< Acts 2 >
1 And when the day of Pentecost was come, they were al with one accord in one place.
Da ranar Fentekos ta yi, dukansu suna tare wuri ɗaya.
2 And suddenly there came a sounde from heauen, as of a russhing and mightie winde, and it filled all the house where they sate.
Ba zato ba tsammani sai aka ji motsi kamar ta babbar iska tana hurowa daga sama ta kuma cika dukan gidan da suke zaune.
3 And there appeared vnto them clouen tongues, like fire, and it sate vpon eche of them.
Suka ga wani abin da ya yi kama da harsunan wuta, suka rarrabu suna kuma sassauka a kan kowannensu.
4 And they were all filled with the holy Ghost, and began to speake with other tongues, as the Spirit gaue them vtterance.
Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka kuma fara magana da waɗansu harsuna yadda Ruhu ya sa suka iya.
5 And there were dwelling at Hierusalem Iewes, men that feared God, of euery nation vnder heauen.
To, a Urushalima akwai Yahudawa masu tsoron Allah, daga kowace ƙasa a duniya.
6 Nowe when this was noised, the multitude came together and were astonied, because that euery man heard them speake his owne language.
Da suka ji wannan motsi, taro ya haɗu wuri ɗaya a ruɗe, domin kowannensu ya ji suna magana da yarensa.
7 And they wondered al, and marueiled, saying among themselues, Beholde, are not all these which speake, of Galile?
Cike da mamaki, suka yi tambaya suna cewa, “Ashe, duk waɗannan mutane masu magana ba Galiliyawa ba ne?
8 How then heare we euery man our owne language, wherein we were borne?
To, yaya kowannenmu yana ji suna yarensa?
9 Parthians, and Medes, and Elamites, and the inhabitants of Mesopotamia, and of Iudea, and of Cappadocia, of Pontus, and Asia,
Fartiyawa, Medes da Elamawa; mazaunan Mesofotamiya, Yahudiya da Kaffadokiya, Fontus da Asiya,
10 And of Phrygia, and Pamphylia, of Egypt, and of the partes of Libya, which is beside Cyrene, and strangers of Rome, and Iewes, and Proselytes,
Firjiya da Famfiliya, Masar da sassa Libiya kusa da Sairin; baƙi daga Roma
11 Creetes, and Arabians: wee hearde them speake in our owne tongues the wonderful works of God.
(Yahudawa da kuma waɗanda suka tuba suka shiga Yahudanci); Kiretawa da Larabawa, mun ji su suna shelar abubuwan banmamaki na Allah da yarenmu!”
12 They were all then amased, and douted, saying one to another, What may this be?
A ruɗe kuma cike da mamaki, suka tambayi junansu cewa, “Mene ne wannan yake nufi?”
13 And others mocked, and saide, They are full of newe wine.
Duk da haka waɗansu suka yi musu ba’a suka ce, “Sun yi tatil da ruwan inabi ne.”
14 But Peter standing with ye Eleuen, lift vp his voice, and said vnto them, Ye men of Iudea, and ye all that inhabite Hierusalem, be this knowen vnto you, and hearken vnto my woordes.
Sai Bitrus ya miƙe tsaye tare da Sha Ɗayan nan, ya ɗaga muryarsa ya yi wa taron jawabi ya ce, “’Yan’uwana Yahudawa da dukanku da kuke zama cikin Urushalima, bari in bayyana muku wannan, ku saurara da kyau ga abin da zan faɗa.
15 For these are not drunken, as yee suppose, since it is but the third houre of the day.
Waɗannan mutane ba su bugu ba, kamar yadda kuka ɗauka. Yanzu ƙarfe tara na safe ne kawai!
16 But this is that, which was spoken by the Prophet Ioel,
A’a, ai, abin da aka yi magana ta bakin annabi Yowel ke nan cewa,
17 And it shalbe in the last daies, saith God, I wil powre out of my Spirite vpon al flesh, and your sonnes, and your daughters shall prophecie, and your yong men shall see visions, and your old men shall dreame dreames.
