fahimci cewa ya sa wa Bulus, ɗan ƙasar Roma sarƙa.
30 On the next day, because hee would haue knowen the certaintie wherefore he was accused of the Iewes, he loosed him from his bonds, and commanded the hie Priests and all their Councill to come together: and he brought Paul, and set him before them.
Kashegari da yake shugaban ƙungiyar sojan ya so yă tabbatar da ainihin abin da ya sa Yahudawa suke zargin Bulus, sai ya sake shi ya kuwa umarci manyan firistoci da dukan Majalisar su taru. Sa’an nan ya kawo Bulus ya sa ya tsaya a gabansu.