< 2 Kings 8 >

1 Then spake Elisha vnto the woman, whose sonne he had restored to life, saying, Vp, and goe, thou, and thine house, and soiourne where thou canst soiourne: for the Lord hath called for a famine, and it commeth also vpon the land seuen yeeres.
To, Elisha ya riga ya ce wa matan da ya tā da ɗanta daga matattu, “Ki kwashe iyalinki ku tafi duk inda za ku tafi na ɗan lokaci, domin Ubangiji ya sa a yi yunwa na shekara bakwai a ƙasar.”
2 And the woman arose, and did after the saying of the man of God, and went both shee and her housholde and soiourned in the lande of the Philistims seuen yeeres.
Sai macen ta yi kamar yadda mutumin Allah ya faɗa. Ita da iyalinta suka tafi ƙasar Filistiyawa suka zauna shekara bakwai.
3 And at the seuen yeeres ende, the woman returned out of the lande of the Philistims, and went out to call vpon the King for her house and for her land.
A ƙarshen shekara bakwai ɗin sai ta dawo daga ƙasar Filistiyawa, ta kuma tafi wajen sarki ta roƙa a mayar mata da gidanta da filinta.
4 And the King talked with Gehazi the seruant of the man of God, saying, Tell mee, I pray thee, all the great actes, that Elisha hath done.
Sarki kuwa yana magana da Gehazi bawan mutumin Allah, ya ce masa, “Ba ni labarin dukan abubuwan banmamakin da Elisha ya yi.”
5 And as he told the King, howe he had restored one dead to life, behold, the woman, whose sonne he had raised to life, called vpon the King for her house and for her land. Then Gehazi sayd, My lorde, O King, this is the woman, and this is her sonne, whom Elisha restored to life.
A sa’ad da Gehazi yana cikin ba shi labarin yadda Elisha ya tā da matacce ke nan, sai ga macen da aka tā da ɗanta daga matattu ta shigo don tă roƙi sarki yă mayar mata da gidanta da filinta. Gehazi ya ce, “Ranka yă daɗe, ai, ga macen, ga kuma ɗan da Elisha ya tā da daga matattu.”
6 And when the King asked the woman, shee told him: so the King appoynted her an Eunuch, saying, Restore thou all that are hers, and all the fruites of her landes since the day shee left the land, euen vntill this time.
Sarki ya tambayi macen game da al’amarin, ita kuwa ta faɗa masa. Sa’an nan ya sa wani hafsa yă dubi damuwarta ya kuma ce masa, “Ka mayar mata kome da yake nata, haɗe da dukan kuɗin da aka samo daga filin, daga ranar da ta bar ƙasar har yă zuwa yanzu.”
7 Then Elisha came to Damascus, and Ben-hadad the King of Aram was sicke, and one told him, saying, The man of God is come hither.
Sai Elisha ya tafi Damaskus, Ben-Hadad mutumin Aram kuwa yana ciwo. Sa’ad da aka faɗa wa sarki, “Mutumin Allah ya hauro tun daga can zuwa nan,”
8 And the king sayd vnto Hazael, Take a present in thine hande, and goe meete the man of God, that thou mayest inquire of ye Lord by him, saying, Shall I recouer of this disease?
sai ya ce wa Hazayel, “Ɗauki wannan tare da kai ka tafi ka taryi mutumin Allah. Ka nemi nufin Ubangiji ta wurinsa; ka tambaye shi, ‘Zan warke daga ciwon nan?’”
9 So Hazael went to meete him, and tooke the present in his hand, and of euery good thing of Damascus, euen the burden of fourtie camels, and came and stood before him, and sayde, Thy sonne Ben-hadad King of Aram hath sent me to thee, saying, Shall I recouer of this disease?
Sai Hazayel ya tafi taryen Elisha, ya ɗauka kyauta na kowane irin kaya masu kyau na Damaskus tare da shi a raƙuma arba’in. Ya shiga ya tsaya a gaban Elisha ya ce, “Ɗanka Ben-Hadad na Aram ya aike ni in tambaye ka, ‘Zan warke daga ciwon nan?’”
10 And Elisha sayd to him, Goe, and say vnto him, Thou shalt recouer: howbeit the Lord hath shewed me, that he shall surely dye.
Elisha ya amsa ya ce, “Je ka ce masa, ‘Ba shakka za ka warke’; ammaUbangiji ya nuna mini cewa ba shakka zai mutu.”
11 And hee looked vpon him stedfastly, till Hazael was ashamed, and the man of God wept.
Sai ya zuba wa Hazayel ido har sai da Hazayel ya ji kunya. Sa’an nan mutumin Allah ya fara kuka.
12 And Hazael sayde, Why weepeth my lord? And he answered, Because I knowe the euill that thou shalt do vnto the children of Israel: for their strong cities shalt thou set on fire, and their yong men shalt thou slay with the sworde, and shalt dash their infantes against the stones, and rent in pieces their women with child.
Hazayel ya ce masa, “Me ya sa ranka yă daɗe yake kuka?” Elisha ya amsa, “Domin na san illar da za ka yi wa Isra’ilawa. Za ka ƙona biranensu masu katanga, ka karkashe majiya ƙarfinsu da takobi, ka fyaffyaɗe ƙananan yaransu da ƙasa, ka tsattsage matansu masu ciki.”