“Allah ya ce, ‘A kwanakin ƙarshe, zan zubo Ruhuna bisa dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, samarinku za su ga wahayoyi, dattawanku kuma za su yi mafarkai.
18 And on my seruauntes, and on mine handmaides I will powre out of my Spirite in those daies, and they shall prophecie.
Kai, har ma a kan bayina, maza da mata, zan zubo Ruhuna a waɗancan kwanaki, za su kuwa yi annabci.
19 And I wil shew wonders in heauen aboue, and tokens in the earth beneath, blood, and fire, and the vapour of smoke.
Zan nuna abubuwan banmamaki a sararin sama da alamu a nan ƙasa, jini da wuta da kuma hauhawan hayaƙi.
20 The Sunne shalbe turned into darkenesse, and the moone into blood, before that great and notable day of the Lord come.
Za a mai da rana duhu, wata kuma ya zama jini, kafin zuwa rana mai girma da kuma ta ɗaukaka ta Ubangiji.
21 And it shalbe, that whosoeuer shall call on the Name of the Lord, shalbe saued.
Kuma duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.’
22 Yee men of Israel, heare these woordes, JESUS of Nazareth, a man approued of God among you with great workes, and wonders, and signes, which God did by him in the middes of you, as yee your selues also knowe:
“Mutanen Isra’ila, ku saurari wannan. Yesu Banazare shi ne mutumin da Allah ya tabbatar muku ta wurin mu’ujizai, ayyukan banmamaki, da kuma alamu, waɗanda Allah ya yi a cikinku ta wurinsa, kamar yadda ku kanku kuka sani.
23 Him, I say, being deliuered by the determinate counsell, and foreknowledge of God, after you had taken, with wicked handes you haue crucified and slaine.
An ba da wannan mutum gare ku bisa ga nufin Allah da kuma rigyasaninsa, ku kuma tare da taimakon mugayen mutane, kuka kashe shi ta wurin kafa shi a kan gicciye.
24 Whome God hath raised vp, and loosed the sorrowes of death, because it was vnpossible that he should be holden of it.
Amma Allah ya tashe shi daga matattu, ya’yantar da shi daga azabar mutuwa, don ba ya yiwuwa mutuwa ta riƙe shi.
25 For Dauid sayeth concerning him, I beheld the Lord alwaies before me: for hee is at my right hand, that I should not be shaken.
Dawuda ya yi faɗi game da shi cewa, “‘Kullum ina ganin Ubangiji a gabana. Gama yana a hannuna na dama, ba zan jijjigu ba.
26 Therefore did mine heart reioyce, and my tongue was glad, and moreouer also my flesh shall rest in hope,
Saboda haka, zuciyata na farin ciki, harshena kuma na murna, jikina kuma zai kasance da bege,
27 Because thou wilt not leaue my soule in graue, neither wilt suffer thine Holy one to see corruption. (Hadēs )
gama ba za ka bar ni cikin kabari ba, ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Hadēs )
28 Thou hast shewed me the waies of life, and shalt make me full of ioy with thy countenance.
Ka sanar da ni hanyoyin rai, za ka cika ni da farin ciki a gabanka.’
29 Men and brethren, I may boldly speake vnto you of the Patriarke Dauid, that hee is both dead and buried, and his sepulchre remaineth with vs vnto this day.
“’Yan’uwa, zan iya tabbatar muku gabagadi cewa kakanmu Dawuda ya mutu aka kuma binne shi, kabarinsa kuwa yana a nan har yă zuwa yau.
30 Therefore, seeing hee was a Prophet, and knewe that God had sworne with an othe to him, that of the fruite of his loynes hee woulde raise vp Christ concerning the flesh, to set him vpon his throne,
Amma shi annabi ne ya kuma san abin da Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa zai ɗora ɗaya daga cikin zuriyarsa a kan gadon sarautarsa.
