< Acts 13 >

1 There were also in the Church that was at Antiochia, certaine Prophets and teachers, as Barnabas, and Simeon called Niger, and Lucius of Cyrene, and Manahen (which had bin brought vp with Herod the Tetrarche) and Saul.
A ikkilisiyar da take a Antiyok akwai waɗansu annabawa da malamai. Barnabas, Siman wanda ake kira Baƙi, Lusiyus mutumin Sairin, Manayen (wanda aka goya tare da Hiridus mai mulki), da kuma Shawulu.
2 Nowe as they ministred to the Lord, and fasted, the holy Ghost said, Separate me Barnabas and Saul, for the worke whereunto I haue called them.
Yayinda suna cikin sujada da azumi ga Ubangiji, Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Ku keɓe mini Barnabas da Shawulu domin aikin da na kira su.”
3 Then fasted they and prayed, and layde their hands on them, and let them goe.
Saboda haka bayan suka yi azumi da addu’a, sai suka ɗibiya musu hannuwansu a kansu suka sallame su.
4 And they, after they were sent foorth of the holy Ghost, came downe vnto Seleucia, and from thence they sayled to Cyprus.
Sai su biyu da Ruhu Mai Tsarki ya aika suka gangara zuwa Selusiya suka shiga jirgin ruwa daga can zuwa Saifurus.
5 And when they were at Salamis, they preached the worde of God in the Synagogues of the Iewes: and they had also Iohn to their minister.
Da suka isa Salamis, sai suka yi shelar maganar Allah a majami’un Yahudawa. Yohanna yana tare da su a matsayin mai taimakonsu.
6 So when they had gone throughout the yle vnto Paphus, they found a certaine sorcerer, a false prophet, being a Iewe, named Bariesus,
Suka zaga dukan tsibirin har sai da suka kai Bafos. A can suka sadu da wani mutumin Yahuda mai sihiri, annabin ƙarya, mai suna Bar-Yesu,
7 Which was with the Deputie Sergius Paulus, a prudent man. He called vnto him Barnabas and Saul, and desired to heare the woorde of God.
wanda yake ma’aikacin muƙaddas Sergiyus Bulus ne. Muƙaddas ɗin kuwa mai azanci ne ƙwarai, ya sa aka kira Barnabas da Shawulu don yana so ya ji maganar Allah.
8 But Elymas, ye sorcerer (for so is his name by interpretation) withstoode them, and sought to turne away the Deputie from the faith.
Amma Elimas mai sihirin nan (domin ma’anar sunansa ke nan) ya yi hamayya da maganarsu ya kuma yi ƙoƙari ya juyar da muƙaddas ɗin daga bangaskiya.
9 Then Saul (which also is called Paul) being full of the holy Ghost, set his eyes on him,
Sai Shawulu, wanda kuma ake kira Bulus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya kafa wa Elimas ido ya ce,
10 And sayde, O full of all subtiltie and all mischiefe, the childe of the deuill, and enemie of all righteousnesse, wilt thou not cease to peruert the straight waies of the Lord?
“Kai ɗan Iblis ne abokin gāban dukan abin da yake daidai! Kana cike da kowane irin ruɗi da munafunci. Ba za ka daina karkata hanyoyin da suke daidai na Ubangiji ba?
11 Nowe therefore behold, the hand of the Lord is vpon thee, and thou shalt be blinde, and not see the sunne for a season. And immediately there fel on him a mist and a darknes; and he went about, seeking some to leade him by the hand.
Ga shi hannun Ubangiji yana gāba da kai. Za ka makance, kuma ba za ka ga rana ba har na wani lokaci.” Nan take, hazo da duhu suka sauko a kansa, ya yi ta lallubawa, yana neman wanda zai yi masa jagora.
12 Then the Deputie when he sawe what was done, beleeued, and was astonied at the doctrine of the Lord.
Sa’ad da muƙaddas ɗin ya ga abin da ya faru, sai ya ba da gaskiya, gama ya yi mamaki a kan da koyarwa game Ubangiji.
