< Acts 16 >
1 Then came he to Derbe and to Lystra: and beholde, a certaine disciple was there named Timotheus, a womans sonne, which was a Iewesse and beleeued, but his father was a Grecian,
Bulus ya kai Derbe sa’an nan kuma zuwa Listira, inda wani almajiri mai suna Timoti yake da zama, wanda mahaifiyarsa mutuniyar Yahuda ce kuma mai bi ce, amma mahaifinsa mutumin Hellenawa ne.
2 Of whom the brethren which were at Lystra and Iconium, reported well.
’Yan’uwa a Listira da Ikoniyum sun yi magana mai kyau ƙwarai a kansa.
3 Therefore Paul would that he should go forth with him, and tooke and circumcised him, because of ye Iewes, which were in those quarters: for they knewe all, that his father was a Grecian.
Bulus ya so ya ɗauke shi a tafiyar, saboda haka ya yi masa kaciya, domin Yahudawan da suke da zama a wurin, don duk sun san cewa mahaifinsa mutumin Hellenawa ne.
4 And as they went through the cities, they deliuered them the decrees to keepe, ordeined of the Apostles and Elders, which were at Hierusalem.
Yayinda suke tafiya daga gari zuwa gari, suka dinga ba da shawarwarin da manzanni da dattawa a Urushalima suka zartar domin mutane su kiyaye.
5 And so were the Churches stablished in the faith, and encreased in number daily.
Saboda haka ikkilisiyoyi suka ginu cikin bangaskiya suka kuma yi girma suka yi ta ƙaruwa kowace rana.
6 Nowe when they had gone throughout Phrygia, and the region of Galatia, they were forbidden of the holy Ghost to preache the worde in Asia.
Bulus da abokan tafiyarsa suka zazzaga dukan yankin Firjiya da Galatiya, don Ruhu Mai Tsarki ya hana su yin wa’azi a lardin Asiya.
7 Then came they to Mysia, and sought to go into Bithynia: but the Spirit suffered them not.
Da suka isa kan iyakar Misiya, suka yi ƙoƙari su shiga Bitiniya, amma Ruhun Yesu bai yarda musu ba.
8 Therefore they passed through Mysia, and came downe to Troas,
Saboda haka suka ratsa Misiya suka zo Toruwas.
9 Where a vision appeared to Paul in the night. There stoode a man of Macedonia, and prayed him, saying, Come into Macedonia, and helpe vs.
Da dare Bulus ya ga wahayin wani mutumin Makidoniya yana tsaye yana roƙonsa cewa, “Ka zo Makidoniya ka taimake mu.”
10 And after he had seene the vision, immediatly we prepared to goe into Macedonia, being assured that the Lord had called vs to preache the Gospel vnto them.
Bayan Bulus ya ga wahayin, muka shirya nan take mu tashi zuwa Makidoniya, mun tabbata cewa, Allah ya kira mu mu yi musu wa’azin bishara.
11 Then went we forth from Troas, and with a straight course came to Samothracia, and the next day to Neapolis,
Daga Toruwas muka tashi zuwa teku muka kuma shiga jirgin ruwa muka miƙe kai tsaye zuwa Samotiras, kashegari kuma muka nufi Neyafolis.
12 And from thence to Philippi, which is the chiefe citie in ye partes of Macedonia, and whose inhabitants came from Rome to dwell there, and we were in that citie abiding certaine dayes.
Daga can muka tafi Filibbi, wata babbar alkaryar Roma wadda kuma take babban birni a gundumar Makidoniya. Muka zauna a can kwanaki masu yawa.
13 And on the Sabbath day, we went out of the citie, besides a Riuer, where they were wont to pray: and we sate downe, and spake vnto the women, which were come together.
A Asabbaci, muka fita ƙofar birnin zuwa bakin kogi, inda muke tsammani za mu sami wurin yin addu’a. Muka zauna muka fara yin wa matan da suka taru a can magana.
14 And a certaine woman named Lydia, a seller of purple, of the citie of the Thyatirians, which worshipped God, heard vs: whose heart the Lord opened, that she attended vnto the things, which Paul spake.
