< 1 Samuel 12 >

1 Samuel then said vnto all Israel, Behold, I haue hearkened vnto your voyce in all that yee sayde vnto mee, and haue appoynted a King ouer you.
Sama’ila ya ce wa Isra’ilawa duka, “Na saurari abubuwan da kuka faɗa mini, na kuma naɗa muku sarki.
2 Now therefore behold, your King walketh before you, and I am old and graie headed, and beholde, my sonnes are with you: and I haue walked before you from my childehood vnto this day.
Yanzu kuna da sarki a matsayin shugaba, ni kuwa na tsufa har da furfura, yarana maza kuma suna tare da ku. Na yi shugabancinku tun ina yaro.
3 Beholde, here I am: beare recorde of me before the Lord and before his Anointed. Whose oxe haue I taken? or whose asse haue I taken? or whome haue I done wrong to? or whome haue I hurt? or of whose hande haue I receiued any bribe, to blinde mine eyes therewith, and I will restore it you?
Ga ni a gabanku. Idan na yi wani abin da ba daidai ba sai ku faɗa a gaban Ubangiji, da gaban sarkin da ya keɓe. Ko na taɓa ƙwace saniya ko jakin wani? Ko na taɓa cuce wani, ko in danne hakkinsa? Ko na taɓa cin hanci daga hannun ɗayanku? Idan na taɓa yi ɗaya daga cikin waɗannan, sai ku faɗa mini, zan kuwa mayar masa.”
4 Then they sayde, Thou hast done vs no wrong, nor hast hurt vs, neither hast thou taken ought of any mans hand.
Suka ce, “Ba ka cuci ko danne hakkin kowa ba, ba ka ƙwace kome daga hannun kowa ba.”
5 And he saide vnto them, The Lord is witnesse against you, and his Anointed is witnesse this day, that yee haue founde nought in mine handes. And they answered, He is witnesse.
Sama’ila ya ce musu, “Ubangiji yă zama shaida a kanku, shafaffensa kuma yă zama shaida a wannan rana cewa ba ku same ni da wani laifin kome ba.” Suka ce, “I, shi ne shaida.”
6 Then Samuel sayde vnto the people, It is the Lord that made Moses and Aaron, and that brought your fathers out of the land of Egypt.
Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutane, Ubangiji ne ya naɗa Musa da Haruna suka fitar da kakanninku daga Masar.
7 Nowe therefore stand still, that I may reason with you before the Lord according to all the righteousnesse of the Lord, which he shewed to you and to your fathers.
Yanzu ku tsaya nan zan yi fito-na-fito da ku da shaida a gaban Ubangiji kan dukan ayyuka masu alherin da Ubangiji ya aikata saboda ku da kakanninku.
8 After that Iaakob was come into Egypt, and your fathers cried vnto the Lord, then the Lord sent Moses and Aaron which brought your fathers out of Egypt, and made them dwell in this place.
Bayan da Yaƙub da’ya’yansa suka shiga Masar suka yi kukan neman taimako daga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya aika musu da Musa da Haruna. Su ne suka kawo kakanni-kakanninku daga Masar suka zauna a nan.
9 And when they forgate the Lord their God, he solde them into the hand of Sisera captaine of the hoste of Hazor, and into the hand of the Philistims, and into the hande of the king of Moab, and they fought against them.
Amma suka manta da Ubangiji Allahnsu, shi kuma ya bashe su a hannun Sisera shugaban rundunar Hazor da kuma hannun Filistiyawa da sarkin Mowab wanda suka yi yaƙi da su.
10 And they cried vnto the Lord, and saide, We haue sinned, because we haue forsaken the Lord, and haue serued Baalim and Ashtaroth. Nowe therefore deliuer vs out of the handes of our enemies, and we will serue thee.
Suka yi kuka a gaban Ubangiji suka ce, “Mun yi zunubi mun bar Ubangiji, muka bauta wa Ba’al da Ashtarot. Amma ka cece mu yanzu daga hannun abokan gābanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
11 Therefore the Lord sent Ierubbaal and Bedan and Iphtaph, and Samuel, and deliuered you out of the handes of your enemies on euery side, and yee dwelled safe.
Sai Ubangiji ya aiki Yerub-Ba’al da Bedan da Yefta da Sama’ila, ya cece ku daga hannun abokan gābanku a kowane gefe domin ku sami cikakken zaman lafiya.