13 Nowe when Paul and they that were with him were departed by shippe from Paphus, they came to Perga a citie of Pamphylia: then Iohn departed from them, and returned to Hierusalem.
Bulus da abokan tafiyarsa suka tashi daga Bafos a jirgin ruwa zuwa Ferga a Famfiliya inda Yohanna ya bar su ya koma Urushalima.
14 But when they departed from Perga, they came to Antiochia a citie of Pisidia, and went into the Synagogue on ye Sabbath day, and sate downe.
Daga Ferga kuwa suka ci gaba zuwa Antiyok na Fisidiya. A ranar Asabbaci sai suka shiga majami’a suka zauna.
15 And after the lecture of the Law and Prophets, the rulers of ye Synagogue sent vnto them, saying, Ye men and brethren, if ye haue any word of exhortation for the people, say on.
Bayan an yi karatu daga cikin Doka, da kuma Annabawa, sai shugabannin majami’ar suka aika musu suka ce, “’Yan’uwa, in kuna da wani saƙon ƙarfafawa domin jama’a, sai ku yi.”
16 Then Paul stoode vp and beckened with the hand, and sayde, Men of Israel, and yee that feare God, hearken.
Yana miƙewa tsaye, sai Bulus ya yi musu alama da hannu ya ce, “Mutanen Isra’ila da kuma ku Al’ummai da kuke wa Allah sujada, ku saurare ni!
17 The God of this people of Israel chose our fathers, and exalted the people when they dwelt in the land of Egypt, and with an high arme brought them out thereof.
Allahn mutanen Isra’ila ya zaɓi kakanninmu; ya kuma sa mutanen suka yi bunkasa yayinda suke zama a ƙasar Masar, da iko mai girma ya fitar da su daga ƙasar,
18 And about the time of fourtie yeeres, suffered he their maners in the wildernesse.
ya kuma jure da halinsu har shekara arba’in a cikin hamada,
19 And he destroied seuen nations in the land of Chanaan, and deuided their lad to them by lot.
ya tumɓuke ƙasashe bakwai a Kan’ana ya kuma ba da ƙasarsu gādo ga mutanensa.
20 Then afterward he gaue vnto them Iudges about foure hundreth and fiftie yeeres, vnto the time of Samuel the Prophet.
Dukan wannan ya ɗauki kusan shekaru 450. “Bayan wannan, Allah ya ba su alƙalai har zuwa zamanin annabi Sama’ila.
21 So after that, they desired a King, and God gaue vnto them Saul, the sonne of Cis, a man of ye tribe of Beniamin, by the space of fourty yeres.
Sa’an nan mutanen suka nemi a ba su sarki, Allah kuwa ya ba su Shawulu ɗan Kish, na kabilar Benyamin, wanda ya yi mulki shekaru arba’in.
22 And after he had taken him away, he raised vp Dauid to be their King, of whom he witnessed, saying, I haue found Dauid the sonne of Iesse, a man after mine owne heart, which will doe all things that I will.
Bayan an kau da Shawulu, sai ya naɗa Dawuda ya zama sarkinsu. Ya kuma yi shaida game da shi cewa, ‘Na sami Dawuda ɗan Yesse, mutum ne da nake so a zuciyata; shi zai aikata dukan abin da nake so.’
23 Of this mans seede hath God according to his promise raised vp to Israel, ye Sauiour Iesus:
“Daga zuriyar mutumin nan ne Allah ya kawo wa Isra’ila Mai Ceto Yesu, kamar yadda ya yi alkawari.
24 When Iohn had first preached before his coming the baptisme of repentance to all the people of Israel.
Kafin zuwan Yesu, Yohanna ya yi wa’azin tuba da baftisma ga dukan mutanen Isra’ila.
25 And when Iohn had fulfilled his course, he saide, Whom ye thinke that I am, I am not he: but beholde, there commeth one after me, whose shooe of his feete I am not worthy to loose.