13 Then Hazael said, What? is thy seruant a dog, that I should doe this great thing? And Elisha answered, The Lord hath shewed mee, that thou shalt be King of Aram.
Hazayel ya ce, “Yaya bawanka, wanda yake kare kawai, zai iya aikata wannan irin abu?” Elisha ya ce, “Ubangiji ya nuna mini cewa za ka zama sarkin Aram.”
14 So he departed from Elisha, and came to his master, who said to him, What saide Elisha to thee? And he answered, Hee tolde mee that thou shouldest recouer.
Sai Hazayel ya rabu da Elisha ya koma wurin maigidansa. Da Ben-Hadad ya yi tambaya, “Me Elisha ya ce maka?” Sai Hazayel ya amsa, “Ya faɗa mini cewa tabbatacce za ka warke.”
15 And on the morow he tooke a thick cloth and dipt in it water, and spread it on his face, and hee dyed: and Hazael reigned in his stead.
Amma kashegari sai ya ɗauki tsumma mai kauri, ya jiƙa shi, ya rufe fuskar sarki da shi, har sai da sarki ya mutu. Sai Hazayel ya gāje shi a matsayin sarki.
16 Now in the fift yere of Ioram ye sonne of Ahab King of Israel, and of Iehoshaphat King of Iudah, Iehoram the sonne of Iehoshaphat King of Iudah began to reigne.
A shekara ta biyar ta mulkin Yoram ɗan Ahab, sarkin Isra’ila, sa’ad da Yehoshafat yake sarautar Yahuda, Yoram ɗan Yehoshafat, ya fara mulkinsa a matsayin sarkin Yahuda.
17 He was two and thirtie yere olde, when he began to reigne: and hee reigned eight yeere in Ierusalem.
Yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki na tsawon shekara takwas a Urushalima.
18 And hee walked in the wayes of the Kings of Israel, as did the house of Ahab: for the daughter of Ahab was his wife, and hee did euill in the sight of the Lord.
Ya bi gurbin sarakunan Isra’ila, yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya yi mugunta a gaban Ubangiji.
19 Yet the Lord would not destroy Iudah, for Dauid his seruants sake, as he had promised him to giue him a light, and to his children for euer.
Duk da haka, saboda bawansa Dawuda, Ubangiji bai ragargaza Yahuda ba. Ya riga ya yi alkawari zai bar wa Dawuda magāji har abada.
20 In those dayes Edom rebelled from vnder the hand of Iudah, and made a King ouer themselues.
A kwanakin Yoram, Edom ta yi wa Yahuda tawaye, ta naɗa wa kanta sarki.
21 Therefore Ioram went to Zair, and all his charets with him, and he arose by night, and smote the Edomites which were about him with the captains of the charets, and the people fled into their tents.
Saboda haka Yehoram ya tafi Zayir da dukan kekunan yaƙinsa. Sojojin Edom suka kewaye shi a can, amma da dare sai Yoram ya ɓarke ya gudu, sojojinsa kuma suka watse zuwa gidajensu.
22 So Edom rebelled from vnder the hand of Iudah vnto this day. then Libnah rebelled at that same time.
Har yă zuwa yau, Edom tana yi wa Yahuda tawaye. A lokaci ɗaya ne Libna ma ta yi tawaye.
23 Concerning the rest of the actes of Ioram and all that hee did, are they not written in the booke of the Chronicles of the Kings of Iudah?
Game da waɗansu abubuwan da suka faru a zamanin Yoram, ba suna a rubuce a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda ba?
24 And Ioram slept with his fathers, and was buried with his fathers in the citie of Dauid. And Ahaziah his sonne reigned in his stead.
Yoram ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda. Sai Ahaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
25 In the twelft yere of Ioram the sonne of Ahab King of Israel did Ahaziah the sonne of Iehoram King of Iudah begin to reigne.
A shekara ta goma sha biyu ta Yoram ɗan Ahab, sarkin Isra’ila, Ahaziya ɗan Yehoram, sarkin Yahuda ya fara mulki.
26 Two and twentie yeere olde was Ahaziah when he began to reigne, and he reigned one yere in Ierusalem, and his mothers name was Athaliah the daughter of Omri King of Israel.
Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ɗaya. Sunan mahaifiyarsa Ataliya, jikanyar Omri, sarkin Isra’ila.
27 And he walked in the way of the house of Ahab, and did euill in the sight of the Lord, like the house of Ahab: for hee was the sonne in law of the house of Ahab.
Ya bi gurbin gidan Ahab, ya yi mugunta a gaban Ubangiji yadda gida Ahab ta yi, gama yana da dangantaka ta aure da gidan Ahab.
28 And he went with Ioram the sonne of Ahab to warre against Hazael King of Aram in Ramoth Gilead, and the Aramites smote Ioram.
Ahaziya ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab don su yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
29 And King Ioram returned to bee healed in Izreel of the wounds which ye Aramites had giuen him at Ramah, whe he fought against Hazael King of Aram. And Ahaziah the sonne of Iehoram King of Iudah went downe to see Ioram the sonne of Ahab in Izreel, because he was sicke.
saboda haka Sarki Yoram ya koma zuwa Yezireyel don yă yi jinyar raunin da Arameyawa suka ji masa a Rama a yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sai Ahaziya ɗan Yehoram, sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel yă dubi Yoram ɗan Ahab domin an yi masa rauni.

< 2 Kings 8 >