< 2 Peter 2 >
1 Bvt there were false prophets also among the people, euen as there shalbe false teachers among you: which priuily shall bring in damnable heresies, euen denying the Lord, that hath bought them, and bring vpon themselues swift damnation.
Annabawan karya sun zo ga mutane, hakannan kuma malaman karya suma sun zo. A asirce za su zo maku da karkatacciyar koyarwa mai hallakarwa, su kuma yi musun sanin Ubangiji da ya fanshe su. Su na jawowa kansu hallaka da sauri.
2 And many shall follow their destructions, by whom the way of trueth shalbe euil spoken of,
Da yawa za su bi gurbinsu, kuma ta wurinsu za a sabawa sahihiyar gaskiya.
3 And through couetousnes shall they with fained words make marchandise of you, whose condemnation long since resteth not, and their destruction slumbreth not.
Ta wurin hadama za su ribace ku ta wurin maganganunsu na yaudara. Hallakarsu ba za ta yi jinkiri ba; hukuncinsu na nan tafe.
4 For if God spared not the Angels that had sinned, but cast them downe into hell, and deliuered them into chaines of darkenes, to be kept vnto damnation: (Tartaroō )
Allah bai kebe mala'ikkun da suka yi zunubi ba. Maimakon haka ya tura su a cikin bakin duhun jahannama daure da sarkoki, har ya zuwa ranar shari'a. (Tartaroō )
5 Neither hath spared the olde worlde, but saued Noe the eight person a preacher of righteousnesse, and brought in the flood vpon the world of the vngodly,
Hakan nan kuma bai kebe duniya ta zamanin da ba. Maimakon haka, ya kebe Nuhu, wanda yake wa'azin adalci, tare da mutane bakwai, lokacin da ya kawo ambaliyar ruwan Tsufana a fuskar duniyar marasa bin Allah.
6 And turned the cities of Sodom and Gomorrhe into ashes, condemned them and ouerthrewe them, and made them an ensample vnto them that after should liue vngodly,
Sa'annan Allah ya kone biranen Sadoma da Gomrata da wuta ya maishe su toka, wannan ya zama misalin abin da zai faru da marasa ibada.
7 And deliuered iust Loth vexed with the vncleanly conuersation of the wicked:
Amma ga adalinnan Lutu, wanda ya zaku a ransa ta wurin miyagun halayen mutanen, Ubangiji kuwa ya cece shi.
8 (For he being righteous, and dwelling among them, in seeing and hearing, vexed his righteous soule from day to day with their vnlawfull deedes.)
Ga wannan mutum mai adalci, wanda yayi zama a cikinsu kowace rana ransa na baci, domin abin da yake gani yake kuma ji.
9 The Lord knoweth to deliuer the godly out of tentation, and to reserue the vniust vnto the day of iudgement vnder punishment.
Saboda haka Allah ya san yadda zai ceci masu adalci daga gwaji, da yadda kuma zai kama masu rashin adalci da hukunci a ranar shari'a.
10 And chiefly them that walke after the flesh, in the lust of vncleannesse, and despise gouernement, which are bolde, and stand in their owne conceite, and feare not to speake euill of them that are in dignitie.
Wannan kuwa musamman gaskiya ce ga wadanda suka ci gaba da ayyuka na jiki suka kuma raina masu mulki. Suna da taurin kai da kuma yin ganin dama. Ba sa tsoron sabo ga wadanda aka daukaka.
11 Where as the Angels which are greater both in power and might, giue not railing iudgement against them before the Lord.
Ko da shike mala'iku suna da karfi da iko fiye da su, amma basu kawo karar batanci a kansu a gaban Ubangiji ba.
12 But these, as naturall brute beasts, led with sensualitie and made to be taken, and destroyed, speake euill of those things which they know not, and shall perish through their owne corruption,
Amma wadannan dabbobi marassa tunani an yi su ne musamman domin a kama a yanka. Suna sabawa abin da ba su sani ba. Zasu halaka.
13 And shall receiue the wages of vnrighteousnes, as they which count it pleasure dayly to liue deliciously. Spottes they are and blottes, deliting them selues in their deceiuings, in feasting with you,
Za su sami sakamakon mugun aikinsu. Suna tunanin yin nishadi da rana abin annashuwa ne. Su kan su tababbu ne. Suna jin dadin ayyukansu na yaudara yayin da suke liyafa tare da ku.
14 Hauing eyes full of adulterie, and that can not cease to sinne, beguiling vnstable soules: they haue heartes exercised with couetousnesse, they are the children of curse:
Suna da idanun sha'awace sha'awacen mata mazinata; ba sa koshi da aikata zunubi. Suna rinjayar wandanda ba su da tsayayyan hankali zuwa ga munanan ayyuka, kuma sun kafa zukatansu ga hadama, su 'ya'yan la'ana ne!
15 Which forsaking the right way, haue gone astray, folowing the way of Balaam, the sonne of Bosor, which loued the wages of vnrighteousnes.
Sun bar bin hanyar gaskiya. Sun bijire kuma sun bi hanyar Bal'amu dan Be'or wanda yake kaunar ribar rashin adalci.
16 But he was rebuked for his iniquitie: for the dumme beast speaking with mans voyce, forbade the foolishnesse of the Prophet.
Amma ya karbi tsautawa domin zunubinsa. Jaki ma da baya magana ya tsauta wa haukan annabin da muryar dan adam.
17 These are welles without water, and cloudes caried about with a tempest, to whome the blacke darkenes is reserued for euer. ()
Wadannan mutane suna kamar mabulbullai da babu ruwa. suna nan kamar gizagizai da iska ke korawa. Duhu mai tsanani yana jiransu.
18 For in speaking swelling wordes of vanitie, they beguile with wantonnesse through the lusts of the flesh them that were cleane escaped from them which are wrapped in errour,
Su masu babatu ne da girman kai. suna yadaurar mutane ta wurin sha'awowin jiki. Suna yaudarar mutane da suke kokarin su tsere daga wadanda suke rayuwa cikin kuskure.
19 Promising vnto them libertie, and are themselues the seruants of corruption: for of whomsoeuer a man is ouercome, euen vnto the same is he in bondage.
Suna masu alkawarin yanci, amma su da kan su bayi ne ga zunubi. Domin mutum bawa ne ga duk abinda ya rinjaye shi.
20 For if they, after they haue escaped from the filthinesse of the world, through the acknowledging of the Lord, and of the Sauiour Iesus Christ, are yet tangled againe therein, and ouercome, the latter ende is worse with them then the beginning.
Duk wanda ya kubuta daga shashanci na duniya ta wurin sanin Ubangiji da mai Ceto Yesu Almasihu, sa'annan ya koma cikin shashaci, yanayinsu na karshe ya zama da muni fiye da na farkon.
21 For it had bene better for them, not to haue acknowledged the way of righteousnes, then after they haue acknowledged it, to turne from the holy commandement giuen vnto them.
Da ma zai fi masu kada su san hanyar adalci da su san ta amma sa'annan su juya daga ka'ida mai tsarki wanda aka damka masu.
22 But it is come vnto them, according to the true Prouerbe, The dogge is returned to his owne vomit: and, The sowe that was washed, to the wallowing in the myre.
Wannan karin magana ya zama gaskiya a kan su: “Kare ya dawo yana lashe amansa. Aladen da akayi masa wanka ya koma cikin tabo.”