Yayinda Yohanna yake kammala aikinsa ya ce, ‘Wa kuke tsammani ni nake? Ba ni ne shi ba. A’a, amma yana zuwa bayana, wanda ko takalmansa ma ban isa in kunce ba.’
26 Yee men and brethren, children of the generation of Abraham, and whosoeuer among you feareth God, to you is the woorde of this saluation sent.
“Ya ku’yan’uwa,’ya’yan Ibrahim, da ku kuma Al’ummai masu tsoron Allah, a gare mu ne fa aka aiko wannan saƙon ceto.
27 For the inhabitants of Hierusalem, and their rulers, because they knewe him not, nor yet the woordes of the Prophets, which are read euery Sabbath day, they haue fulfilled them in condemning him.
Mutanen Urushalima da masu mulkinsu ba su gane da Yesu ba, duk da haka cikin hukunta shi suka cika kalmomin annabawan da ake karantawa kowane Asabbaci.
28 And though they found no cause of death in him, yet desired they Pilate to kill him.
Ko da yake ba su same shi da wani dalilin da ya kai ga hukuncin kisa ba, suka roƙi Bilatus yă sa a kashe shi.
29 And when they had fulfilled all things that were written of him, they tooke him downe from the tree, and put him in a sepulchre.
Sa’ad da suka aikata duk abin da aka rubuta game da shi, sai suka saukar da shi daga itacen suka kuma sa shi a kabari.
30 But God raised him vp from the dead.
Amma Allah ya tashe shi daga matattu,
31 And hee was seene many dayes of them, which came vp with him from Galile to Hierusalem, which are his witnesses vnto the people.
kuma kwanaki da yawa waɗanda suka yi tafiya tare da shi daga Galili zuwa Urushalima suka gan shi. Su ne yanzu shaidu ga mutanenmu.
32 And we declare vnto you, that touching the promise made vnto the fathers,
“Muna gaya muku labari mai daɗi cewa abin da Allah ya yi wa kakanninmu alkawari,
33 God hath fulfilled it vnto vs their children, in that he raised vp Iesus, euen as it is written in the seconde Psalme, Thou art my Sonne: this day haue I begotten thee.
ya cika mana, mu zuriyarsu, ta wurin tā da Yesu daga matattu. Kamar yadda yake a rubuce a cikin Zabura ta biyu cewa, “‘Kai Ɗana ne, yau na zama Uba a gare ka.’
34 Nowe as concerning that he raised him vp from the dead, no more to returne to corruption, he hath said thus, I wil giue you the holy things of Dauid, which are faithfull.
Gaskiyar cewa Allah ya tā da shi daga matattu, a kan ba zai taɓa ruɓewa ba, an faɗe shi a cikin waɗannan kalmomi. “‘Zan ba ku tsarki da kuma tabbatattun albarkun da na yi wa Dawuda alkawari.’
35 Wherefore hee sayeth also in another place, Thou wilt not suffer thine Holy one to see corruption.
Haka kuma aka faɗa a wani wuri. “‘Ba za ka yarda Mai Tsarkinka ya ruɓa ba.’
36 Howbeit, Dauid after hee had serued his time by the counsell of God, hee slept, and was laid with his fathers, and sawe corruption.
“Gama sa’ad da Dawuda ya gama hidimar nufin Allah a zamaninsa, sai ya yi barci; aka binne shi tare da kakanninsa jikinsa kuwa ya ruɓe.
37 But he whom God raised vp, sawe no corruption.
Amma wanda Allah ya tā da daga matattu bai ruɓa ba.
38 Be it knowen vnto you therefore, men and brethren, that through this man is preached vnto you the forgiuenesse of sinnes.
“Saboda haka,’yan’uwana, ina so ku san cewa ta wurin Yesu ana sanar muku da gafarar zunubi.
39 And from al things, from which ye could not be iustified by the Law of Moses, by him euery one that beleeueth, is iustified.
Ta wurinsa kowa da ya gaskata an kuɓutar da shi daga dukan abin da Dokar Musa ba tă iya kuɓutar ba.
