< Acts 12 >

1 Nowe about that time, Herod the King stretched forth his hands to vexe certaine of the Church,
Kusan a wannan lokaci ne Sarki Hiridus ya kama waɗansu da suke na ikkilisiya, da niyya ya tsananta musu.
2 And he killed Iames the brother of Iohn with the sword.
Ya sa aka kashe Yaƙub, ɗan’uwan Yohanna, da takobi.
3 And when he sawe that it pleased the Iewes, he proceeded further, to take Peter also (then were the dayes of vnleauened bread.)
Sa’ad da ya ga wannan ya faranta wa Yahudawa rai, sai ya kama Bitrus shi ma. Wannan ya faru kwanakin Bikin Burodi Marar Yisti.
4 And when he had caught him, he put him in prison, and deliuered him to foure quaternions of souldiers to be kept, intending after the Passeouer to bring him foorth to the people.
Bayan ya kama shi, sai ya sa shi a kurkuku, ya danƙa shi a hannun soja hurhuɗu kashi huɗu, don su yi gadinsa. Hiridus ya yi niyyar ya yi masa shari’a a gaban mutane bayan Bikin Ƙetarewa.
5 So Peter was kept in prison, but earnest prayer was made of ye Church vnto God for him.
Saboda haka aka tsare Bitrus a kurkuku, amma ikkilisiya ta nace da addu’a ga Allah dominsa.
6 And when Herod woulde haue brought him out vnto the people, the same night slept Peter betweene two souldiers, bound with two chaines, and the keepers before the doore, kept the prison.
A daren da in gari ya waye da Hiridus yake niyyar kawo shi domin a yi masa shari’a, Bitrus yana barci tsakanin sojoji biyu, daure da sarƙoƙi biyu, masu gadi kuma suna bakin ƙofa.
7 And behold the Angel of the Lord came vpon them, and a light shined in the house, and he smote Peter on the side, and raysed him vp, saying, Arise quickely. And his chaines fell off from his handes.
Ba zato ba tsammani sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana haske kuma ya haskaka a ɗakin. Ya bugi Bitrus a gefe ya kuma tashe shi ya ce, “Maza, ka tashi!” Sarƙoƙin kuwa suka zube daga hannuwansa.
8 And the Angel saide vnto him, Girde thy selfe, and binde on thy sandales. And so he did. Then he said vnto him, Cast thy garment about thee, and follow me.
Sa’an nan mala’ikan ya ce masa, “Ka sa rigunarka da takalmanka.” Bitrus kuwa ya sa. Mala’ikan ya faɗa masa cewa, “Ka yafa mayafinka ka bi ni.”
9 So Peter came out and followed him, and knewe not that it was true, which was done by the Angel, but thought he had seene a vision.
Bitrus ya bi shi suka fita kurkukun, amma bai ma san cewa abin da mala’ikan yake yi tabbatacce ne ba; yana tsammani wahayi yake gani.
10 Nowe when they were past the first and the second watch, they came vnto the yron gate, that leadeth vnto the citie, which opened to them by it owne accord, and they went out, and passed through one streete, and by and by the Angel departed from him.
Suka wuce masu gadi na fari da na biyu, suka kuma isa ƙofar ƙarfe ta shiga birni. Ƙofar kuwa ta buɗe musu da kanta, suka kuma wuce. Sa’ad da suka yi tafiya tsawon wani titi, nan take mala’ikan ya bar shi.
11 And when Peter was come to himselfe, he said, Nowe I know for a trueth, that the Lord hath sent his Angel, and hath deliuered me out of the hand of Herod, and from all the wayting for of the people of the Iewes.
Sai Bitrus ya dawo hankalinsa ya ce, “Yanzu na sani ba shakka Ubangiji ne ya aiki mala’ikansa yă cece ni daga hannun Hiridus da kuma dukan mugun fatan Yahudawa.”
12 And as he considered the thing, he came to the house of Marie, the mother of Iohn, whose surname was Marke, where many were gathered together, and prayed.
Da ya gane haka, sai ya tafi gidan Maryamu uwar Yohanna, wanda ake kuma kira Markus, inda mutane da yawa suka taru suna addu’a.