12 Notwithstanding when you sawe, that Nahash the King of the children of Ammon came against you, ye sayde vnto me, No, but a King shall reigne ouer vs: when yet the Lord your God was your King.
Amma da kuka ga Nahash sarkin Ammonawa yana matsowa yă yaƙe, sai kuka ce mini, “Sam, muna so sarki yă shugabance mu.” Ko da yake Ubangiji Allahnku ne yake mulkinku.
13 Nowe therefore beholde the King whome yee haue chosen, and whome yee haue desired: loe therefore, the Lord hath set a King ouer you.
Yanzu ga sarkinku da kuka zaɓa wanda kuka nema, ga shi Ubangiji ya naɗa muku sarki.
14 If ye wil feare the Lord and serue him, and heare his voyce, and not disobey the worde of the Lord, both yee, and the King that reigneth ouer you, shall follow the Lord your God.
In kuka ji tsoron Ubangiji, kuka bauta masa, kuka yi masa biyayya, ba ku kuwa ƙi bin umarninsa ba, in kuma ku da sarkin da yake mulkinku kun bi Ubangiji Allahnku, to, za ku zauna lafiya.
15 But if yee will not obey the voyce of the Lord, but disobey the Lordes mouth, then shall the hand of the Lord be vpon you, and on your fathers.
Amma in ba ku yi biyayya ga Ubangiji ba, in kuma kuka ƙi bin umarnansa, fushinsa zai zauna a kanku.
16 Nowe also stande and see this great thing which the Lord will doe before your eyes.
Yanzu ku tsaya tsit ku ga abin da Ubangiji ke dab da yi a gabanku.
17 Is it not nowe wheat haruest? I wil call vnto the Lord, and he shall send thunder and raine, that yee may perceiue and see, howe that your wickednesse is great, which ye haue done in the sight of the Lord in asking you a King.
Ba lokacin yankan alkama ke nan ba? Zan roƙi Ubangiji yă aiko da tsawa da ruwan sama, za ku kuwa gane wace irin mugunta kuka yi a gaban Ubangiji sa’ad da kuka roƙa a ba ku sarki.
18 Then Samuel called vnto the Lord, and the Lord sent thunder and raine the same day: and all the people feared the Lord and Samuel exceedingly.
Sai Sama’ila ya roƙi Ubangiji, a ranar kuwa Ubangiji ya aiko da tsawa da ruwan sama. Dukan mutane suka ji tsoron Ubangiji da kuma Sama’ila.
19 And all the people said vnto Samuel, Pray for thy seruaunts vnto the Lord thy God, that we die not: for we haue sinned in asking vs a King, beside all our other sinnes.
Dukan mutane suka ce wa Sama’ila, “Ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda bayinka, domin kada mu mutu, gama mun ƙara wa kanmu zunubi da muka roƙa a yi mana sarki.”
20 And Samuel said vnto the people, Feare not. (ye haue indeede done all this wickednesse, yet depart not from following the Lord, but serue the Lord with all your heart,
Sama’ila ya ce, “Kada ku ji tsoro.” Kun yi waɗannan mugunta duk da haka kada ku bar bin Ubangiji, amma ku bauta wa Ubangiji da dukan zuciyarku.
21 Neither turne yee backe: for that shoulde be after vaine things which cannot profite you, nor deliuer you, for they are but vanitie)
Kada ku bi alloli marasa amfani. Ba za su iya yi muku kome nagari ba, ba kuwa za su iya cece ku ba, gama ba su da amfani.
22 For the Lord will not forsake his people for his great Names sake: because it hath pleased the Lord to make you his people.
Saboda suna mai girma da Ubangiji yake da shi, ba zai taɓa ƙin mutanensa ba. Gama Ubangiji ya ji daɗi da ya yi ku mutanensa.
23 Moreouer God forbid, that I should sinne against the Lord, and cease praying for you, but I will shewe you the good and right way.
Ni kam ba zai taɓa yiwu in yi wa Ubangiji zunubi ta wurin ƙin yin addu’a dominku ba. Zan koya muku hanyar da tana da kyau da ta kuma cancanta.
24 Therefore feare you the Lord, and serue him in the trueth with all your hearts, and consider howe great things he hath done for you.
Amma ku amince za ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da aniya da dukan zuciyarku, kuna da manyan abubuwan da ya yi muku.
25 But if ye doe wickedly, ye shall perish, both yee, and your King.
Amma in kuka duƙufa cikin aikin mugunta da ku da sarkinku za a hallaka ku.

< 1 Samuel 12 >