Ɗaya daga cikin waɗanda suka saurare mu mace ce mai suna Lidiya, mai sayar da yadunan jan garura masu tsada daga birnin Tiyatira, mai yi wa Allah sujada. Ubangiji ya buɗe zuciyarta har ta karɓi saƙon Bulus.
15 And when she was baptized, and her houshold, she besought vs, saying, If ye haue iudged me to be faithfull to ye Lord, come into mine house, and abide there: and she constrained vs.
Da aka yi mata baftisma tare da iyalin gidanta, sai ta gayyace mu zuwa gidanta. Ta ce, “In kun amince ni mai bi ce cikin Ubangiji, sai ku zo ku sauka a gidana.” Sai ta kuwa rinjaye mu.
16 And it came to passe that as we went to prayer, a certaine maide hauing a spirit of diuination, mette vs, which gate her masters much vantage with diuining.
Wata rana muna tafiya zuwa wurin yin addu’a, sai muka sadu da wata baranya mai ruhun aljani mai duba. Takan samo wa mutanenta kuɗi da yawa, duban da take yi.
17 She followed Paul and vs, and cryed, saying, These men are the seruants of the most high God, which shewe vnto you the way of saluation.
Wannan yarinya kuwa ta bi Bulus da kuma sauranmu, tana ihu tana cewa, “Waɗannan mutane bayin Allah Mafi Ɗaukaka ne, suna sanar da ku hanyar ceto.”
18 And this did she many dayes: but Paul being grieued, turned about, and said to the spirit, I commaund thee in the Name of Iesus Christ, that thou come out of her. And he came out the same houre.
Ta yi ta faɗin haka har kwanaki masu yawa. A ƙarshe Bulus ya damu ƙwarai sai ya juya ya ce wa aljanin, “A cikin sunan Yesu Kiristi na umarce ka, ka rabu da ita!” Nan take aljanin ya rabu da ita.
19 Nowe when her masters sawe that the hope of their gaine was gone, they caught Paul and Silas, and drewe them into the market place vnto the Magistrates,
Da iyayengijin baranyar suka ga hanyar samun kuɗinsu ta toshe, sai suka kama Bulus da Sila suka ja su zuwa cikin kasuwa don su fuskanci hukuma.
20 And brought them to the gouernours, saying, These men which are Iewes, trouble our citie,
Sai suka kawo su a gaban alƙalai suka ce, “Waɗannan Yahudawa ne, suna kuma birkitar mana da gari,
21 And preache ordinances, which are not lawfull for vs to receiue, neither to obserue, seeing we are Romanes.
ta wurin koyar da al’adun da ba daidai ba ne mu Romawa mu karɓa ko mu aikata.”
22 The people also rose vp together against them, and the gouernours rent their clothes, and commanded them to be beaten with roddes.
Sai taron suka fāɗa wa Bulus da Sila gaba ɗaya, alƙalan kuwa suka yi umarni a tuɓe su a kuma yi musu dūka.
23 And when they had beaten them sore, they cast them into prison, commaunding the Iayler to keepe them surely.
Bayan an yi musu bulala sosai, sai aka jefa su cikin kurkuku, aka umarci mai gadin kurkukun yă tsare su da kyau.
24 Who hauing receiued such commandement, cast them into the inner prison, and made their feete fast in the stockes.
Da karɓan irin umarnan nan, sai ya sa su can cikin ɗakin kurkuku na ciki-ciki, kuma ya ɗaura ƙafafunsu a turu.
25 Nowe at midnight Paul and Silas prayed, and sung Psalmes vnto God: and the prisoners heard them.
Wajen tsakar dare Bulus da Sila suna addu’a suna rera waƙoƙi ga Allah, sauran’yan kurkuku kuwa suna sauraronsu.
26 And suddenly there was a great earthquake, so that the foundation of the prison was shaken: and by and by all the doores opened, and euery mans bands were loosed.
Ba zato ba tsammani sai aka yi wata babbar girgizar ƙasa har tushen ginin kurkukun ya jijjiga. Nan da nan sai duk ƙofofin kurkukun suka bubbuɗe, sarƙoƙin kowa kuma suka ɓaɓɓalle.