31 Hee knowing this before, spake of the resurrection of Christ, that his soule shoulde not bee left in graue, neither his flesh shoulde see corruption. (Hadēs )
Ganin abin da yake gaba, ya yi magana a kan tashin Kiristi daga matattu cewa, ba a bar shi a kabari ba, jikinsa kuma bai ruɓa ba. (Hadēs )
32 This Iesus hath God raised vp, whereof we all are witnesses.
Allah ya tashe wannan Yesu zuwa rai, mu kuwa duk shaidu ne ga wannan.
33 Since then that he by the right hande of God hath bene exalted, and hath receiued of his Father the promise of the holy Ghost, hee hath shed foorth this which yee nowe see and heare.
An ɗaukaka shi zuwa ga hannun dama na Allah, ya karɓi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga Uba, ya kuma zubo abin da yanzu kuke gani kuke kuma ji.
34 For Dauid is not ascended into heauen, but he sayth, The Lord sayd to my Lord, Sit at my right hande,
Gama Dawuda bai hau zuwa sama ba, duk da haka ya ce, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
35 Vntill I make thine enemies thy footestoole.
sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
36 Therefore, let all the house of Israel know for a suretie, that God hath made him both Lord, and Christ, this Iesus, I say, whome yee haue crucified.
“Saboda haka bari dukan Isra’ila su tabbatar da wannan. Allah ya mai da wannan Yesu, da kuka gicciye, Ubangiji da kuma Kiristi.”
37 Now when they heard it, they were pricked in their heartes, and said vnto Peter and the other Apostles, Men and brethren, what shall we doe?
Sa’ad da mutane suka ji wannan, sai suka soku a zuci sai suka ce wa Bitrus da sauran manzanni, “’Yan’uwa, me za mu yi?”
38 Then Peter said vnto them, Amend your liues, and bee baptized euery one of you in the Name of Iesus Christ for the remission of sinnes: and ye shall receiue the gift of the holy Ghost.
Bitrus ya amsa, “Ku tuba a kuma yi muku baftisma, kowannenku a cikin sunan Yesu Kiristi domin gafarar zunubanku. Za ku kuwa karɓi kyautar Ruhu Mai Tsarki.
39 For the promise is made vnto you, and to your children, and to all that are a farre off, euen as many as the Lord our God shall call.
Alkawarin dominku ne da’ya’yanku da kuma dukan waɗanda suke da nesa, domin dukan waɗanda Ubangiji Allahnmu zai kira.”
40 And with many other words he besought and exhorted them, saying, Saue your selues from this froward generation.
Da waɗansu kalmomi masu yawa ya gargaɗe su; ya kuma roƙe su cewa, “Ku ceci kanku daga wannan lalataccen zamani.”
41 Then they that gladly receiued his word, were baptized: and the same day there were added to the Church about three thousand soules.
Waɗanda suka yarda da saƙonsa kuwa aka yi musu baftisma, a ranar kuwa yawansu ya ƙaru da mutum kusan dubu uku.
42 And they continued in the Apostles doctrine, and fellowship, and breaking of bread, and prayers.
Suka ba da kansu ga koyarwar manzanni da kuma ga zumunci, ga gutsuttsura burodin da kuma ga addu’a.
43 And feare came vpon euery soule: and many wonders and signes were done by ye Apostles.
Kowa ya cika da tsoro, manzannin kuwa suka aikata abubuwan banmamaki da alamu masu yawa.
44 And all that beleeued, were in one place, and had all things common.
Dukan masu bi suna tare, suna kuma mallakar kome tare.
45 And they sold their possessions and goods, and parted them to all me, as euery one had need.
Suka dinga sayar da ƙaddarorinsu da kayayyakinsu, suka ba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
46 And they continued dayly with one accord in the Temple, and breaking bread at home, did eate their meate together with gladnesse and singlenesse of heart,
Kowace rana suka ci gaba da taruwa a filin haikali. Suka gutsuttsura burodi a gidajensu suna cin abinci tare da farin ciki da zuciya ɗaya,
47 Praysing God, and had fauour with all the people: and the Lord added to the Church from day to day, such as should be saued.
suna yabon Allah suna kuma samun tagomashin dukan mutane. Ubangiji kuwa ya ƙara yawansu kowace rana na waɗanda suke samun ceto.