40 Beware therefore lest that come vpon you, which is spoken of in the Prophets,
Ku lura kada abubuwan da annabawa suka faɗa su faru muku.
41 Behold, ye despisers, and wonder, and vanish away: for I woorke a woorke in your daies, a woorke which yee shall not beleeue, if a man would declare it you.
“‘Ku duba, ku masu ba’a, ku yi mamaki, ku hallaka, gama zan yi wani abu a zamaninku da ba za ku taɓa gaskatawa ba ko da wani ya gaya muku.’”
42 And when they were come out of the Synagogue of the Iewes, the Gentiles besought, that they woulde preach these woordes to them the next Sabbath day.
Bulus da Barnabas suna fita daga majami’ar ke nan, sai mutane suka gayyace su su ƙara yin maganan nan a kan waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci mai zuwa.
43 Nowe when the congregation was dissolued, many of the Iewes and Proselytes that feared God, followed Paul and Barnabas, which spake to them, and exhorted them to continue in the grace of God.
Da aka sallami jama’a, Yahudawa da yawa da kuma waɗanda suka tuba suka shiga Yahudanci masu ibada suka bi Bulus da Barnabas, waɗanda suka yi magana musu suka kuma ƙarfafa su su ci gaba a cikin alherin Allah.
44 And ye next Sabbath day came almost the whole citie together, to heare the worde of God.
A ranar Asabbaci na biye kusan dukan birnin suka taru don su ji maganar Ubangiji.
45 But when the Iewes saw the people, they were full of enuie, and spake against those things, which were spoken of Paul, contrarying them, and railing on them.
Sa’ad da Yahudawa suka ga taron mutanen, sai suka cika da kishi suka yi ta munanan maganganu a kan abin da Bulus yake faɗi.
46 Then Paul and Barnabas spake boldly, and sayde, It was necessarie that the woorde of God shoulde first haue beene spoken vnto you: but seeing yee put it from you, and iudge your selues vnworthie of euerlasting life, loe, we turne to the Gentiles. (aiōnios g166)
Sai Bulus da Barnabas suka amsa musu gabagadi, suka ce, “Ya zama mana dole mu yi muku maganar Allah da farko. Da yake kun ƙi ta ba ku kuma ga kun cancanci rai madawwami ba, to, za mu juya ga Al’ummai. (aiōnios g166)
47 For so hath the Lord commanded vs, saying, I haue made thee a light of the Gentiles, that thou shouldest be the saluation vnto the end of the world.
Gama abin da Allah ya umarce mu ke nan cewa, “‘Na sa ka zama haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.’”
48 And when the Gentiles heard it, they were glad, and glorified the woorde of the Lord: and as many as were ordeined vnto eternall life, beleeued. (aiōnios g166)
Sa’ad da Al’ummai suka ji haka, sai suka yi farin ciki suka ɗaukaka maganar Ubangiji; kuma duk waɗanda aka zaɓa don samun rai madawwami, suka gaskata. (aiōnios g166)
49 Thus the worde of the Lord was published throughout the whole countrey.
Maganar Ubangiji kuwa ta bazu a dukan yankin.
50 But the Iewes stirred certaine deuoute and honourable women, and the chiefe men of the citie, and raised persecution against Paul and Barnabas, and expelled them out of their coastes.
Amma Yahudawa suka zuga waɗansu mata masu tsoron Allah masu martaba da kuma waɗansu maza masu matsayi a gari. Suka tā da tsanani ga Bulus da Barnabas, suka kore su daga yankinsu.
51 But they shooke off the dust of their feete against them, and came vnto Iconium.
Saboda haka suka karkaɗe ƙurar ƙafafunsu don shaidar a kansu suka kuwa tafi Ikoniyum.
52 And the disciples were filled with ioy, and with the holy Ghost.
Masu bi kuwa suka cika da farin ciki da kuma Ruhu Mai Tsarki.

< Acts 13 >