27 Then the keeper of the prison waked out of his sleepe, and when he sawe the prison doores open, he drewe out his sword and would haue killed himselfe, supposing the prisoners had bin fled.
Mai gadin kurkukun ya farka daga barci, sa’ad da ya ga ƙofofin kurkukun a buɗe, sai ya zāre takobinsa yana shirin kashe kansa domin ya ɗauka’yan kurkukun sun gudu.
28 But Paul cryed with a loude voyce, saying, Doe thy selfe no harme: for we are all here.
Amma Bulus ya yi ihu ya ce, “Kada ka yi wa kanka lahani! Dukanmu muna nan!”
29 Then he called for a light, and leaped in, and came trembling, and fell downe before Paul and Silas,
Mai gadin kurkukun ya kira a kawo fitilu, ya ruga ciki ya fāɗi yana rawan jiki a gaban Bulus da Sila.
30 And brought them out, and said, Syrs, what must I doe to be saued?
Sai ya fito da su waje ya kuma tambaye su ya ce, “Ranku yă daɗe, me zan yi domin in sami ceto?”
31 And they saide, Beleeue in the Lord Iesus Christ, and thou shalt be saued, and thine houshold.
Suka amsa suka ce, “Ka gaskata da Ubangiji Yesu, za ka sami ceto, kai da iyalinka.”
32 And they preached vnto him the worde of the Lord, and to all that were in the house.
Sa’an nan suka yi masa maganar Ubangiji shi da kuma dukan sauran da suke a gidansa.
33 Afterwarde he tooke them the same houre of the night, and washed their stripes, and was baptized with all that belonged vnto him, straigthway.
A wannan sa’a na daren, mai gadin kurkukun ya ɗauke su ya wanke musu raunukansu; nan take aka yi masa baftisma da dukan iyalinsa.
34 And when he had brought them into his house, he set meate before them, and reioyced that he with all his houshold beleeued in God.
Sai mai gadin kurkukun ya kawo su cikin gidansa ya ba su abinci; ya kuwa cika da murna don yă gaskata da Allah, shi da dukan iyalinsa.
35 And when it was day, the gouernours sent the sergeants, saying, Let those men goe.
Da gari ya waye, sai alƙalan suka aika ma’aikatansu wajen mai gadin kurkukun da umarni cewa, “Ka saki mutanen nan.”
36 Then the keeper of the prison tolde these woordes vnto Paul, saying, The gouerness haue sent to loose you: nowe therefore get you hence, and goe in peace.
Sai mai gadin kurkukun ya gaya wa Bulus cewa, “Alƙalai sun ba da umarni a sake ku kai da Sila. Yanzu sai ku tafi. Ku sauka lafiya.”
37 Then sayde Paul vnto them, After that they haue beaten vs openly vncodemned, which are Romanes, they haue cast vs into prison, and nowe would they put vs out priuily? nay verely: but let them come and bring vs out.
Amma Bulus ya ce wa ma’aikatan, “Sun yi mana dūka a fili ba tare da shari’a ba, ko da yake mu’yan ƙasar Roma ne, suka kuma jefa mu cikin kurkuku. Yanzu suna so su fitar da mu a ɓoye? A’a! Sai dai su zo da kansu su rako mu waje.”
38 And the sergeants tolde these woordes vnto the gouernours, who feared whe they heard that they were Romanes.
Sai ma’aikatan suka faɗa wa alƙalan wannan, da suka ji cewa Bulus da Sila Romawa ne, sai suka ji tsoro.
39 Then came they and praied them, and brought them out, and desired them to depart out of the citie.
Sai suka zo don su roƙe su, suka yi musu rakiya daga kurkukun, suna roƙonsu su bar birnin.
40 And they went out of the prison, and entred into the house of Lydia: and when they had seene the brethren, they comforted them, and departed.
Bayan Bulus da Sila suka fita daga kurkukun, sai suka tafi gidan Lidiya, inda suka sadu da’yan’uwa suka kuma ƙarfafa su. Sa’an nan suka tafi.