13 And when Peter knocked at the entrie doore, a maide came foorth to hearken, named Rhode,
Bitrus ya ƙwanƙwasa ƙofar waje, sai wata mai aiki a gidan da ake kira Roda ta zo tă ji ko wane ne.
14 But when she knew Peters voyce, she opened not the entrie doore for gladnesse, but ranne in, and tolde howe Peter stood before the entrie.
Da ta gane muryar Bitrus, ta cika da murna ta gudu ta koma ba tare da ta buɗe ƙofar ba, sai ta koma a guje ta ce da ƙarfi, “Ga Bitrus a bakin ƙofa!”
15 But they said vnto her, Thou art mad. Yet she affirmed it constantly, that it was so. Then said they, It is his Angel.
Sai suka ce mata, “Kina hauka.” Da ta nace cewa shi ne, sai suka ce, “To, lalle, mala’ikansa ne.”
16 But Peter continued knocking, and when they had opened it, and sawe him, they were astonied.
Amma Bitrus ya yi ta ƙwanƙwasawa. Da suka buɗe ƙofar suka kuma gan shi, sai suka yi mamaki.
17 And he beckened vnto them with the hand, to hold their peace, and told them how the Lord had brought him out of the prison. And he saide, Goe shewe these things vnto Iames and to the brethren: and he departed and went into an other place.
Bitrus ya yi musu alama da hannunsa su yi shiru sai ya bayyana yadda Ubangiji ya fitar da shi daga kurkuku. Ya ce, “Ku gaya wa Yaƙub da kuma’yan’uwa game da wannan,” sa’an nan ya tashi ya tafi wani wuri.
18 Nowe assoone as it was day, there was no small trouble among the souldiers, what was become of Peter.
Da safe, hargitsin da ya tashi tsakanin sojojin ba ƙarami ba ne, a kan abin da ya sami Bitrus.
19 And when Herod had sought for him, and found him not, he examined the keepers, and commanded them to be led to be punished. And he went downe from Iudea to Cesarea, and there abode.
Bayan Hiridus ya neme shi bai same shi ba, sai ya tuhumi masu gadin, ya kuma ba da umarni a kashe su. Sa’an nan Hiridus ya tashi daga Yahudiya ya tafi Kaisariya ya kuma yi’yan kwanaki a can.
20 Then Herod was angrie with them of Tyrus and Sidon, but they came all with one accord vnto him, and perswaded Blastus the Kings Chamberlaine, and they desired peace, because their countrey was nourished by the Kings land.
Yana da rashin jituwa da mutanen Taya da na Sidon; sai suka haɗa kai suka nemi ganawa da shi. Bayan suka sami goyon bayan Bilastus, amintaccen bawan sarki, sai suka nemi salama, domin sun dogara ga ƙasar sarkin don samun abincinsu.
21 And vpon a day appointed, Herod arayed himselfe in royall apparell, and sate on the iudgement seate, and made an oration vnto them.
A ranar da aka shirya Hiridus, sanye da kayan sarautarsa, ya zauna a gadon sarautarsa ya kuma ya wa mutanen jawabi.
22 And the people gaue a shoute, saying, The voyce of God, and not of man.
Suka tā da murya suka ce, “Wannan muryar wani allah ne, ba ta mutum ba.”
23 But immediatly the Angel of the Lord smote him, because he gaue not glorie vnto God, so that he was eaten of wormes, and gaue vp the ghost.
Nan take, domin Hiridus bai yi wa Allah yabo ba, wani mala’ikan Ubangiji ya buge shi, tsutsotsi kuwa suka cinye shi ya kuma mutu.
24 And the worde of God grewe, and multiplied.
Amma maganar Allah ta ci gaba da ƙaruwa ta kuma bazu.
25 So Barnabas and Saul returned from Hierusalem, when they had fulfilled their office, and tooke with them Iohn, whose surname was Marke.
Sa’ad da Barnabas da Shawulu suka kammala aikinsu, sai suka komo daga Urushalima, tare da Yohanna, wanda ake kira Markus.

< Acts 12 >